Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-05-04@13:45:29 GMT

Ghana Za Ta Hada Gwiwa Da Gwamnatin Jihar Kebbi Kan Noma

Published: 4th, May 2025 GMT

Ghana Za Ta Hada Gwiwa Da Gwamnatin Jihar Kebbi Kan Noma

Ministan Abinci da Noma na Jamhuriyar Ghana Mista Eric Opoku, ya ce Ghana za ta hada gwiwa da gwamnatin jihar Kebbi domin bunkasa noman shinkafa a kasarsa.

 

Ministan ya bayyana haka ne a lokacin da ya ziyarci mataimakin gwamnan jihar Kebbi Sanata Umar Abubakar a Birnin Kebbi.

 

Ya bayyana cewa, sabuwar gwamnatin Ghana da ta fara aiki watanni hudu da suka gabata, tana neman hanyoyin magance kalubalen samar da abinci a kasar.

 

A cewar Ministan, sabuwar gwamnatin ta gaji wani katafaren kudi na shigo da kaya inda ta ke shigo da shinkafa da yawa duk kuwa da kasa mai albarka da ruwa mai yawa, wanda zai iya tallafawa noman cikin gida.

 

Mista Opoku ya yi nuni da cewa, kasar Ghana ta samu kwarin gwuiwa ne sakamakon nasarar da jihar Kebbi ta samu a fannin noman shinkafa, wanda shi ne babban makasudin ziyarar da suka kai.

 

Da yake mayar da jawabi, mataimakin gwamnan jihar Kebbi Sanata Umar Abubakar, a lokacin da yake maraba da tawagar kasar Ghana tare da nuna sha’awarsu na hadin gwiwa a fannin noma da gwamnatin jihar Kebbi, ya bayyana cewa jihar a shirye take ta hada kai da kasar Ghana, musamman a fannin noma.

 

Ya ce, baya ga aikin noma, jihar ta samu albarkar ma’adanai irin su Zinariya da Lithium, wadanda a shirye suke don bincike.

 

COV/Abdullahi Tukur

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: jihar Kebbi

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar Hizbullahi Ta Lebanon Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya Suka Kai Kan Kasar Siriya

Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hizbullah ta kasar Lebanon ta yi Allah wadai da harin wuce gona da irin da ‘yan sahayoniyya suke yi kan kasar Siriya

Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hizbullah ta kasar Lebanon ta yi Allah-wadai da harin bam da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai a Siriya a ranar Asabar.

A cikin wata sanarwa da kungiyar ta Hizbullahi ta fitar ta ce: Tana jaddada tofin Allah tsine da yin Allah wadai da zaluncin yahudawan sahayoniyya da suka addabi kasar Siriya a wani mummunan hari da suka kai kan yankunan kasar, tare da fakewa da munanan kalamai da take-take na aiwatar da ayyukanta na fadadawa da wargaza kasar Siriya da nufin rusa hadin kan kasar da kuma haifar da fitina a tsakanin al’ummarta.”

Kungiyar ta kuma jaddada cewa: Wannan wuce gona da iri na yahudawan sahayoniyya wani yunkuri ne karara na gurgunta zaman lafiyar kasar Siriya da raunana karfinta, kuma hakan na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da kai hare-hare a kan kasar Lebanon da zirin Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Share Filin Noma Kadada 100 Don Karfafa Matasa Su Yi Noma A Babura Jihar Jigawa
  • Kungiyar Hizbullahi Ta Lebanon Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya Suka Kai Kan Kasar Siriya
  • Hajjin Bana: Gwamnatin Jigawa ta aika wa NAHCON Naira biliyan 6 
  • Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja
  • Sashen Yawon Shakatawa Na Teku A Kasar Sin Ya Samu Gagarumin Ci Gaba A Rubu’in Farkon Bana
  • HOTUNA: Yadda aka tarbi Shugaba Tinubu a Katsina
  • NLC Kano Ta Yabawa Gwamnati Na Kokarin Kyautata Jin Dadin Ma’aikata
  • Gwamnan Kabawa Ya Tabbatarwa Ma’aikatan Gwamnati Ingantacciyar Walwala
  • Ministan Tsaron Iran Ya Bayyana Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya A Matsayar Alamar Yan Ta’adda