Dole Jama’a Su Marawa Sojoji Baya Don Samun Nasara A Yaƙi Da Ƴan Ta’adda
Published: 2nd, May 2025 GMT
Wata ƙungiyar matasa mai suna “North-East Coalition Against Terrorism” ta yi maraba da Major General Abdulsalam Abubakar, sabon kwamandan yakin Operation HADIN KAI (OPHK), inda ta bayyana cewa tana fatan zaman lafiya ya dawo yankin.
A cikin wata sanarwa da Ismail Mustapha da Sakatare Danlami Bukar suka rattaba hannu, ƙungiyar ta ce Sojojin Nijeriya a ƙarƙashin babban Hafsan Soja Janar Chris Musa za su ci gaba da matsa lamba kan mayakan.
Ƙungiyar ta gargadi matasa su ƙi tayin shiga ƙungiyoyin da ba su da kyakkyawar manufa. Ta kuma bayyana cewa naɗin sabon kwamandan wani yunƙuri ne na ƙara sabbin dabarun yaƙi. “Ya daɗe yankin Arewa-Maso Gabas bai sami cikakkiyar zaman lafiya ba. Za mu ci gaba da zama a baya har sai dukkan al’umma sun goyi bayan Sojojin don shawo kan waɗanda suka jawo mana wannan rikicin,” in ji ƙungiyar North-East Coalition Against Terrorism
Ta kara da cewa; “Lokaci ya yi da za mu tattara mu goyi bayan Sojoji a ƙarƙashin Janar Chris Musa da sauran shugabannin Sojoji don dawo da zaman lafiya a yankinmu “
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Boko Haram Operation Haɗin Kai
এছাড়াও পড়ুন:
Shugabannin Duniya Za Su Gudanar Da Taron Sanya Hannun Jarin Bunƙasa Ƙudurorin Muradun Ƙarni A Sifaniya
Shirin dai zai kunshi abubuwa masu mahimmanci guda uku;
Na farko, Taron Sevilla zai taimaka wajen zaburar da shigowar tallafi zuwa ga kasashen da suka fi bukatarsa.
Na biyu, dole ne kasashe su kasance a kan kujerar tattara albarkatun cikin gida ta hanyar karfafa samar da kudaden shiga da magance rashin biyan haraji, hadin gwiwar kasa da kasa. Wannan zai samar da albarkatun da ake bukata sosai domin bayar da fifikon kashe kudade a wuraren da ke da tasiri mafi girma kamar ilimi, kiwon lafiya, ayyuka, kariya ga zamantakewa, samar da abinci, da makamashi irin na zamani.
A bangare daya kuma, akwai bukatar bankunan ci gaban kasa, da na shiyya-shiyya da kuma bankunan raya kasa-da-kasa, su hada hannu domin saka manyan jari.
Domin tallafa wa wannan shirin bayar da lamuni na wadannan bankunan, akwai bukatar a ninkawa sau uku ta yadda kasashe masu tasowa za su iya samun babban jari ba tare da an dora masu ruwa mai yawa ba.
Hakan zai bayar da damar ajiyar dukiya a asusun waje ba tare da wasu sharuda masu tsauri ba ko damar gudanar da al’amura a kasashe masu tasowa.
A ko’ina, masu bayar da tallafi dole ne su cika alkawuransu na kawo ci gaba, kuma dole ne a gyara tsarin bayar da bashi, domin akwai rashin adalci da yaudara a tsarin.
Daga karshe, dole ne taron Sevilla ya tsawatar tare da karfafa kasashe masu tasowa a tsarin kudi na duniya domin biya musu bukatunsu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp