Jami’an tsaro a tarayyar Najeriya sun kama wani jami’in sojan kasar Burtania mai suna Manjor Micah Polo tare da zarginsa da shigo da makamai kasar sannan da kokarin fasa korinsu zuwa wajen kasar.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa, an lama manjo polo ne da makamai wadanda suka hada da MK-47 50, bindiga mai jigida 6 da kuma manya-manyan albarusai har 3000.

Labarin ya kara da cewa, Nigeria’s  Department of State Services (DSS), ta bada labarin cewa ta kai sumame a wani wuri a birnin Asaba na Jihar Delta inda ake fama da yanbinga masu fasa bututan mai da kuma sace mutane don karban kudaden fansa inda suka kama makaman sannan sun kama Manjo Polo a lokacinda yake kokarin fata daga kasar zuwa kasar Burtania a birnin Lagos na kudancin kasar.

Sannan makaman suna iya isa hannun mayakan Boko haran a arewa masu gabacin kasar da kuma arewa maso yammacin kasar inda ake fama da tashe-tashen hankula tun shekara ta 2009.

Kungiyoyi da dama sun bukaci a gudanar da bincike mai tsanani don tabbatar da zargin cewa kasashen waje suna da hannu a tashe tashen hankula a Najeriya da kuma wasu kasashen Afirka.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun ceto fasinjoji 99 daga hatsarin kwale-kwale a Ribas

A ranar Laraba ne jami’an sojojin ruwa na Najeriya da ke Fatakwal suka ceto fasinjoji 99 daga wani hatsarin kwale-kwale da ya rutsa da su a kogin Bukuma da ke ƙaramar hukumar Degema a Jihar Ribas.

Jirgin ruwan, wanda yake na jigilar fasinja yana kan hanyarsa ta daga Fatakwal zuwa Ƙaramar hukumar Akuku-Toru, inda ya yi karo da wani jirgin ruwa a tsakiyar kogin.

Gobara ta lalata shagunan kasuwar waya a Kwara Dalilin da ya sa aka samu fashewar abubuwa a barikin Maiduguri – Sojoji

Jami’ar yaɗa labarai na sansanin, Laftanar Kwamanda Bridget Bebia, a wata sanarwa da ta fitar a Fatakwal, ta ruwaito Kwamandan sojojin masu aikin bincike, Commodore Cajethan Aniaku, ya tabbatar da faruwar lamarin.

A cewar Aniaku, ba a samu asarar rai ba, kuma an kuɓutar da akasarin kayayyakin fasinjojin tare da ceto su daga cikin jirgin.

Rundunar sojin ruwan ta ce jami’anta da ke NSS 035 tare da tallafin jiragen ruwa huɗu sun ƙaddamar da aikin bincike mai inganci, inda suka yi nasarar ceto dukkan fasinjoji 99.

“Saboda saurin agajin da tawagar ceto ta yi, ba a sami asarar rayuka ko jikkata ba,” in ji Rundunar Sojan Ruwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Limamin Jumma’a A Nan Tehran Ya Ce Iran Tana Da Masu Tattaunawa Da Amurka Kwararru
  • ’Yan acaba sun yi wa mai fura fyaɗe Abuja
  • An kama matashi kan ‘satar’ ’yar maƙwabcinsa
  • Sojoji sun ceto fasinjoji 99 daga hatsarin kwale-kwale a Ribas
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Kamuwa Da Cutar Hawan Jini Da Hanyoyin Magance Ta
  • Dubban Mutanen Burkina Faso Sun Yi  Gangamin Nuna Goyon Bayan Shugaban Kasa Ibrahim Traore
  • Kasar Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Najeriya Wajen Yin Watsi Da Kariyar Cinikayya Da Yin Adawa Da Danniya Da Cin Zarafi
  • Kwastam Ta Kama Jirage Marasa Matuka Da Sauran Kayayyaki Da Darajarsu Ta Haura Naira Biliyan 921 A Legas
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna