HausaTv:
2025-11-03@10:04:01 GMT

 Iran Ta Yi Allawadai Da Hare-haren HKI Akan Syria Da Nufin Rusa Kasar

Published: 3rd, May 2025 GMT

 Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran Isma’ila Baka’i ya bayyana cewa; Manufar HKI akan Syria a fili take ba a boye ba.”

Baka’i ya ci gaba da cewa; Manufar HKI  ita ce rusa duk wani karfi da Syria take da shi na yaki, da kuma lalata tattalin arzikinta, domin share fagen shimfida iko a kasar da kuma a cikin wannan yankin.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya kuma ci gaba da cewa; matsayin jamhuriyar musulunci ta Iran akan kasar Syria, a fili yake wanda shi ne kare hadin kan wannan kasa da hana ta tarwatsewa da kare daukakarta a matsayinta na kasa mai ‘yanci da kuma al’umma mai tsawo tarihi na ci gaba,sannan kuma mai tasiri a cikin wannan yanki na yammacin Asiya.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen na Iran ya dora alhakin abinda yake faruwa a Syria, akan dukkanin wadanda su ka taka rawa wajen jefa kasar cikin halin da take a  yanzu.

Wuraren da HKI ta kai wa hare-hare a daren jiya sun hada da sansanin sojan runduna ta 47 da sojoji Syria dake yankin Humah ta yamma, haka nan kuma rumbun ajiyar makamai na sojan sama a kusa da garub shahdaha, da ya jikkata mutane 4,kamar yadda kamfanin dillancin labaurn “SANA” na kasar ta Syria ya nakalto.

A birnin Damascuss ma sojojin HKI sun kai wasu hare-haren da su ka hada da kusa da fadar shugaban kasa. Kafafen watsa labaru sun ambci shahadar mutum daya, da kuma jikkatar wasu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

El-Zakzaki: Yakin Sudan Yana Kare Maslahar Kasashen Yamma ne Kawai

A wata hira da kafar watsa labarai ta iran press ta yi da jagoran harkar musulunci a najeriya shaikh Ibrahim zakzaki yayi tir da ci gaba da kashe mutane da ake yi a kasar sudan inda kungiyar RSF ta kasashe sama da mutane 2000 a garin el-fishar, ya zargi kasar hadaddiyar daular larabawa da ruruta wutar yaki a madadin kasashen masu girma na duniya.

Yakin basasar dake ci gaba da gudana a kasar sudan ya dauki mummunan yanayi yayin  da kungiyoyin masu samun goyon bayan kasashen waje ke kara kai hare-hare kan fararen hula da basu ji ba basu gani ba, bayanan na shaikh zakzaki sun kara haskaka yanayin siyasar da ke mayar da kasashen afrika fagen yaki don rarrabasu,

Har ila yau shaikh zakzaki yayi tir da mummunan rikicin da ya keta kasar sudan din gida biyu, kana ya jaddada cewa dukkan dakarun sojin kasar sudan da kuma kungiyar RSF yan kasar Sudan ne wadanda suke aiwatar da agenda kasashen waje, yace lamari ne mai taba zuciya a ce dan uwa yana kashe dan uwansa kawai don kare masalar wasu a waje,

Yace kasar hadaddiyar daular larabawa tana aiki ne a madadin kasashen yamma kuma matukar baa yanke hannun kasashen waje ba to yaki ba zai tsaya ba, fararen hula ne kawai zasu ci gaba da zama cikin mawuyacin hali.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Karbi Sako Kan Batun Komawa Teburin Tattaunawa Ba Kai Tsaye Ba November 3, 2025 Ministar Jin Dadin Jama’a ta Sudan: Mayakan RSF Sun Kashe Mata 300 Da Yi Wa 25 Fyade A El Fasher November 3, 2025 Pezeshkian: Bunkasa Masana’antar Makamashin Nukiliyar Iran Don Inganta Rayuwar Al’ummar Iran Ne November 2, 2025 Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran November 2, 2025 Larijani: Iran Ba Ta Tsoron Gudanar Da Tattaunawa, Amma Ta Zama Mai Amfani November 2, 2025 Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza November 2, 2025 Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher November 2, 2025 IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya November 2, 2025 Amurka : zamu dauki matakin soja idan Najeriya ta gaza kawo karshen kashe Kiristoci November 2, 2025 Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza November 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • El-Zakzaki: Yakin Sudan Yana Kare Maslahar Kasashen Yamma ne Kawai
  • Al’ummar Kauru Sun Koka Game Da Karuwar Hare-hare Da Ke Barazana Ga Gonaki Da Rayuka
  • Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran
  • A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
  • Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
  • MDD Tana Sa Ido Akan Kashe-kashen Da Ake Yi A Zaben Kasar Tanzania
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific
  • CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
  • Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC