A cikin wata daya kadai sojojin HKI sun rushe gidajen Falasdinawa 152 a yammacin Kogin Jordan.

Majiyar Falasdinawa ta ambaci cewa a kudancin garin Khalil ‘yan mamayar sun rushe gidaje 25 da kuma wasu cibiyoyi, da hakan ya sa adadin gidajen da su ka rushe zuwa 152 kamar yadda hukumar Falasdinu ta ambata.

Bugu da kari, majiyar Falasdinawan ta ce, ‘yan mamayar sun kuma aike wa da wasu cibiyoyin da gidaje 46 gargadin cewa za su rushe su, da yin kira da  su fice daga cikinsu.

Wata cibiyar ta Falasdinawa ta ce fada wa kamfanin dillancin labarun “Anatoli’ cewa; ;yan mamayar sun rushe gidaje 96 da mutane suke rayuwa a cikinsu, sai kuma wasu gidaje 10 da babu mutane a ciki.Haka nan kuma rusau din ya shafi wasu cibiyoyin noma 34.

Mafi yawancin gidajen da aka rushe dai suna a yankin Tubas ne, Khalil sannan kuma da birnin Kudus.

Wani rahoto ya ambaci cewa; A cikin watan da ya gabata,’yan mamaya suna nazarin gina matsugunan ‘ya share wuri zauna 27 a cikin birnin Kudus.

A gefe daya, ‘yan share wuri zauna din sun kai hare-hare akan Falasdinawa har sau 1693 wanda ya fara a cikin watan Afrilu. Hare-haren kuwa sun hada lalata hanyoyi da tunbuke bishiyoyi, a kwace filayen Falasdinawa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu na ƙaddamar da wasu ayyuka a Jihar Kaduna

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu na ziyarar aiki a cikin Jihar Kaduna.

Shugaba Tinubu na ziyarar ne domin ƙaddamar da wasu ayyuka da gwamnan jihar, Uba Sani ya aiwatar a tsawon shekara biyu da ya yi yana mulkin jihar.

Za a dawo da dukkan Alhazai gida ranar 28 ga Yuni – NAHCON Kotu ta ba da belin Natasha kan N50m kan zargin bata sunan Akpabio

Wasu daga cikin ayyukan da shugaban ya ƙaddamar sun haɗa da: asibitin ƙwararru mai gadaje 300 da gwamnatin jihar ta gina don bunƙasa harkokin lafiya.

Daga nan kuma shugaban ya ƙaddamar da cibiyar koyar da sana’o’i, da kuma motocin sufuri masu amfani da iskar gas ta CNG guda 100.

A cikin waɗanda suka yi wa Shugaba Tinubu rakiya sun haɗa da: Mataikamin Shugaban ƙasa na musamman kan harkokin siyasa, Sanata Ibrahim Masara, da mai taimaka wa shugaban kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu da Shugaban Majalisar Wakilai,  Tajudeen Abbas da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Barau I. Jibrin da wasu manyan jami’an gwamnati.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Katolika ta horar da shugabannin al’umma da na addini kan zaman lafiya
  • Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya
  • Sin Na Son Taka Rawar Gani Wajen Maido Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Sauri
  • Tinubu na ƙaddamar da wasu ayyuka a Jihar Kaduna
  • Ba Atiku kaɗai ba ne matsalar PDP — Gwamna Lawal
  • An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina
  • Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi
  • Sojojin Nijeriya sun kashe gomman ’yan ta’adda a Tafkin Chadi
  • EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kwaso ‘Yan Nijeriya Da Suka Maƙale A Isra’ila Da Iran