Gwamnan Sakkwato, Dokta Ahmad Aliyu ya bayyana ƙarara cewa gwamnatinsa ta kasa cika alƙawarin da ta yi wa ma’aikatan gwamnatin jihar kusan shekara ɗaya kenan.

Gwamnan ya bayyana hakan a yayin bikin Ranar Ma’aikata da aka gudanar a makon da ya gabata.

Lakurawa sun kashe ’yan bijilanti 11 a Sakkwato Ya kamata a zuba jari a harkar noman rani — Zulum

Ya bayyana cewa nan ba da jimawa ba za a biya kuɗin goron sallah babba na naira dubu talatin-talatin da ya ba da umarnin a bai wa ma’aikatan ƙananan hukumomi amma wasu suka yi sama da faɗi da kuɗin.

Gwamna ya bai wa ma’aikata tabbacin nan ba da jimawa ba za raba kuɗin ga waɗanda ke da haƙƙi kamar yadda tsarin biyan kuɗin sallah ya kasance a shekarar da ta gabata.

A yayin bikin sallah babba na shekarar da ta gabata ce gwamnan ya amince a baiw a kowane ma’aikaci a jihar naira dubu 30 don sauƙaƙa musu bukin sallah babba, sai dai har zuwa yanzu da yawan ma’aikatan da malaman firamare ba su samu nasu ba.

Sai dai baya aka sanar da ma’aikata da malaman ƙananan hukumomin cewa an yi sama da faɗi da kuɗin da aka ce a ba su.

Gwamna ya bayyana cewa ya ba da umarnin a fitar da miliyan 500 duk wata haɗi da wasu naira miliyan 300 domin biyan waɗanda suka yi ritaya daga shekarar 2023 zuwa yanzu.

Ya ba da sanarwar ƙaddamar da shagon sauki na Amadun Alu domin sayar da kayan masarufi a cikin sauƙi ga ma’aikata.

Ya yi kira ga ma’aikata su zama masu kula da aiki da sadaukarwa domin ci gaban jihar.

A jawabinsa, shugaban ƙungiyar ƙwadago ta jihar, Abdullahi Aliyu ya yaba wa gwamnan kan fifita walwalar ma’aikata.

Shugaban ya gode wa gwamna kan biyan mafi ƙarancin albashi na naira dubu 70 ga ma’aikata.

“Mun samu farin ciki ƙwarai musamman yadda na jagoranci tantance ma’aikata domin fitar da na bogi a tsarin biyan ma’aikata.”

A cewarsa, kwamitin ya samu ci gaba sosai, inda aka cire ma’aikatan bogi da ke cin kuɗin mutane ba da haƙƙi ba.

Ya ce ƙungiyarsu za ta ci gaba da taimakon gwamnati don samun nasara.

Masana a jihar suna ganin gwamna bai da wani dalilin rashin biyan kuɗin ga ma’aikata, lamarin da suka bayyana a matsayin kasawa ce ƙarara daga ɓangaren gwamnatinsa.

Sun bayyana cewa “gwamnati ta kasa ne kawai ba don haka ba umarnin gwamna ba wasa ba ne da har wani zai kasa biyayya gare shi, hakan ya sa gwamnan da kansa bai bayar da wani dalili ba saboda ya kasa ga cika alƙawarin da ya ɗauka.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Sakkwato wa ma aikata

এছাড়াও পড়ুন:

An yanke wa Soja hukuncin kisa ta hanyar rataya

Wata babbar kotun sojin Najeriya da ke zamanta a sansanin sojoji ta Maxwell Khobe da ke garin Jos a Jihar Filato ta yanke wa wani soja mai suna Lukman Musa hukuncin kisa ta hanyar rataya.

An yanke wa Musa hukuncin kisa ne a ranar Alhamis bayan da aka same shi da laifuka biyu kan kisan gilla da aka yi wa wani direban babur mai ƙafa uku mai suna Abdulrahman Isa a garin Azare na Jihar Bauchi.

Wani ya sace munduwar Fir’auna a gidan tarihin Masar ’Yan sanda sun kama mutum 9 kan yin garkuwa da kansu

Daily Trust ta ruwaito cewa, an fara shari’ar Musa ne a farkon watan Agustan 2025 bayan kama shi biyo bayan binciken haɗin gwiwa da jami’an sojoji sashin harkokin da hukumomin yankin suka gudanar.

Al’amarin ya ja hankalin jama’a sosai saboda tsananin mugun halin da aka aikata da kuma yunkurin tauye amanar jama’a da sojan ya yi.

Shugaban Kotun Sojojin Najeriya ta 3, Birgediya-Janar, Liafis Bello ya ce an samu sojan da laifin kisan kai da kuma mallakar harsasai ba bisa ƙa’ida ba.

Kotun ta tabbatar da cewa, shaidun da aka gabatar a lokacin shari’ar sun nuna cewa, Musa ya haɗa baki da wani mai suna Mista Oba, domin su kai Isa gidansa da zargin taimaka masa wajen kwashe kayansa.

Ya ƙara da cewa Musa ya bugi Isa a kai da wani abu na katako, inda ya sume, kafin ya shaƙe shi ya mutu.

A ƙoƙarinsu na ɓoye laifin, Musa da abokinsa sun cusa gawar wanda aka kashe a cikin buhu tare da jefa ta a tsakanin ƙauyukan Shira da Yala a Jihar Bauchi.

“An sayar da babur mai ƙafa uku na Isa daga baya, wanda ya ƙara fallasa yadda aka tsara yadda lamarin ya faru,” in ji masu gabatar da ƙara na soji yayin shari’ar.

Hakazalika sun bayyana cewa a binciken da ake yi, an samu Musa da harsashi na musamman har guda 34 na nau’in 7.62mm ba tare da wata izinin doka ba.

Da yake yanke hukuncin, Birgediya Janar Bello ya bayyana abin da Musa ya yi a matsayin “abin kunya, rashin tausayi da kuma cin zarafi da rahin a ɗa’a da kimar sojoji.”

“Ka nuna rashin tausayi daga mai kare ’yan ƙasa zuwa mai kisan gilla, matakin da kuka ɗauka abin kunya ne kuma abin kunya ga Sojojin Najeriya,” in ji kotun.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An yanke wa Soja hukuncin kisa ta hanyar rataya
  • Shugabar Ma’aikata Ta Jihar Kaduna Ta Yi Kiran Amfani Da Fasahar AI.
  • Gwamnatin Tarayya ta raba wa talakawa N330bn — Ministan Kuɗi
  • Mataimakin Gwamnan Zamfara Ya Jajantawa Al’ummar Gumi
  • ’Yan bindiga sun sako ma’auratan da suka sace a Katsina bayan biyan N50m
  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025