’Yan bindiga sun kashe matar aure bayan karɓar N10m kuɗin fansa
Published: 5th, May 2025 GMT
’Yan bindiga sun kashe wata mata da suka sace tare da mijinta Yakubu Dada watanni bakwai da suka gabata a yankin Kontagora da ke Jihar Neja.
Aminiya ta ruwaito cewa ’yan ta’addan sun halaka matar mai suna Lami bayan karɓar Naira miliyan 10 kuɗin fansa.
’Yan fashi sun kashe matashi a Kano Kwankwaso: Abba ya mayar wa Baffa Bichi martaniKazalika, ’yan bindigar sun kuma nemi ƙarin Naira miliyan 20 da baburan Bajaj huɗu, tare da yin barazanar kashe mijinta muddin aka gaza kai musu abubuwan da suka buƙata.
Aminiya ta ruwaito cewa, tun a ranar 31 ga watan Oktoba na 2024 ne Yakubu Dada da mai ɗakinsa suka faɗa tarkon masu garkuwa yayin da suke kan hanyar zuwa Kontagora.
Da take zantawa da wakilinmu, uwargidan magidancin mai suna Maimuna, ta ce sun cefanar da kusan duk abin da suka mallaka ciki har da gidaje, motoci, gadaje, akwatin talabijin domin tara kuɗin fansar naira miliyan 10 da suka biya a watan Nuwamban bara.
Ta ce wani ƙanin mijinsu ne ya kai wa masu garkuwar kuɗin fansar a wani daji a Jihar Kebbi, amma daga bisani suka nemi ƙarin naira miliyan 60 sannan suka sassauta zuwa naira miliyan 20 da har kawo yanzu sun gaza biya.
Maimuna wadda ta ce masu garkuwa sun kashe abokiyar zamanta a ranar Lahadin da ta gabata, ta buƙaci gwamnatin jihar Neja da hukumomin tsaro da su shiga lamarin domin ceto mijin nasu.
Wani makwabci, Idris Mohammed, ya ce an yi kiran neman tallafa wa waɗanda lamarin ya shafa a yayin sallar Juma’ar da ta gabata tun kafin labarin mutuwar Lami.
Aminiya ta tuntuɓi mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Neja, SP Wasiu Abiodun, sai dai ya yi alƙawarin zai bibiyi lamarin gabanin cewa komai a kai.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga garkuwa da mutane Jihar Neja matar aure
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Fadada Matakin Rage Haraji Ga Kasashe Masu Raunin Tattalin Arziki
Tawagar kasar Sin a taron birnin Geneva, ta shaidawa kungiyar cinikayya ta duniya WTO, cewa kasar ta fadada matakinta na rage harajin fito da take karba daga kasashe masu karancin karfin tattalin arziki, daga kaso 98 bisa dari zuwa kaso 100 bisa dari.
A jiya Laraba ne tawagar ta Sin ta bayyana wannan albishir, inda ta ce baya ga janye dukkanin harajin fito baki daya, Sin ta sha alwashin kara aiwatar da matakai na ingiza cinikayyar hajoji, da karfafa kwarewar aiki, da aiwatar da kwasa-kwasai na horar da sana’o’in fasaha a kasashen Afirka masu raunin tattalin arziki.
Kazalika, tawagar ta Sin ta ce wadannan matakai na da nufin samar da sabbin damammakin habaka ci gaban wannan rukuni na kasashen Afirka, tare da bayar da gudummawar daidaitawa, da ingiza ci gaban cinikayya tsakanin sassan kasa da kasa.
Membobin kungiyar WTO sun jinjinawa wannan albishir na tawagar Sin, yayin da wakilai daga kasashen Afirka masu raunin tattalin arziki, da sauran sassan kasa da kasa suka bayyana godiya game da hakan, suna masu nuni da tarin kalubale, da yanayin rashin tabbas da kasashe masu tasowa ke fuskanta a duniya. Har ila yau, membobin WTOn sun yi kira ga karin kasashen duniya da su yi koyi da kasar Sin, wajen samar da manufofi masu dacewa, da tallafin horar da kwararru, da tallafawa rukunin kasashe masu karancin karfin tattalin arziki, ta yadda za a iya bunkasa cinikayya mai dorewa, da game dukkanin sassan kasa da kasa. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp