Gwamnan Sakkwato, Dokta Ahmad Aliyu ya bayyana ƙarara cewa gwamnatinsa ta kasa cika alƙawarin da ta yi wa ma’aikatan gwamnatin jihar kusan shekara ɗaya kenan.

Gwamnan ya bayyana hakan a yayin bikin Ranar Ma’aikata da aka gudanar a makon da ya gabata.

Lakurawa sun kashe ’yan bijilanti 11 a Sakkwato Ya kamata a zuba jari a harkar noman rani — Zulum

Ya bayyana cewa nan ba da jimawa ba za a biya kuɗin goron sallah babba na naira dubu talatin-talatin da ya ba da umarnin a bai wa ma’aikatan ƙananan hukumomi amma wasu suka yi sama da faɗi da kuɗin.

Gwamna ya bai wa ma’aikata tabbacin nan ba da jimawa ba za raba kuɗin ga waɗanda ke da haƙƙi kamar yadda tsarin biyan kuɗin sallah ya kasance a shekarar da ta gabata.

A yayin bikin sallah babba na shekarar da ta gabata ce gwamnan ya amince a baiw a kowane ma’aikaci a jihar naira dubu 30 don sauƙaƙa musu bukin sallah babba, sai dai har zuwa yanzu da yawan ma’aikatan da malaman firamare ba su samu nasu ba.

Sai dai baya aka sanar da ma’aikata da malaman ƙananan hukumomin cewa an yi sama da faɗi da kuɗin da aka ce a ba su.

Gwamna ya bayyana cewa ya ba da umarnin a fitar da miliyan 500 duk wata haɗi da wasu naira miliyan 300 domin biyan waɗanda suka yi ritaya daga shekarar 2023 zuwa yanzu.

Ya ba da sanarwar ƙaddamar da shagon sauki na Amadun Alu domin sayar da kayan masarufi a cikin sauƙi ga ma’aikata.

Ya yi kira ga ma’aikata su zama masu kula da aiki da sadaukarwa domin ci gaban jihar.

A jawabinsa, shugaban ƙungiyar ƙwadago ta jihar, Abdullahi Aliyu ya yaba wa gwamnan kan fifita walwalar ma’aikata.

Shugaban ya gode wa gwamna kan biyan mafi ƙarancin albashi na naira dubu 70 ga ma’aikata.

“Mun samu farin ciki ƙwarai musamman yadda na jagoranci tantance ma’aikata domin fitar da na bogi a tsarin biyan ma’aikata.”

A cewarsa, kwamitin ya samu ci gaba sosai, inda aka cire ma’aikatan bogi da ke cin kuɗin mutane ba da haƙƙi ba.

Ya ce ƙungiyarsu za ta ci gaba da taimakon gwamnati don samun nasara.

Masana a jihar suna ganin gwamna bai da wani dalilin rashin biyan kuɗin ga ma’aikata, lamarin da suka bayyana a matsayin kasawa ce ƙarara daga ɓangaren gwamnatinsa.

Sun bayyana cewa “gwamnati ta kasa ne kawai ba don haka ba umarnin gwamna ba wasa ba ne da har wani zai kasa biyayya gare shi, hakan ya sa gwamnan da kansa bai bayar da wani dalili ba saboda ya kasa ga cika alƙawarin da ya ɗauka.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Sakkwato wa ma aikata

এছাড়াও পড়ুন:

Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda

A cewar ta a cikin shekarar 2024 jihar Katsina kawai ta samu masu wannan cuta mutum 17 tare da guda biyu a karamar hukumar Danmusa a cikin wannan shekara

Haka kuma Hajiya Zulaihat Radda ya bada tabbacin cewa kowane yaro an tabbatar da ya amshi allurar Riga-kafin shan Inna

Ana jawabin wakilin asusun tallafawa yara na UNICEF na ofishin Kano, Rahama Mohammed Farah ta yabawa kokarin jihar Katsina na dawo da sabon yunkurin kawar cutar shan Inna a Nijeriya baki daya

Ya kuma bayyana cewa asusun kula da kananan yara na UNICEF Yana hadin gwiwa da gwamnatoci da hukumomi da masu ruwa da tsaki a kananan hukumomi domin ganin wajen fadakar da al’umma akan allurar Riga-kafin shan Inna a jihar Katsina.

Shima da yake jawabi shugaban hukumar lafiya a matakin farko ta Jihar Katsina Dakta Shansudeen Yahaya ya yi alkawarin cigaba da wayar da kan al’umma akan wannan cuta ta shan Inna da sauran cututtuka masu kashe yara a kananan hukumomi 34 na jihar Katsina

Wadanda suka shaida wannan bikin ranar ‘Polio’ ta duniya sun hada da hukumar lafiya ta WHO da kuma masu lalurar cutar shan Inna da wakilan asusun UNICEF da matan shugabannin kananan hukumomi 34 na jihar Katsina

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi October 31, 2025 Manyan Labarai Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai October 31, 2025 Manyan Labarai Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda matata ta ɓace a Abuja aka tsince ta a Sakkwato
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
  • Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda
  • Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai