Limamin Jumma’a A Nan Tehran Ya Ce Iran Tana Da Masu Tattaunawa Da Amurka Kwararru
Published: 2nd, May 2025 GMT
Limamin da ya jagoranci sallar Jumma’a a nan Tehran Hujjatul Islam kazim Sadiki ya bayyana cewa kasar tana da kwararru wadanda suke da kwarewa a sanin fasahar nukliya da kuma hanyoyin dublomasiyya a tattaunawar da Iran take da Amurka dangane da shirin Nukliyar kasar.
Tashar talabijin ta Al-alam a nan Tehran ta nakalto limamin yana fadar haka a khudubobinsa na sallar Jumm’a.
Hujjatul Islam Sadiki ya kara da cewa tawagar Iran a wannan tattaunawar, suna amfani da tajruban da suke da shi a tattaunawar baya, sannan sauran jami’an gwamnati suna sanya ido suna kuma kula da yadda tattaunawar take. Sannan ko way a san cewa wannan tattaunawar tana dimfare da makaman JMI ganin yadda kasar Amurka take barazanar faraway Iran da yaki sannan tana karawa kasar Takunkuman tattalin arziki ana cikin tattaunawar.
Har’ila yau limamin yana yi magana dangane da ranar ‘Malami” a kasar Iran wanda yayi dai-dai da ranar shahadin daya daga cikin jaga-jigan malaman da suka jagoranci juyin juya halin musulunci a kasar a shekara 1979. Wato Aya. Shahid Murtada Muttahari.
Wata batacciyar kungiyar wacce ake kira furkan ce ta kashe Aya. Shahid Muttahari wataki bai 80 da nasarrar juyin juya halin musulunci a kasar.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: a tattaunawar
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka Ta Rufe Ofishin Jakadancinta Da Ke Tel-Aviv Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila
Gwamnatin Amurka ta rufe Ofishin Jakadancinta da ke haramtacciyar kasar Isra’ila
Jakadan Amurka a haramtacciyar kasar Isra’ila Mike Huckabee ya sanar a yau Litinin cewa: Wani makami mai linzami na Iran ya fado kusa da ofishin jakadancin Amurka da ke birnin Tel Aviv, wanda ya yi barna kadan amma ba a samu rauni a tsakanin ma’aikatan ba.
A cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce: Daga yau Litinin ofishin jakadancin da sauran ofisoshin Amurka da suke haramtacciyar kasar Isra’ila za su ci gaba da kasancewa a rufe a matsayin matakin riga-kafi.
Jakadan ya kara da cewa: Babban abin da ya sa a gaba shi ne kare lafiyar jami’an diflomasiyyar kasarsa, kuma za su ci gaba da sanya ido kan abubuwan da ke faruwa tare da hadin gwiwar hukumomin haramtacciyar kasar Isra’ila.