Iran Ta Kira Jakadan Burtaniya A Tehran Saboda Tuhumar Da Akewa Iran Da Leken Asiri A London
Published: 19th, May 2025 GMT
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta kira mataimakin jakadan kasar Burtania a Tehran zuwa ma’aikatar don gabatar mata da korafi kan yadda jami’an tsaron kasar Burtaniya suke kama yan kasar Iran ma zauna birnin London tare da tuhumarsu da ayyukan Leken asiri wa JMI.
Tashar talabjin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa a cikin wannan watan Mayu da muke ciki Jami’an yansanda a kasar Burtaniya sun kama Iraniyawa mazauna birnin London har guda 7 a sumamen guda biyu da suka kaimasu a gidajensu.
Labarin ya kara da cewa an gabatar da mutane uku a gaban kotu a birnin London tare da tuhumar su da aikin leken asiri ga JMI.
Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya kara da cewa, kame kamen da gwamnatin kasar Burtaniya takewa Iraniyawa a London na siyasa ne.
Labarin ya kara da cewa saboda yawan kame-kamen ne ya sa ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta kira mataimakon jakadan kasar Burtaniya a nan Birnin Tehran zuwa ma’aikatar don gabatar mata da wannan korafin.
Masana suna ganin gwamnatin Burtaniya tana yin haka ne don takurawa JMI inji ma’aikatar.
Labarin ya kara da cewa sakataren harkokin wajen kasar Burtaniya ya kira jakadan Iran a Lodon Sayyed Ali Musawi inda suka fada masa cewa gwamnatin Iran ce da alhakin wasu matsalolin tsaro a kasar Burtaniya.
Ya zuwa yanzu da an gurfanar da Iraniyawa uku a gaban kutu a binin Landa, kuma sun hada da Mostafa Sepahvand, dan shekara 39 a duniya, sai Farhad Javadi Manesh, dan shekara 44 a duniya da kuma Shapoor Qalehali Khani Noori dan shekara 55 a duniya dukkaninsu mazauna birnin Landon.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Burtaniya ya kara da cewa
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Irin Aniyar Da Gwamantinsa Ta Kudurta Wajen Kare Tsaron Kasa Da Al’ummarta
Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Sun kuduri aniyar kare kan iyakokin Iran da tsaron kasar da kuma al’ummarta
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya ce: “Suna goyon bayan zaman lafiya, kuma ba su amince da yaki ba, amma a lokaci guda kuma, suna tabbatar da aniyarsu ta kare kan iyakokin Iran da tsaron kasarta da kuma al’ummarta.”
A yau, Laraba ne, Shugaban kasar Iran Pezeshkian ya wallafa wani rubutu a shafinsa na sadarwa, inda ya jaddada babban kudirin gwamnatin Jamhuriyar Musulunci ta Iran na kare kan iyakokin kasar da tsaro da al’ummar kasar. Yana mai jaddada cewa: “A tushen al’adu da wayewar Iran, suna da gogewa da yawa wajen rage wahalhalun da mutane ke fuskanta.”
Shugaban ya kara da cewa: Iran na cike da kayan ado da kyau kuma gaskiya tana bayyana a kowane lungu da sako, a ko da yaushe suna neman gina gadoji ne tare da wasu, ba katanga ba.
A gefen taron Majalisar ministocin kasar, shugaba Pezeshkian ya ce: “A kwanakin nan tunaninsu ya fi karkata ne wajen magance matsalolin al’ummar kasa da kuma rage damuwarsu tare da jaddada wajibcin yin aiki tare a tsakanin al’ummar Iran don kaucewa jefa su cikin matsaloli; Ya kara da cewa: Al’ummar Iran sun nuna jajircewa da hadin kai wajen samar da alfahari da daukaka ga kansu, kuma sun yi nasarar dakile makircin makiya, kuma hakan ya cancanci a yaba musu.