Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta kira mataimakin jakadan kasar Burtania a Tehran zuwa ma’aikatar don gabatar mata da korafi kan yadda jami’an tsaron kasar Burtaniya suke kama yan kasar Iran ma zauna birnin London tare da tuhumarsu da ayyukan Leken asiri wa JMI.

Tashar talabjin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa a cikin wannan watan Mayu da muke ciki Jami’an yansanda a kasar Burtaniya sun kama Iraniyawa mazauna birnin London har guda 7 a sumamen guda biyu da suka kaimasu a gidajensu.

Labarin ya kara da cewa an gabatar da mutane uku a gaban kotu a birnin London tare da tuhumar su da aikin leken asiri ga JMI.

Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya kara da cewa, kame kamen da gwamnatin kasar Burtaniya takewa Iraniyawa a London na siyasa ne.

Labarin ya kara da cewa saboda yawan kame-kamen ne ya sa ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta kira mataimakon jakadan kasar Burtaniya a nan Birnin Tehran zuwa ma’aikatar don gabatar mata da wannan korafin.

Masana suna ganin gwamnatin Burtaniya tana yin haka ne don takurawa JMI inji ma’aikatar.

Labarin ya kara da cewa sakataren harkokin wajen kasar Burtaniya ya kira jakadan Iran a Lodon Sayyed Ali Musawi inda suka fada masa cewa gwamnatin Iran ce da alhakin wasu matsalolin tsaro a kasar Burtaniya.

Ya zuwa yanzu da an gurfanar da Iraniyawa uku a gaban kutu a binin Landa, kuma sun hada da Mostafa Sepahvand, dan shekara 39 a duniya, sai Farhad Javadi Manesh, dan shekara 44 a duniya da kuma Shapoor Qalehali Khani Noori dan shekara 55 a duniya dukkaninsu mazauna birnin Landon.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Burtaniya ya kara da cewa

এছাড়াও পড়ুন:

DSS ta gurfanar da matashin da ya yi kira a yi juyin mulki a Najeriya a gaban kotu

Hukumar tsaro ta DSS ta gurfanar wani matashi mai suna Innocent Chukwuemeka Onukwume, mai shekaru 27, bisa zargin kiran sojoji da su yi juyin mulki a Najeriya.

Hukumar dai ta shigar da ƙarar matashin ne cikin tuhuma shida a gaban Kotun Tarayya da ke Abuja.

Ɗan Majalisar Wakilai daga Kano Sagir Ƙoƙi ya fice daga NNPP PDP ta sha alwashin gudanar da babban taronta duk da umarnin kotu

An shigar da ƙarar ne mai lamba FHC/ABJ/CR/610/2025, dangane da wasu rubuce-rubuce da matashin ya wallafa a shafinsa na X a watan Oktoban 2025.

A cewar DSS, waɗannan rubuce-rubuce sun nemi a kifar da gwamnatin jam’iyyar APC mai mulki tare da nuna goyon baya ga sojoji su karɓi mulki a ƙasar.

Lauyan DSS, A.M. Danalami, ya shigar da ƙarar a ranar Talata, inda aka bayyana cewa ayyukan wanda ake zargin sun saɓa da sashe na 46A(1) da 59(1) na Dokar Manyan Laifuka ta Ƙasa, da kuma Sashe na 24(1)(b) na Dokar Laifukan Intanet ta 2024 (wacce aka yi wa gyara).

Daga cikin kalaman da ake zargin ya wallafa akwai: “Ana buƙatar juyin mulki a Najeriya. A kawar da APC, a dakatar da gwamnatin Najeriya, a shiga kungiyar AES. Wannan ne kawai muke buƙata yanzu.”

Haka kuma, ana zargin ya rubuta cewa: “A karshe zai faru,  yak u ’yan Najeriya. Sojoji na buƙatar goyon bayanku yanzu! Su kaɗai ne za su iya ceton ƙasar nan. Wanda ke Aso Rock ya sayar da ƙasar nan ga Turawa, su ke sarrafa sirrikanmu. Sojoji kaɗai za su iya sake daidaita ƙasar nan.”

A wani rubutu daban kuma ya ce: “Dole ne Tinubu ya tafi, kuma dole APC ta mutu kafin Najeriya ta samu daidaito.”

Ana sa ran za a gurfanar da Onukwume, wanda mazaunin Umusayo Layout ne a Karamar Hukumar Oyigbo ta Jihar Ribas a kotu cikin makon nan.

A watan Oktoba, an samu rahotanni da ke nuna cewa wasu jami’an sojoji sun yi yunkurin kifar da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya
  • An kama mutum 3 kan zargin safarar yara 17 a Zariya
  • Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa
  • Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing
  • Iran Da Pakistan Sun yi Kira Da Yin Aiki Tare Don Tunkarar  Makiyansu
  • Sin Ta Yi Kira Da A Inganta Mika Mulki Cikin Kwanciyar Hankali A Sudan Ta Kudu
  • DSS ta gurfanar da matashin da ya yi kira a yi juyin mulki a Najeriya a gaban kotu
  • Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam
  • Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa
  • Mai cutar HIV ya yi wa ’yar shekara 4 fyaɗe a Yobe