Aminiya:
2025-08-04@11:10:31 GMT

’Yan bindiga sun kashe matar aure bayan karɓar N10m kuɗin fansa

Published: 5th, May 2025 GMT

’Yan bindiga sun kashe wata mata da suka sace tare da mijinta Yakubu Dada watanni bakwai da suka gabata a yankin Kontagora da ke Jihar Neja.

Aminiya ta ruwaito cewa ’yan ta’addan sun halaka matar mai suna Lami bayan karɓar Naira miliyan 10 kuɗin fansa.

’Yan fashi sun kashe matashi a Kano Kwankwaso: Abba ya mayar wa Baffa Bichi martani

Kazalika, ’yan bindigar sun kuma nemi ƙarin Naira miliyan 20 da baburan Bajaj huɗu, tare da yin barazanar kashe mijinta muddin aka gaza kai musu abubuwan da suka buƙata.

Aminiya ta ruwaito cewa, tun a ranar 31 ga watan Oktoba na 2024 ne Yakubu Dada da mai ɗakinsa suka faɗa tarkon masu garkuwa yayin da suke kan hanyar zuwa Kontagora.

Da take zantawa da wakilinmu, uwargidan magidancin mai suna Maimuna, ta ce sun cefanar da kusan duk abin da suka mallaka ciki har da gidaje, motoci, gadaje, akwatin talabijin domin tara kuɗin fansar naira miliyan 10 da suka biya a watan Nuwamban bara.

Ta ce wani ƙanin mijinsu ne ya kai wa masu garkuwar kuɗin fansar a wani daji a Jihar Kebbi, amma daga bisani suka nemi ƙarin naira miliyan 60 sannan suka sassauta zuwa naira miliyan 20 da har kawo yanzu sun gaza biya.

Maimuna wadda ta ce masu garkuwa sun kashe abokiyar zamanta a ranar Lahadin da ta gabata, ta buƙaci gwamnatin jihar Neja da hukumomin tsaro da su shiga lamarin domin ceto mijin nasu.

Wani makwabci, Idris Mohammed, ya ce an yi kiran neman tallafa wa waɗanda lamarin ya shafa a yayin sallar Juma’ar da ta gabata tun kafin labarin mutuwar Lami.

Aminiya ta tuntuɓi mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Neja, SP Wasiu Abiodun, sai dai ya yi alƙawarin zai bibiyi lamarin gabanin cewa komai a kai.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga garkuwa da mutane Jihar Neja matar aure

এছাড়াও পড়ুন:

MDD: HKI Ta Kashe Falasdinawa 1 Fiye Da 100 A Cikin Kwanaki 2 A Lokacinda Suka Karban Abinci

Hukumar kula da samar da agaji ta MDD OCHA ta bada sanarwan kissan Falasdinawa fiye da 100 a lokacinda suke kokarin neman abincin da zasu ci.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto mataimakin shugaban kungiyar ta OCHA Farhan Haq yana fadar haka. Ya kuma kara da cewa bai kamata mutane sum utu a wajen neman abinci ba. Dokokin kasa da kasa sun tabbatar da cewa, mutum ko menene laifinsa bai kamata a hana shi abinci ba, kuma bai kamata yam utu  saboda neman abinci ba.

Farhan Haq ya yi gargadin cewa idan wannan halin ya ci gaba, to dukkan duniya sun ji kunya, idan suna da shi, suna ganin Falasdinawa suna mutuwa a lokacinda kowa a duniya yana kallo, amma ba wanda ya isa ya hana hakan faruwa.

Yace kofar ragon da HKI ta yiwa Gaza, ya kai ga a halin nyanzu yunwa ta yi tsanani a gaza ta yadda yuwan tana kashesu a mazauninsu a cikin gaza. Kuma maganin shi ne dole ne a cika gaza da kayakin abinci.


Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Mutanen Kasar Siriya Sun Fito Zanga-Zanga Yin Allawadai Da Kissan Alawiyya A Kasar August 2, 2025 Shugaban Ansarullah: Amurka Tana Da Hannu A Ta’asar Da HKI Take Aikatawa A Gaza August 2, 2025 Kungiyar Wasan Taekwondo Ta Guragu Ta Iran Ta Zama Zakara A Asiya Karo Na 10 A Jere August 2, 2025 Iran ta yi gargadi game da makircin Isra’ila na kawo cikas ga tsaron yankin August 2, 2025 Firayim Ministan Senegal Ya Bayyana Sabon Shirin Farfado Da Tattalin Arzikin Kasar August 2, 2025 Gaza: Witfkoff ya yi rangadi a wuraren da Amurka ta kafa domin tallafi August 2, 2025 ‘Yan Sudan dama na komawa gida bayan gudun hijira na tsawon shekaru a Masar August 2, 2025 Iran Ta Ce Batun Neman Dakatar Da Tace Uranium Zai Rusa Duk Wata Jarjejeniya Da Ake Son Cimmawa August 1, 2025 Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Yi Watsi Da Duk Wani Zarge-Zargen Neman Bata Mata Suna August 1, 2025 Limamin Sallar Juma’a Ya Ce; Iran Zata Mayar Da Isra’ila Kufai Idan Ta Sake Kai Hari Kan Kasarta August 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara
  • Gwamnatin Sakkwato Za Ta Kashe fiye da Naira Miliyan 200 Wajen Gyara Tashar Talabijin Ta Kasa NTA
  • Shirin kashe N712bn kan gyaran filin jirgin Legas ya tayar da ƙura
  • Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 
  • Najeriya na hasashen samun N300bn a shekara daga noman dabino
  • Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50
  • An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo
  • MDD: HKI Ta Kashe Falasdinawa 1 Fiye Da 100 A Cikin Kwanaki 2 A Lokacinda Suka Karban Abinci
  • Martani: Har yanzu muna ci gaba da yajin aiki — Ma’aikatan jinya  
  • Nijeriya Na Asarar Kusan Naira Tiriliyan 17.9 Duk Shekara Sakamakon Cutar Hanta — Gwamnati