Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-08-03@16:43:05 GMT

Ghana Za Ta Hada Gwiwa Da Gwamnatin Jihar Kebbi Kan Noma

Published: 4th, May 2025 GMT

Ghana Za Ta Hada Gwiwa Da Gwamnatin Jihar Kebbi Kan Noma

Ministan Abinci da Noma na Jamhuriyar Ghana Mista Eric Opoku, ya ce Ghana za ta hada gwiwa da gwamnatin jihar Kebbi domin bunkasa noman shinkafa a kasarsa.

 

Ministan ya bayyana haka ne a lokacin da ya ziyarci mataimakin gwamnan jihar Kebbi Sanata Umar Abubakar a Birnin Kebbi.

 

Ya bayyana cewa, sabuwar gwamnatin Ghana da ta fara aiki watanni hudu da suka gabata, tana neman hanyoyin magance kalubalen samar da abinci a kasar.

 

A cewar Ministan, sabuwar gwamnatin ta gaji wani katafaren kudi na shigo da kaya inda ta ke shigo da shinkafa da yawa duk kuwa da kasa mai albarka da ruwa mai yawa, wanda zai iya tallafawa noman cikin gida.

 

Mista Opoku ya yi nuni da cewa, kasar Ghana ta samu kwarin gwuiwa ne sakamakon nasarar da jihar Kebbi ta samu a fannin noman shinkafa, wanda shi ne babban makasudin ziyarar da suka kai.

 

Da yake mayar da jawabi, mataimakin gwamnan jihar Kebbi Sanata Umar Abubakar, a lokacin da yake maraba da tawagar kasar Ghana tare da nuna sha’awarsu na hadin gwiwa a fannin noma da gwamnatin jihar Kebbi, ya bayyana cewa jihar a shirye take ta hada kai da kasar Ghana, musamman a fannin noma.

 

Ya ce, baya ga aikin noma, jihar ta samu albarkar ma’adanai irin su Zinariya da Lithium, wadanda a shirye suke don bincike.

 

COV/Abdullahi Tukur

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: jihar Kebbi

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji
  • HOTUNA: Yadda aka yi Jana’izar Sarkin Gudi na Yobe bayan rasuwarsa a Abuja
  • Firayim Ministan Senegal Ya Bayyana Sabon Shirin Farfado Da Tattalin Arzikin Kasar
  • Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa
  • Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar
  • NBRDA Za Ta Hada Gwiwa Da KIRCT Domin Habaka Magunguna Da Yaki Da Cututtuka
  • An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano
  • Gwamnatin Jigawa ta horas da malamai 20,000 fasahar sadarwar zamani