Yayin da aka tabo batun manufofin cinikayya da gwamnatin Trump ta dauka, Newsom ya ce, dalilin da ya sa ya soki matakan na gwamnatin Trump shi ne, jihar California ta fi fama da mummunan tasirin da manufofin suka haifar sama da sauran jihohin kasar.

 

Tun bayan da shugaba Trump ya sanar da matakin kakaba haraji a watan Afirilu, Newsom ta yi kira ga kasashe masu karfin tattalin arziki da ke wajen Amurka, da kada su sanya harajin ramuwar gayya kan kayayyakin da ake fitarwa daga jihar California.

Kazalika, California ce jihar farko da ta kai karar gwamnatin Trump kan batun harajin. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Zulum zai mayar da ’yan gudun hijira 5,000 Bama

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya ce gwamnatinsa na shirin mayar da mutum 5,000 gida daga sansanin ‘yan gudun hijira kafin wucewar damina domin su samu damar yin noma.

Mutanen za su fito ne daga garuruwan Goniri, Bula Kuriye, Mayanti, Abbaram, da Darajamal.

Ma’aikatan jinya sun dakatar da yajin aiki a faɗin Najeriya Rufe gidan rediyo ya haifar da cece-ku-ce a Neja

Gwamnan, ya bayyana hakan ne lokacin da ya kai wa Mai Martaba Shehun Bama, Dakta Umar ibn Kyari Umar El-Kanemi, ziyara a fadarsa da ke Bama.

Ya ce an riga an kammala gina matsuguni 1,000 a Darajamal, sannan kuma aikin gina wasu a sauran garuruwan hudu.

“Mun ƙudiri aniyar dawo da ‘yan gudun hijira gida. A Mayanti, Goniri, Bula Kuriye da Abbaram muna gina gidaje, na Darajamal kuma an riga an gama,” in ji Gwamnan.

Ya ƙara da cewa gwamnati za ta kewaye yankunan da rami domin inganta tsaro.

Zulum, ya jaddada muhimmancin noma a rayuwar al’umma.

“Muna so mutanen da za a dawo da su gida su samu damar yin noma, saboda noma shi ne abin dogaron rayuwa a Borno,” in ji shi.

Ya ce zai gana da shugabannin JTF da Civilian JTF domin tsara yadda za a kare lafiyar manoma da gonaki.

Haka kuma, Zulum ya shaida wa Shehun Bama cewa gwamnatinsa ta ƙara tsaurara tsaro a garin Nguro Soye, domin samun damar yin noma.

“Daga dawowa daga Gwoza, na tsaya a sansanin sojoji da ke kusa da Banki, inda muka tattauna yadda za a tsaurara tsaro a Nguro Soye. Na bai wa sojoji da Civilian JTF kayan aiki kuma na yi alƙawarin biyan ‘yan sa-kai da ke sintiri alawus ɗin watanni shida da suka wuce,” in ji Gwamnan.

A nasa ɓangaren, Mai Martaba Shehun Bama ya yaba wa Zulum bisa ƙoƙarinsa na kyautata tsaro da jin daɗin jama’a.

“Ina yi wa gwamna godiya saboda dawo da mutanen Darajamal gida. Muna fatan sauran mutane ma za su dawo gida cikin kwanciyar hankali,” in ji Shehun.

Shehun, ya kuma roƙi gwamnatin da ta ƙara tallafa wa Civilian JTF domin kare manoma da gonaki a lokacin damina.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 
  • Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara
  • Gwamnan Neja Ya Bada Umarnin Sake Bude Jami’ar Ibrahim Badamasi Babangida, Lapai.
  • Gwamnan Jihar Kwara Ya Hori Sabbin Matasa Masu Yiwa Kasa Hidima Akan Kishin Kasa
  • Gwamnatin Sakkwato Za Ta Kashe fiye da Naira Miliyan 200 Wajen Gyara Tashar Talabijin Ta Kasa NTA
  • Gwamnatin Jigawa Ta Dauki Manyan Matakan Kare Jihar Daga Ambaliyar Ruwa
  • Zulum zai mayar da ’yan gudun hijira 5,000 Bama
  • Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya
  • HOTUNA: Yadda aka yi Jana’izar Sarkin Gudi na Yobe bayan rasuwarsa a Abuja
  • Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine