Indiya ta amsa cewa Pakistan ta kakkaɓo jiragen yaƙinta
Published: 31st, May 2025 GMT
A karon farko, rundunar tsaron Indiya ta tabbatar da cewa ta rasa wasu jiragen yaƙi a yayin arangama mai tsanani da suka fafata da Pakistan a farkon watan Mayu.
Wannan sanarwa ta fito ne daga bakin Babban Hafsan Tsaro na Indiya, Anil Chauhan, a taron Shangri-La Dialogue, babban taron tsaro na Asiya, a Singapore.
Tun da farko, jami’an Indiya sun yi ta musanta duk wata asarar jiragen sama a cikin wannan arangama, wanda aka fara ne bayan wani hari da aka kai wa masu yawon bude ido a yankin Kashmir da Indiya ke mulka a watan Afrilu, wanda Indiya ta dora alhakinsa kan Pakistan.
Ita kuwa Pakistan, ta yi ikirarin cewa ta harbo jiragen Indiya da dama, ciki har da uku kirar Rafale na Faransa.
Za a yi Huɗubar Ranar Arfa a harsunan Najeriya 3 Gwamnatin Tinubu na amfani da talauci a matsayin makami — AtikuLokacin da wani wakilin kafar yaɗa labarai ta Bloomberg ya tambaye shi kai tsaye game da iƙirarin Pakistan na harbo “jiragen Indiya shida,” Chauhan da farko ya musanta adadin a matsayin “cikakken kuskure.”
Amma daga baya ya canza zance, yana mai cewa, “abin da ke da muhimmanci shi ne dalilin da ya sa suka fadi,” yana nuni da cewa lallai an rasa wasu jiragen sama.
Bugu da ƙari, ya amince cewa sojojin Indiya sun yi “kuskuren dabara” a farkon fadan.
“Abin da ya yi kyau shi ne mun sami damar fahimtar kuskuren da muka yi, muka gyara, kuma muka sake aiwatar da shi bayan kwana biyu, muna sake kai hari daga nesa,” in ji Chauhan, yana mai nuna saurin daidaita dabarun bayan koma bayan na farko.
Faɗan na watan Mayu, wanda Indiya ta fara kai hare-hare a yankin da Pakistan ke iko da shi, ya nuna wani babban tashin hankali tsakanin kasashen biyu masu makamin nukiliya.
Daga ƙarshe an sanar da tsagaita wuta a ranar 10 ga Mayu, wanda ya kawo ƙarshen fadan na kwanaki hudu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Indiya Jiragen Yaƙi yaki
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Amurka Trump Ya Bukaci Gurfanar Da Tsohon Shugaban Amurka Barack Obama A gaban Kuliya
Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya zargi tsohon shugaban kasar Barack Obama da cin amanar kasa tare da yin kira da a yi masa shari’a
Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya zargi magabacinsa, Barack Obama da cin amanar kasa, inda ya bukaci a gurfanar da shi a gaban kuliya kan wani rahoton sirri da ya nuna cewa; Jami’an gwamnatin Obama sun murguda bayanai game da katsalandan din Rasha a zaben Amurka na shekara ta 2016.
Kalaman na Trump sun zo ne yayin wani taron manema labarai a ofishin Oval, wanda shugaban kasar Philippines Ferdinand Marcos ya halarta. Yana cewa:”Bisa ga abin da ya karanta…tsohon shugaba Obama ne ya fara wannan badakalar,” ya kara da cewa Obama shi ne “shugaba” na abin da ya bayyana a matsayin “gungun maciya amana.”
An karfafa wadannan zarge-zarge ne bayan da Daraktar hukumar leken asirin kasar Tulsi Gabbard ta aike da masu gabatar da kara ga ma’aikatar shari’a dangane da wani rahoto da aka fitar a ranar Juma’ar da ta gabata da ke tabbatar da cewa jami’an gwamnatin Obama na da hannu wajen kirkirar bayanan sirri da nufin share fagen juyin mulki na tsawon shekara daya kan shugaba Trump.