Iran Ta Kira Jakadan Burtaniya A Tehran Saboda Tuhumar Da Akewa Iran Da Leken Asiri A London
Published: 19th, May 2025 GMT
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta kira mataimakin jakadan kasar Burtania a Tehran zuwa ma’aikatar don gabatar mata da korafi kan yadda jami’an tsaron kasar Burtaniya suke kama yan kasar Iran ma zauna birnin London tare da tuhumarsu da ayyukan Leken asiri wa JMI.
Tashar talabjin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa a cikin wannan watan Mayu da muke ciki Jami’an yansanda a kasar Burtaniya sun kama Iraniyawa mazauna birnin London har guda 7 a sumamen guda biyu da suka kaimasu a gidajensu.
Labarin ya kara da cewa an gabatar da mutane uku a gaban kotu a birnin London tare da tuhumar su da aikin leken asiri ga JMI.
Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya kara da cewa, kame kamen da gwamnatin kasar Burtaniya takewa Iraniyawa a London na siyasa ne.
Labarin ya kara da cewa saboda yawan kame-kamen ne ya sa ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta kira mataimakon jakadan kasar Burtaniya a nan Birnin Tehran zuwa ma’aikatar don gabatar mata da wannan korafin.
Masana suna ganin gwamnatin Burtaniya tana yin haka ne don takurawa JMI inji ma’aikatar.
Labarin ya kara da cewa sakataren harkokin wajen kasar Burtaniya ya kira jakadan Iran a Lodon Sayyed Ali Musawi inda suka fada masa cewa gwamnatin Iran ce da alhakin wasu matsalolin tsaro a kasar Burtaniya.
Ya zuwa yanzu da an gurfanar da Iraniyawa uku a gaban kutu a binin Landa, kuma sun hada da Mostafa Sepahvand, dan shekara 39 a duniya, sai Farhad Javadi Manesh, dan shekara 44 a duniya da kuma Shapoor Qalehali Khani Noori dan shekara 55 a duniya dukkaninsu mazauna birnin Landon.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Burtaniya ya kara da cewa
এছাড়াও পড়ুন:
Kotu Ta Daure Wasu Mutane 3 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Mutum A Gidan Yarin Adamawa
Wadanda ake tuhumar dai, a cewar rahoton farko, sun yi wa mamacin dukan tsiya har sai da ya suma, inda aka garzaya da shi Cibiyar Kiwon Lafiya ta Tarayya ta Hong inda wani likita ya tabbatar da mutuwarsa.
Dukkan wadanda ake tuhumar dai sun ki amsa laifin da ake zarginsu da aikatawa lokacin da aka karanta musu tuhume-tuhumen.
Kotun da ke karkashin Alkali Uwani Danladi, ta bayar da umarnin a garkame wadanda ake kara a gidan gyaran hali don bai wa ‘yansanda damar kammala bincike tun da har yanzu akwai sauran mutum daya da ake tuhuma.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp