HausaTv:
2025-05-21@12:22:51 GMT

UNRWA : ba wani abu dake shiga Gaza in banda bama-bamai

Published: 21st, May 2025 GMT

Hukumar Ba da Agaji ta Majalisar Dinkin Duniya mai kula da ‘yan gudun hijirar Falasdinu a Gabas ta Tsakiya (UNRWA) ta yi gargadin cewa akwai yiyuwar Gaza ta fuskanci matsalar jin kai mafi muni tun watan Oktoban 2023.

A cikin wani sako da ta wallafa a shafin X, UNRWA ta ce yanzu haka makonni 11 kenan da gwamnatin Isra’ila ta hana shigar da abinci, man fetur da magunguna zuwa Gaza.

“Makonni 11, jami’an Isra’ila da gangan sun hana duk wani kayan agaji zuwa Gaza, abin da kawai ke shiga Gaza a yanzu shi ne bama-bamai.

Daruruwan Falasdinawa ne aka kashe a wannan makon yayin da gwamnatin Isra’ila ke kara kai hare-hare ta sama, in ji UNRWA.

“Zafafa hare-haren bama-bamai ta sama da kasa da na ruwa na Isra’ila ya haifar da asarar daruruwan rayuka da kuma gudun hijirar jama’a.”inji hukumar

Mataimakin sakatare mai kula da harkokin jin kai na Majalisar Dinkin Duniya Tom Fletcher ya fada jiya talata cewa jarirai 14,000 a Gaza za su iya mutuwa cikin sa’o’i 48 masu zuwa idan ba a kai musu dauki ba.

Tom Fletcher ya yi Allah-wadai da dokar hana kai kayan agaji zuwa zirin Gaza, yana mai cewa tireloli biyar ne kawai aka ba da izinin shiga a ranar Litinin, wanda ya bayyana a matsayin “digo a cikin teku.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sarkin Saudiyya Ya Ɗauki Nauyin Falasɗinawa 1,000 Su Sauke Farali

Sarkin Saudiyya, Salman Bin Abdulaziz, ya bayar da umarnin ɗaukar nauyin Hajjin iyalan Falasɗinawa 1,000 da suka rasa ‘yan uwansu sakamakon yaƙin da ke ci gaba da gudana a Zirin Gaza da Isra’ila.

Wannan taimako na cikin littafin kujerun Hajji da masarautar ke rabawa a kowace shekara ga al’umma ko kuma ɗaukar nauyin waɗanda suka cancanta, ciki har da waɗanda suka riga suka biya kuɗin Hajjin.

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah

Sarkin ya bayyana wannan mataki ne a matsayin ɗaya daga cikin hanyoyin nuna goyon baya da jin ƙai ga al’ummar Falsɗinawa a wannan lokaci mai wahala da suke ciki sakamakon yaƙi da ƙasar Yahudawa ta Isra’ila ta ƙaddamar a Gaza.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Falasdinawa 94 sun yi shahada a Hare-haren Isra’ila a rana guda
  • Hare-Haren Wuce Gona Da Irin Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Janyo Shahadan Falasdinawa Masu Yawa
  • Hare-Haren Isra’ila Ya Hallaka Aƙalla Mutum 38 A Gaza Cikin Rabin Sa’a
  • HKI Ta Bude Kofofin Shigar Kayakin Agaji Zuwa Cikin Gaza A Karon Farko Bayan Kimani Watanni 2.5
  • Yadda jami’an tsaron Vatican suka hana Seyi zuwa wajen Tinubu da Fafaroma
  • Isra’ila Ta Kai Hari Ga Rumbun Magungunna A Kudancin Gaza
  • Sarkin Saudiyya Ya Ɗauki Nauyin Falasɗinawa 1,000 Su Sauke Farali
  • An kashe ’yan kasuwa 15 a wani sabon hari a Binuwai
  •  Gaza: Falasdinawa 150 Ne Su Ka Yi Shahada A Yau Lahadi