Wata ƙungiyar matasa mai suna “North-East Coalition Against Terrorism” ta yi maraba da Major General Abdulsalam Abubakar, sabon kwamandan yakin Operation HADIN KAI (OPHK), inda ta bayyana cewa tana fatan zaman lafiya ya dawo yankin.

A cikin wata sanarwa da Ismail Mustapha da Sakatare Danlami Bukar suka rattaba hannu, ƙungiyar ta ce Sojojin Nijeriya a ƙarƙashin babban Hafsan Soja Janar Chris Musa za su ci gaba da matsa lamba kan mayakan.

Ta kuma yi kira ga al’ummar yankin su ba sabon kwamandan goyon baya.

Boko Haram Sun Kashe Masu Kamun Kifi 18 A Borno Sojoji Sun Harbe Mutane Biyu Har Lahira Da Ake Zargi Ɓarayin Mota Ne A Filato 

Ƙungiyar ta gargadi matasa su ƙi tayin shiga ƙungiyoyin da ba su da kyakkyawar manufa. Ta kuma bayyana cewa naɗin sabon kwamandan wani yunƙuri ne na ƙara sabbin dabarun yaƙi. “Ya daɗe yankin Arewa-Maso Gabas bai sami cikakkiyar zaman lafiya ba. Za mu ci gaba da zama a baya har sai dukkan al’umma sun goyi bayan Sojojin don shawo kan waɗanda suka jawo mana wannan rikicin,” in ji ƙungiyar North-East Coalition Against Terrorism

Ta kara da cewa; “Lokaci ya yi da za mu tattara mu goyi bayan Sojoji a ƙarƙashin Janar Chris Musa da sauran shugabannin Sojoji don dawo da zaman lafiya a yankinmu “

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Boko Haram Operation Haɗin Kai

এছাড়াও পড়ুন:

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Ce Kasar Oman Ce Ta Bukaci Dage Zaman Tattaunawan Iran Da Amurka

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: An dage zaman tattaunawan Iran da Amurka ne bisa shawarar kasar Oman

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya yi nuni da cewa: Ministan harkokin wajen kasar Oman ne ya sanar da sauyin lokacin zaman tattaunawan ba na kai tsaye ba tsakanin Iran da Amurka, yana mai bayanin cewa, dage shawarwarin ya zo ne bisa shawarar ministan harkokin wajen kasar, kuma za a sanar da wata sabuwar rana daga baya.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya sanar da manema labarai cewa: An canja ranar da za a gudanar da zaman shawarwarin ba na kai tsaye ba na gaba tsakanin Iran da Amurka, wanda aka shirya gudanarwa a ranar Asabar 3 ga watan Mayu a birnin Roma na kasar Italiya.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen na Iran ya yi nuni da cewa: Ministan harkokin wajen kasar Oman ne ya sanar da wannan sauyi, yana mai bayanin cewa, dage shawarwarin ya zo ne bisa shawarar ministan harkokin wajen kasar, kuma za a sanar da wata sabuwar rana daga baya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sabon Tsarin Ci Gaba Na Sin Ya Kawo Sauyi Daga Samar Da Takalma Miliyan 100 Zuwa Kera Mattarar Bayanai Ta Microchip
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Ce Kasar Oman Ce Ta Bukaci Dage Zaman Tattaunawan Iran Da Amurka
  • Ministan Tsaron Iran Ya Bayyana Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya A Matsayar Alamar Yan Ta’adda
  • Ma’aikata Sun Kauracewa Fareti, Sun Gudanar Da Taron Goyon Baya Ga Dakataccen Gwamnan Ribas
  • Dalilin da ya sa aka samu fashewar abubuwa a barikin Maiduguri – Sojoji
  • Dakarun IRGC Na JMI Sun Kaddamar Da Sabon Kwale-Kwale Mai Cilla Makamai Masu Linzami
  • Tarayyar Afirka ta dage takunkumin da ta kakabawa Gabon
  • Sabbin Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci: Nan Ba Da Jimawa Ba, ‘Yan Ta’adda Za Su Ɗanɗana Kuɗarsu – COAS
  • Saudiya Ta Yi Allawadai Da Kissan Kiyashin Da HKI Take Yi A Gaza A Gaban Kutun ICJ