A cikin wata daya kadai sojojin HKI sun rushe gidajen Falasdinawa 152 a yammacin Kogin Jordan.

Majiyar Falasdinawa ta ambaci cewa a kudancin garin Khalil ‘yan mamayar sun rushe gidaje 25 da kuma wasu cibiyoyi, da hakan ya sa adadin gidajen da su ka rushe zuwa 152 kamar yadda hukumar Falasdinu ta ambata.

Bugu da kari, majiyar Falasdinawan ta ce, ‘yan mamayar sun kuma aike wa da wasu cibiyoyin da gidaje 46 gargadin cewa za su rushe su, da yin kira da  su fice daga cikinsu.

Wata cibiyar ta Falasdinawa ta ce fada wa kamfanin dillancin labarun “Anatoli’ cewa; ;yan mamayar sun rushe gidaje 96 da mutane suke rayuwa a cikinsu, sai kuma wasu gidaje 10 da babu mutane a ciki.Haka nan kuma rusau din ya shafi wasu cibiyoyin noma 34.

Mafi yawancin gidajen da aka rushe dai suna a yankin Tubas ne, Khalil sannan kuma da birnin Kudus.

Wani rahoto ya ambaci cewa; A cikin watan da ya gabata,’yan mamaya suna nazarin gina matsugunan ‘ya share wuri zauna 27 a cikin birnin Kudus.

A gefe daya, ‘yan share wuri zauna din sun kai hare-hare akan Falasdinawa har sau 1693 wanda ya fara a cikin watan Afrilu. Hare-haren kuwa sun hada lalata hanyoyi da tunbuke bishiyoyi, a kwace filayen Falasdinawa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Kammala Horon Hadin Gwiwa Tsakanin Sojojin Saman Sin Da Masar Cikin Nasara

Da safiyar jiya Lahadi bisa agogon wurin, aka kammala horon hadin gwiwa tsakanin sojojin saman kasashen Sin da Masar mai suna “Shaho na wayewar kai-2025” cikin nasara, a wani sansanin sojojin saman Masar, wanda ya kwashe kwanaki guda 18.

 

Wannan horon na hadin gwiwa shi ne karo na farko da rundunar sojin saman kasar Sin ta aike da dakaru zuwa kasashen Afirka domin ba da horon hadin gwiwa. A yayin horon na hadin gwiwa, sojojin saman kasashen Sin da Masar sun tattauna tare da yin musayar ra’ayi kan nau’o’in horarwa, da dabarun yaki da jiragen sama, da samar da man fetur a sama da dai sauransu, kuma sun samu nasarar kammala horarwa kan ayyukan sarrafa jiragen sama, da kiyaye tsaron sararin sama, da ceton mutane a fagen yaki, da yin darussan hadin gwiwa da dai sauransu, wannan wani mafari ne da kuma ci gaba a kan hanyar hadin gwiwar soji tsakanin kasashen biyu. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kammala Horon Hadin Gwiwa Tsakanin Sojojin Saman Sin Da Masar Cikin Nasara
  • Sojojin Sudan Da ‘Yan Tawayen Kasar Suna Ci Gaba Da Gwabza Fada A Wasu Saasan Kasar
  • HKI Ta Tabbatar Da Halakar Sojojinta 2 A Yankin Rafa Na Zirin Gaza
  • Kissoshin Rayuwa : Imam Al-Hassan (a) 113
  • An kammala Bada Horo Ga Matan Sojojin Runduna Ta 8 Da Ke Sakkwato
  • Sojojin Sun Kakkabe Wasu Manyan ‘Yan Bindiga A Zamfara
  • Pakistan Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Mai Cin Tazarar Kilo Mita Fiye Da 400
  • Yadda sojoji suka kashe manyan ’yan bindiga 5 a Zamfara
  • Falasdinawa 40 Ne suka Yi Shahada A Zirin Gaza Sakamakon Ta’addancin Sojojin Mamayar Isra’ila A Jiya Juma’a