HausaTv:
2025-05-04@06:45:36 GMT

 Iran Ta Yi Allawadai Da Hare-haren HKI Akan Syria Da Nufin Rusa Kasar

Published: 3rd, May 2025 GMT

 Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran Isma’ila Baka’i ya bayyana cewa; Manufar HKI akan Syria a fili take ba a boye ba.”

Baka’i ya ci gaba da cewa; Manufar HKI  ita ce rusa duk wani karfi da Syria take da shi na yaki, da kuma lalata tattalin arzikinta, domin share fagen shimfida iko a kasar da kuma a cikin wannan yankin.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya kuma ci gaba da cewa; matsayin jamhuriyar musulunci ta Iran akan kasar Syria, a fili yake wanda shi ne kare hadin kan wannan kasa da hana ta tarwatsewa da kare daukakarta a matsayinta na kasa mai ‘yanci da kuma al’umma mai tsawo tarihi na ci gaba,sannan kuma mai tasiri a cikin wannan yanki na yammacin Asiya.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen na Iran ya dora alhakin abinda yake faruwa a Syria, akan dukkanin wadanda su ka taka rawa wajen jefa kasar cikin halin da take a  yanzu.

Wuraren da HKI ta kai wa hare-hare a daren jiya sun hada da sansanin sojan runduna ta 47 da sojoji Syria dake yankin Humah ta yamma, haka nan kuma rumbun ajiyar makamai na sojan sama a kusa da garub shahdaha, da ya jikkata mutane 4,kamar yadda kamfanin dillancin labaurn “SANA” na kasar ta Syria ya nakalto.

A birnin Damascuss ma sojojin HKI sun kai wasu hare-haren da su ka hada da kusa da fadar shugaban kasa. Kafafen watsa labaru sun ambci shahadar mutum daya, da kuma jikkatar wasu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Dakarun Kai Daukin Gaggawa Sun Kashe Fararen Hula Kusan 300 A Hare-Haren Baya-Bayan Nan A Sudan

Ana gwabza kazamin fada a Sudan, inda dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces suka kashe fararen hula kusan 300

A tsakiyar bala’in Sudan, ana ci gaba da gwabza kazamin fada tsakanin sojojin Sudan da dakarun kai daukin gaggawa, a daidai lokacin da ake fama da munanan ayyukan jin kai da ke ba da mummunan hoto kan makomar kasar.

A yammacin jihar Kordofan, sojojin kasar Sudan sun sanar da janyewa daga birnin Nahud, bayan kazamin fada da dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces, wadanda suka sanar da kwace iko da birnin da kuma hedikwatar Brigade ta sha takwas, baya ga birnin Al-Khawi.

Yayin da ake ci gaba da gwabza fada, gwamnatin Sudan ta zargi dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces da aikata munanan laifuka kan fararen hula a birnin Nahud, da suka hada da kisan kai, sace-sacen dukiya da lalata cibiyoyi. Ta kuma sha alwashin hukunta wadanda ke da hannu a aikata wadannan muggan laifuka da kuma kasashen da ke tallafa musu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Yaba Da Sadaukarwar Da ‘Yan Jarida Suka Bayar Kan Watsa Wahalhalun Falasdinawa
  • Kungiyar Hizbullahi Ta Lebanon Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya Suka Kai Kan Kasar Siriya
  • Dakarun Kai Daukin Gaggawa Sun Kashe Fararen Hula Kusan 300 A Hare-Haren Baya-Bayan Nan A Sudan
  •  Syria: A Karon Farkon Jirgi Mai Saukar Angulu Na HKI Ya Sauka A Yankin Suwaidah
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Sokin Kasar Faransa Kan Mummunar Rawar Da Take Son Takawa Kan Iran
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Yi Kakkausar Suka Kan Hare-Haren Jiragen Saman Amurka Kan Kasar Yemen
  • Jiragen Saman Yakin Sojojin Isra’ila Sun Kai Hare-Haren Wuce Gona Da Iri Kan Kasar Siriya
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Ce Kasar Oman Ce Ta Bukaci Dage Zaman Tattaunawan Iran Da Amurka
  • Syria: Adadin Wadanda Aka Kashe A Rikicin Bangaranci Sun Kai 70