Aminiya:
2025-09-17@23:10:37 GMT

Indiya ta amsa cewa Pakistan ta kakkaɓo jiragen yaƙinta

Published: 31st, May 2025 GMT

A karon farko, rundunar tsaron Indiya ta tabbatar da cewa ta rasa wasu jiragen yaƙi a yayin arangama mai tsanani da suka fafata da Pakistan a farkon watan Mayu.

Wannan sanarwa ta fito ne daga bakin Babban Hafsan Tsaro na Indiya, Anil Chauhan, a taron Shangri-La Dialogue, babban taron tsaro na Asiya, a Singapore.

Tun da farko, jami’an Indiya sun yi ta musanta duk wata asarar jiragen sama a cikin wannan arangama, wanda aka fara ne bayan wani hari da aka kai wa masu yawon bude ido a yankin Kashmir da Indiya ke mulka a watan Afrilu, wanda Indiya ta dora alhakinsa kan Pakistan.

Ita kuwa Pakistan, ta yi ikirarin cewa ta harbo jiragen Indiya da dama, ciki har da uku kirar Rafale na Faransa.

Za a yi Huɗubar Ranar Arfa a harsunan Najeriya 3 Gwamnatin Tinubu na amfani da talauci a matsayin makami — Atiku

Lokacin da wani wakilin kafar yaɗa labarai ta Bloomberg ya tambaye shi kai tsaye game da iƙirarin Pakistan na harbo “jiragen Indiya shida,” Chauhan da farko ya musanta adadin a matsayin “cikakken kuskure.”

Amma daga baya ya canza zance, yana mai cewa, “abin da ke da muhimmanci shi ne dalilin da ya sa suka fadi,” yana nuni da cewa lallai an rasa wasu jiragen sama.

Bugu da ƙari, ya amince cewa sojojin Indiya sun yi “kuskuren dabara” a farkon fadan.

“Abin da ya yi kyau shi ne mun sami damar fahimtar kuskuren da muka yi, muka gyara, kuma muka sake aiwatar da shi bayan kwana biyu, muna sake kai hari daga nesa,” in ji Chauhan, yana mai nuna saurin daidaita dabarun bayan koma bayan na farko.

Faɗan na watan Mayu, wanda Indiya ta fara kai hare-hare a yankin da Pakistan ke iko da shi, ya nuna wani babban tashin hankali tsakanin kasashen biyu masu makamin nukiliya.

Daga ƙarshe an sanar da tsagaita wuta a ranar 10 ga Mayu, wanda ya kawo ƙarshen fadan na kwanaki hudu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Indiya Jiragen Yaƙi yaki

এছাড়াও পড়ুন:

DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu

Hukumar Tsaron Farin Kaya a Nijeriya DSS, ta gurfanar da fitaccen ɗan gwagwarmayar nan, Omoyele Sowore a kotu.

A ƙunshin ƙarar da DSS ta gabatar a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta haɗa da shafukan sada zumunta na X da kuma Facebook, inda take zarginsu da ba da ƙofar aibata Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Bida Poly ta sa sojoji kula da jarrabawar ɗalibai Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku

Darekan shigar da ƙara na Ma’aikatar Shari’a ta Tarayya, M.B Abubakar da wasu lauyoyi huɗu —M.E. Ernest da U.B. Bulla da C.S. Eze da kuma E.G. Orubor, ne suka shigar da ƙarar a madadin Gwamnatin Tarayya da kuma hukumar ta DSS.

DSS wadda ta kafa hujja da sashe na 24 da ke cikin kundin dokokin yanar gizo, ta ce Sowore ya yi amfani da shafukansa na dandalan sada zumunta na X da Facebook wajen wallafa wani saƙo da ke cin mutuncin Shugaba Tinubu.

Tun dai a farkon watan nan ne DSS ta buƙaci goge wani saƙo da ɗan gwagwarmayar ya wallafa wanda ta riƙa a matsayin bayanan ƙarya, cin zarafi ta yanar gizo da kalaman haddasa ƙiyayya, waɗanda kuma ta ce na iya haddasa rikici su kuma ɓata sunan Najeriya a ƙasashen waje.

Sai dai har zuwa ranar Litinin, 15 ga watan Satumba, babu wani mataki da aka ɗauka na goge saƙon da DSS ɗin ta buƙata.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
  • An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha