Abin da ya hana ni cika alƙawarin da na yi wa ma’aikata — Gwamnan Sakkwato
Published: 4th, May 2025 GMT
Gwamnan Sakkwato, Dokta Ahmad Aliyu ya bayyana ƙarara cewa gwamnatinsa ta kasa cika alƙawarin da ta yi wa ma’aikatan gwamnatin jihar kusan shekara ɗaya kenan.
Gwamnan ya bayyana hakan a yayin bikin Ranar Ma’aikata da aka gudanar a makon da ya gabata.
Lakurawa sun kashe ’yan bijilanti 11 a Sakkwato Ya kamata a zuba jari a harkar noman rani — ZulumYa bayyana cewa nan ba da jimawa ba za a biya kuɗin goron sallah babba na naira dubu talatin-talatin da ya ba da umarnin a bai wa ma’aikatan ƙananan hukumomi amma wasu suka yi sama da faɗi da kuɗin.
Gwamna ya bai wa ma’aikata tabbacin nan ba da jimawa ba za raba kuɗin ga waɗanda ke da haƙƙi kamar yadda tsarin biyan kuɗin sallah ya kasance a shekarar da ta gabata.
A yayin bikin sallah babba na shekarar da ta gabata ce gwamnan ya amince a baiw a kowane ma’aikaci a jihar naira dubu 30 don sauƙaƙa musu bukin sallah babba, sai dai har zuwa yanzu da yawan ma’aikatan da malaman firamare ba su samu nasu ba.
Sai dai baya aka sanar da ma’aikata da malaman ƙananan hukumomin cewa an yi sama da faɗi da kuɗin da aka ce a ba su.
Gwamna ya bayyana cewa ya ba da umarnin a fitar da miliyan 500 duk wata haɗi da wasu naira miliyan 300 domin biyan waɗanda suka yi ritaya daga shekarar 2023 zuwa yanzu.
Ya ba da sanarwar ƙaddamar da shagon sauki na Amadun Alu domin sayar da kayan masarufi a cikin sauƙi ga ma’aikata.
Ya yi kira ga ma’aikata su zama masu kula da aiki da sadaukarwa domin ci gaban jihar.
A jawabinsa, shugaban ƙungiyar ƙwadago ta jihar, Abdullahi Aliyu ya yaba wa gwamnan kan fifita walwalar ma’aikata.
Shugaban ya gode wa gwamna kan biyan mafi ƙarancin albashi na naira dubu 70 ga ma’aikata.
“Mun samu farin ciki ƙwarai musamman yadda na jagoranci tantance ma’aikata domin fitar da na bogi a tsarin biyan ma’aikata.”
A cewarsa, kwamitin ya samu ci gaba sosai, inda aka cire ma’aikatan bogi da ke cin kuɗin mutane ba da haƙƙi ba.
Ya ce ƙungiyarsu za ta ci gaba da taimakon gwamnati don samun nasara.
Masana a jihar suna ganin gwamna bai da wani dalilin rashin biyan kuɗin ga ma’aikata, lamarin da suka bayyana a matsayin kasawa ce ƙarara daga ɓangaren gwamnatinsa.
Sun bayyana cewa “gwamnati ta kasa ne kawai ba don haka ba umarnin gwamna ba wasa ba ne da har wani zai kasa biyayya gare shi, hakan ya sa gwamnan da kansa bai bayar da wani dalili ba saboda ya kasa ga cika alƙawarin da ya ɗauka.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Sakkwato wa ma aikata
এছাড়াও পড়ুন:
Kiwon Lafiya: Jihar Kwara Ta Bayyana Yadda Karancin Likitoci Ke Kawo Mata Cikas
Dakta Abdulmalik ya ce, a halin yanzu gwamnatin jihar na da likitoci 99 kadai ne, wadanda ke kan tsarin albashi, ya kara da cewa; adadin da ake bukata kuma sun kai kimanin 180 zuwa 200.
“Likitoci ukun da suka bar aiki, sun dawo bayan karin albashin likitocin da gwamnan ya yi a baya-bayan nan. Don haka, a da muna da likitoci 96, amma bayan karin albashin da gwamnan ya yi, uku da suka bar aikin sun dawo. Saboda haka, a halin yanzu muna da likitoci 99. Kazalika, muna da bukatar kari, domin kuwa kimanin likitoci 180 zuwa 200 muke bukata.”
Saboda haka, hukumar ta ce; tana kokarin samar da wata manhaja da za ta bai wa marasa lafiya, domin ziyartar cibiyoyin kiwon lafiya 45 da kuma samun bayanai kan adadin likitocin da ake da su a kowane lokaci, domin rage jinkirin da aka saba samu na ganin likita.
Ya ce, hakan kuma zai rage yanayin da marasa lafiya kan samu kansu ko kuma fita daga hayyacinsu kafin su ga likita a asibiti.
Babban Sakataren ya kara da cewa, yankunan karkara su ne wuraren da kalubalen ya fi yin kamari, ya ci gaba da cewa; hukumar na aikin samar da kudaden alawus-alawus ga likitocin, domin magance lamarin da kuma samar da kayan aiki.
“Albashin zai kasance daidai da abin da ake biya a kasashen Turai, inda yawaicin likitocin ke arcewa a matsayin balaguro”, in ji shi.
Dakta Abdulmalik ya ce, akwai wani shiri da gwamnatin jihar ke yi na kokarin cike gibin da ake da shi a bangaren likitocin jihar, inda ya ce shirin zai fara nan shekara hudu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp