Indiya ta amsa cewa Pakistan ta kakkaɓo jiragen yaƙinta
Published: 31st, May 2025 GMT
A karon farko, rundunar tsaron Indiya ta tabbatar da cewa ta rasa wasu jiragen yaƙi a yayin arangama mai tsanani da suka fafata da Pakistan a farkon watan Mayu.
Wannan sanarwa ta fito ne daga bakin Babban Hafsan Tsaro na Indiya, Anil Chauhan, a taron Shangri-La Dialogue, babban taron tsaro na Asiya, a Singapore.
Tun da farko, jami’an Indiya sun yi ta musanta duk wata asarar jiragen sama a cikin wannan arangama, wanda aka fara ne bayan wani hari da aka kai wa masu yawon bude ido a yankin Kashmir da Indiya ke mulka a watan Afrilu, wanda Indiya ta dora alhakinsa kan Pakistan.
Ita kuwa Pakistan, ta yi ikirarin cewa ta harbo jiragen Indiya da dama, ciki har da uku kirar Rafale na Faransa.
Za a yi Huɗubar Ranar Arfa a harsunan Najeriya 3 Gwamnatin Tinubu na amfani da talauci a matsayin makami — AtikuLokacin da wani wakilin kafar yaɗa labarai ta Bloomberg ya tambaye shi kai tsaye game da iƙirarin Pakistan na harbo “jiragen Indiya shida,” Chauhan da farko ya musanta adadin a matsayin “cikakken kuskure.”
Amma daga baya ya canza zance, yana mai cewa, “abin da ke da muhimmanci shi ne dalilin da ya sa suka fadi,” yana nuni da cewa lallai an rasa wasu jiragen sama.
Bugu da ƙari, ya amince cewa sojojin Indiya sun yi “kuskuren dabara” a farkon fadan.
“Abin da ya yi kyau shi ne mun sami damar fahimtar kuskuren da muka yi, muka gyara, kuma muka sake aiwatar da shi bayan kwana biyu, muna sake kai hari daga nesa,” in ji Chauhan, yana mai nuna saurin daidaita dabarun bayan koma bayan na farko.
Faɗan na watan Mayu, wanda Indiya ta fara kai hare-hare a yankin da Pakistan ke iko da shi, ya nuna wani babban tashin hankali tsakanin kasashen biyu masu makamin nukiliya.
Daga ƙarshe an sanar da tsagaita wuta a ranar 10 ga Mayu, wanda ya kawo ƙarshen fadan na kwanaki hudu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Indiya Jiragen Yaƙi yaki
এছাড়াও পড়ুন:
An Kama Mutane 49 Da Ake Zargi Da Damfara A Jihar Kogi
PUNCH Metro ta tuna cewa a kwanakin baya jami’an hukumar EFCC shiyyar Ilorin sun kama wasu mutane 17 da ake zargi da damfarar yanar gizo a cikin hadaka a Kananan Hukumomin Ilorin da Ifelodun na jihar.
Oyewale ya ce an tare wadanda ake zargin ne a madatsar ruwa ta Asa da yankin Jami’ar Al-Hikmah da yankin Gaa-Odota da ke Ilorin da kuma yankin Ganmo da Amoyo na jihar.
“Kamen da aka yi a ranar Talata, 13 ga Mayu, 2025, ya biyo bayan bayanan sirri da aka samu wanda ya alakanta wadanda ake zargin da ayyukan damfara ta Intanet a jihar.
Sanarwar ta kara da cewa, “Kayan da aka kwato daga hannunsu da aka kama sun hada da manyan motocin alfarma guda uku, manyan wayoyin hannu da kwamfutocin tafi da gidanka”.
Kamen na baya-bayan nan ya biyo bayan wanda aka kama a makon da ya gabata wanda ya shafi mutane 47, wadanda aka kama a Ilorin da kuma Karamar Hukumar Ifelodun bisa ga bayanan sirri da suka bankado badakalar ayyukansu na intanet.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp