Ministan harkokin jin kai da rage radadin talauci na UNOCHA, Farfesa Nentawe Goshwe, ya sanar da yunkurin hukumar na ficewa daga Nijeriya. Ya shaida hakan ne a yayin taron kara wa juna sani kan tsarin da za a dauka a Nijeriya, wanda aka gudanar a cibiyar yaki da ta’addanci ta kasa, ofishin mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro a Abuja.

A cikin wata wasika da aka yada a shafin intanet na hukumar a ranar 11 ga Afrilu, shugaban hukumar ta UNOCHA, Tom Fletcher ya ba da sanarwar yanke ayyuka sakamakon karancin kudade na kusan dala miliyan 60 a shekarar 2025.

Hukumar ta ce za ta rage ayyukanta a Nijeriya, Kamaru, Kolombiya, Eritriya, Iraki, Libya, Pakistan, Turkiyya da Zimbabwe, da nufin ba da fifikon da maida cikakken karfi a sauran wuraren da take gudanar da ayyukanta.

Kazalika, ita ma hukumar samar da abinci ta duniya (WFP) a ranar 28 ga watan Maris ta yi gargadin cewa mutane miliyan 58 na cikin hadarin rasa taimakon ceton rai a cikin ayyukan 28 na ceto da hukumar take yi sakamakon raguwar kudade a cikin manyan masu ba da agaji.

Mataimakiyar Babban Darakta na WFP, Rania Dagash-Kamara kan hadin gwiwa da kirkire-kirkire, ta ce hukumar na fuskantar raguwar kudaden tallafin da kashi 40 cikin 100 a shekarar 2025, idan aka kwatanta da na bara.

Sai dai abu mafi muni, ‘yan gudun hijira sun nuna gayar damuwa bisa halin da suke ciki. Wasu ‘yan gudun hijira a Muna, Maiduguri, da ke Jihar Borno, sun shaida cewar tsawon watanni suna fuskantar matsalolin yunwa sakamakon janye ayyukan tallafi na abinci a sansanonin ‘yan gudun hijira da ke jihar.

Shugaban sansanin Muna, Malam Abatcha Mustapha, ya ce ‘yan gudun hijira na cikin matsanancin rayuwa na yunwa kuma ba za su iya ci gaba da kasancewa ba tare da tallafin abinci ba.

“Mun samu kanmu a cikin tsaka mai wuya lokacin da suka daina kawo mana abinci, sai a ranar Sallah ne hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa (NEMA) ta kawo mana abinci. Mutanenmu suna cikin matsanancin yanayi. Muna zaman jiran umarni daga wajen gwamna domin komawa asalin gidajenmu a kananan hukumomi Dikwa da Mafa.”

Ya ce akwai ‘yan gudun hijira sama da mutane 44,000 a wannan sansanin kuma a shirye suke su koma gidajensu na asali domin ba karamar wahala suke sha a inda suke a halin yanzu ba.

Shugaban nakasassu a sansanin Abiso Kadi ya ce, “Tun daga lokacin da hukumar NEMA da sauran masu sa baki suka janye tallafin abinci na wucin gadi a wannan sansanin, rayuwa ta yi mana wuya, ba ni da aikin da zan yi a nan a matsayina na makaho, abin da na dogara da shi shi ne tallafin da hukumar NEMA ta bayar.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: yan gudun hijira

এছাড়াও পড়ুন:

Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata

Ita jigida irin ta da ba haka kawai ake sakata ba, domin shahararru kuma jarumai ne a wacan lokacin suke yin ta don haka ne take da tasiri da kuma tsada ga masu saye.

Sai dai a baya akwai jigida ta ‘yan mata akwai ta matan aure da kuma na tsofaffi, kuma a wannan lokacin babu matsala ko wani gani-gani da ake yi wa macen da aka ganta sanye da jigida saboda abu ne da aka dauka na al’ada maimakon ado ko kiran maza da wasu ke ganin matan yanzu suke yi da jigida ba.

Yanzu dai sanya jigida ga mata ya bunkasa ya fadada har cikin kashen Turai. Matan turawa kamar yadda bincike ya tabbatar kashi 60 cikin 100 suna sawa.

Sai dai a wannan zamanin da muke ciki sanya jigida ga mata ya zama abin ado ne ba domin dalilai irin na camfi da muka ambata a baya da mutanen baya suke yi ba, duk da yake ana samun kadan daga cikin matan kauyawa masu saka jigida da manufa ta camfi.

Shima dai kamar irin na da ne, wannan zamanin ana yin jigida ne da wasu duwatsu masu kyalli da kuma robobi masu sheki wadanda nauyinsu bai kai irin na zamanin baya ba.

Babban alfanun da jigida yake yi wa mata kamar yadda bincike ya tabbatar a wannan lokacin shi ne, yana kara wa mace fadin kugunta ga irin matan nan da suke da karancisa.

Maza da dama da aka zanta da su sun nuna sha’awarsu ta ganin matansu na aure suna saka jigida domin yana karamusu kyau musamman idan mace tana sanye da kayan da za su bayyanasu.

Har ilayau cikin alfanun da jigida ke da shi shi ne ta kan motsa sha’awan maza a yayin da suka ji sautinsa ko suka hango shatinsa.

Sai dai duk da wadannan tasiri, mahimanci da alfanun da jigida ke da su ba duka mata bane suke sanyawa ba, haka ma maza da dama ba su son ganin mace da jigida. Wasu mutane sun riga sun kudura cewa duk mace ko budurwar da aka ga tana sa jigida ko aka ji sautinsa a tare da ita suna daukan irin wadannan matan mazinata ne.

Sannan kuma yanzu ana jigida ta mganin mata. Masu maganin mata sun samo yadda ake jigida da garin magani a maimakon duwatsun da ake yi da shi, sai a yi da maganin a ciccura ta kamar dutse sai a huda tsakiyar asa zare duk haka za’a jera su. Mata su daurashi a kugunsu yana maganin mata.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mataimakin Gwamnan Sakkwato bai karɓi shanun tallafin layya ba — Hukumar Zakka
  • Ƴansanda Sun Fara Tsananta Ɗaukar Mataki Kan Ƴan Daba A Kano
  • An tallafa wa mata 250 da abinci da kayan sana’a a Kaduna
  • Dakarun IRGC Sun Kakkabo Jirahen Yakin HKI Wadanda Ake Sarrafasu Daga Nesa A Lardin Zanjan
  • Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran
  • Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata
  • DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci
  • Sudan Ta Zargi Janar Haftar Na Libiya Da Goyon Bayan ‘Yan Tawayen Kasarta Na Rapid Support Forces
  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai