Da safiyar yau Talata mazauna yankin “al-Daraj’dake Gaza su ka  farka daga cikin sanadiyyar  harin da jiragen yakin HKI su ka kai wa makarantar ” Musa Bin Nusair” dake karkashin hukumar agaji ta UNRWA” wacce take kunshe da daruruwan ‘yan hijira.

Dama dai wannan ba shi ne karon farko da wannan yankin yake fuskantar hare-hare daga HKI ba.

Ma’aikatar kiwon lafiya ta Gaza ta sanar da cewa; Harin na yau ya yi sanadiyyar shahadar Falasdinawa 44,mafi yawancinsu mata ne da kananan yara, baya ga wani adadi mai yawa na Falasdinawan da su ka jikkata.

Kananan yara da suke rayuwa a cikin wannan sansanin ‘yan hijira sun rika kai da komowa suna neman kayan wasanninsu daga karkashin baraguzai.

A kusa da asibitin “Ma’amadani” wanda sojojin sahayoniyar su ka kashe mutane 500 a cikinsa, tun farko-farkon yaki, an ga wasu mata suna bak kwana da dangi da ‘yan’uwansu da su ka yi shahada cikin kuka mai kuna.

Tuni dai aka yi jana’izar jam’i ta shahidan su 44.

Yakin Gaza dai ya shiga watanni na 18, ta yadda a halin yanzu babu wani wuri mai rufi idan ba hemomin da ‘yan hijira suke ciki ba. Bugu da kari sojojin na HKI sun lalata dukkanin muhimman cibiyoyin yankin na Gaza, da su ka hada  na samar da ruwa, wutar lantarki, da kuma hana shigar da kayan abinci da magani cikin yankin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dinkin Duniya Ta Fitar Da Rahoton Wadanda Suke Taimakawa Yahudawan Sahayoniyya Wajen Murkushe Falasdinawa

Rahoton Majalisar Dinkin Duniya mai ban tsoro ya bayyana cewa: Manyan kamfanoni suna da hannu wajen aiwatar da kisan kare dangi a Gaza

Wani rahoto da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar ya bayyana sunayen wasu manyan kamfanoni na duniya sama da 60 da ke da hannu a tallafawa wajen gine-ginen matsugunan yahudawa ‘yan kaka gida a yankunan gabar yammacin kogin Jordan da kuma hare-haren wuce gona da iri kan Zirin Gaza.

Rahoton wanda wakiliyar Majalisar Dinkin Duniya na musamman kan halin da ake ciki na kare hakkin bil adama a yankunan Falasdinawa da aka mamaye, Francesca Albanese, ta wallafa ya samo asali ne daga bayanai sama da 200 daga kasashe, kungiyoyin kare hakkin bil adama, masana ilimi da kamfanoni. Ta yi kira ga kamfanonin da su daina kasuwanci da haramtacciyar kasar Isra’ila, ta kuma yi tambayar cewa saboda rike harkokin gudanarwar kudade da kuma doka da oda don fa’idarsu da suke samu daga hare-haren da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke kai wa yankunan Falasdinawa.

Daga cikin kamfanonin da aka ambata a cikin rahoton, mafiya shahararsu akwai kamfanonin Amurka: Google, Microsoft, IBM, Caterpillar, a heavy equipment manufacturer, Lockheed Martin, a military manufacturer, da Hyundai na kasar Koriya ta Kudu. Rahoton ya zarge su da hannu a ayyukan danniya, kera makamai, da lalata dukiyoyi a yankunan Falasdinu.

Rahoton yana wakiltar fadada jerin sunayen da aka baiwa  Majalisar Dinkin Duniya a shekara ta 2023 wanda ya mayar da hankali kawai kan kamfanonin da ke da alaka gwamnatin mamaya, yayin da sabon rahoton ya kunshi bangarori masu fadi da ke da alaka da cin zarafi a Gaza. Albanese ta gabatar da wannan zargi a cikin wani cikakken bayani game da rikicin Falasdinu: “Yayin da ake kashe rayuka a Gaza kuma ake ci gaba da kara kashe-kashen a gabar yammacin kogin Jordan, wannan rahoto ya nuna cewa kisan kiyashin da ake kira ya ci gaba ne kawai saboda yana da riba ga bangarori da yawa.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Masu Neman Karbar Kayan Agaji A Gaza
  • Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace
  •   Gaza: Fiye Da Falasdinawa 17 Ne Su Ka Yi Shahada Ayau Juma’a
  •  Antonio Guterres Ya Kadu Saboda Mummunan Halin Da Falasdinawan Gaza Suke Ciki
  • Kwamandan Sojojin Iran Ya Ziyarci Gidan Babban Jami’in Sojin Kasar Da Ya Yii Shahada Lokacin Yakin Baya-Bayan Nan
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Fitar Da Rahoton Wadanda Suke Taimakawa ‘Yan Sahayoniyya Wajen Murkushe Falasdinawa
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Fitar Da Rahoton Wadanda Suke Taimakawa Yahudawan Sahayoniyya Wajen Murkushe Falasdinawa
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Sake Aiwatar Da Kisan Kare Dangi Kan ‘Yan Gudun Hijiran Falasdinawa
  • Falasdinawa Kimani 40,000 HKI Ta Kora Daga Yankin Yamma Da Kogin Jordan
  • Ben Gafir Ya Bukaci Gwamnatin HKI Ta Mamaye Yankin Gaza Gaba daya