Iran Ta Yi Allawadai Da Hare-haren HKI Akan Syria Da Nufin Rusa Kasar
Published: 3rd, May 2025 GMT
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran Isma’ila Baka’i ya bayyana cewa; Manufar HKI akan Syria a fili take ba a boye ba.”
Baka’i ya ci gaba da cewa; Manufar HKI ita ce rusa duk wani karfi da Syria take da shi na yaki, da kuma lalata tattalin arzikinta, domin share fagen shimfida iko a kasar da kuma a cikin wannan yankin.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya kuma ci gaba da cewa; matsayin jamhuriyar musulunci ta Iran akan kasar Syria, a fili yake wanda shi ne kare hadin kan wannan kasa da hana ta tarwatsewa da kare daukakarta a matsayinta na kasa mai ‘yanci da kuma al’umma mai tsawo tarihi na ci gaba,sannan kuma mai tasiri a cikin wannan yanki na yammacin Asiya.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen na Iran ya dora alhakin abinda yake faruwa a Syria, akan dukkanin wadanda su ka taka rawa wajen jefa kasar cikin halin da take a yanzu.
Wuraren da HKI ta kai wa hare-hare a daren jiya sun hada da sansanin sojan runduna ta 47 da sojoji Syria dake yankin Humah ta yamma, haka nan kuma rumbun ajiyar makamai na sojan sama a kusa da garub shahdaha, da ya jikkata mutane 4,kamar yadda kamfanin dillancin labaurn “SANA” na kasar ta Syria ya nakalto.
A birnin Damascuss ma sojojin HKI sun kai wasu hare-haren da su ka hada da kusa da fadar shugaban kasa. Kafafen watsa labaru sun ambci shahadar mutum daya, da kuma jikkatar wasu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Yi Kira Ga Iran Da Isra’ila Su Dauki Matakan Dakile Ruruwar Wutar Rikicinsu Nan Da Nan
Yau Litinin, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin, Guo Jiakun ya gudanar da taron manema labarai na yau da kullum.
Game da halin da ake ciki yanzu a yankin Gabas ta Tsakiya, Guo Jiakun ya ce, ministan wajen Sin Wang Yi ya riga ya tattauna ta waya tare da takwarorinsa na Iran da Isra’ila, inda ya yi kira ga bangarorin biyu su warware rikicin ta hanyar tattaunawa. Ya ce ya kamata bangarorin biyu su dauki matakai nan da nan don hana ruruwar wutar rikicin. Kana Sin za ta ci gaba da yin mu’ammala da bangarorin da abin ya shafa, ta yadda za ta ba da gudunmawa wajen yayyafa ruwa ga rikicin.
Game da taron koli na Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya karo na biyu da za a gudanar ba da jimawa ba, Guo Jiakun ya ce, shugabannin kasar Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya za su tsara hadin gwiwa a nan gaba tare, da inganta gina al’umma mai makoma ta bai-daya ta kasar Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya mai inganci.
Game da batun zamowar kasar Vietnam kawar kungiyar BRICS, Guo Jiakun ya ce, kasar Sin na maraba da Vietnam ta zama kawar BRICS, kuma ana ganin cewa, Vietnam za ta ba da gudummawa mai kyau ga tsarin BRICS.(Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp