Leadership News Hausa:
2025-08-02@03:40:43 GMT

Atiku Ne Rikitacce Ba Tinubu Ba

Published: 2nd, May 2025 GMT

Atiku Ne Rikitacce Ba Tinubu Ba

Sai dai kuma, idan Atiku da sauran ‘yan adawa suka ji tsoro, wanda hakan mai yiwuwa ne, kuma Tinubu ya sake cin zaven 2027, wanda shi ma zai iya yiwuwa, hakan ba zai zama saboda sauya sheka ba ne; domin kuwa tuni Atiku ya share fagen ruguza PDP, don kuwa ya nuna shi ne yake da jam’iyyar, abin da ba a cika fada ba, saboda yana jin dadin qalubalantar Tinubu.

*Damar Da Ta Kuvuce

Misali, jigo a jam’iyyar PDP, Sule Lamido a ranar Talata ya bayyana cewa; “Ya kamata shugaban qasa ya yi adalci, ya ceci ‘yan adawa daga murkushewa. Ba ni da tabbacin nawa Lamido zai biya Tinubu, saboda zaluntarsa.Wani abin mamaki shi ne, xaya daga cikin wadanda suka kafa PDP, bai san cewa wasu tsiraru daga cikin wadanda suka kafa tan sun ruguza ta ba, sannan babu wanda zai iya farfado da ita sai wasu daga cikinta.

Mafi kyawun damar da ta samu tun bayan rasa mulki shekaru 10 da suka wuce, shi ne shekarar 2023 lokacin da APC ta tsinci kanta cikin mawuyacin hali. Daidai lokacin Gwamnatin Muhammadu Buhari ta dauki mamayar da PDP ta yi a matsayin tamkar wani kisan kai. Saboda haka, Lamido ya fi kowa sanin cewa, Atiku ya saki hanya.

Mirgina Dutse Wurin Da Babu Gansa-kuka

Bayan ya tsaya takara a jam’iyyar APC ya fadi a zaven 2014, Atiku ya sake sauya sheka zuwa jam’iyyar PDP a shekarar 2017, ya kuma sake tsayawa takarar fidda gwani a 2019. A wancan lokacin PDP ta fara farfadowa daga mummunan kayen da ta sha a 2015, inda ta rasa jihohi tara daga cikin 22 da kuma kujeru 93 na majalisar dokoki ta kasa.

A tsarin zaven shugaban kasa kuwa, PDP ta sha mummunan kaye, lokacin Atiku baya nan. Sai dai, a hankali an sake gina jam’iyyar musamman da gudunmawar Gwamnan Jihar Ribas na wancan lokacin, Nyesom Wike. Har lokacin da Atiku ya dawo jam’iyyar, ba ta farfado ta koma kamar yadda take a baya ba. Rikicin da jam’iyyar APC ta samu a karkashin shugaba Buhari, da bangaren jam’iyyar kafin zaven 2023, da kuma yanayin da ake ciki a wancan lokacin ya nuna cewa; Nijeriya na cikin mawuyacin hali. Kasar ta gaji da mulkin APC.

Amma Atiku da yake shi Atiku ne, yana jin cewa ya zama dole a tabbatar da hasashen da aka yi a shekarar 1998 na cewa; wata rana zai zama shugaban kasa.Babu shakka, wannan neman shugabanci ya haifar masa da matsala tsakaninsa da Shugaban Kasa Olusegun Obasanjo a 2003; tsananin son mulkin nasa ne yasa ya fice daga PDP zuwa ACN, daga bisani kuma ya sake komawa APC. A karshe kuma, kishirwar wannan mulki ce tasa shi sake dawowa PDP.

Neman Wanda Za A Xora Wa Laifi

Ya riga ya zama tarihi, PDP ta sha kasa. Jam’iyyar da ta bugi kirji cewa, ita ce babbar jam’iyya a Afirka, wadda za ta yi mulki na tsawon shekara 60, yanzu ta kare mata, ta fada cikin rubibi, ‘ya’yanta sun koma neman mafaka da inda za su samu su huta a duk inda suka samu kansu.Ta yaya za a danganta wannan matsala da Tinubu, bayan Atiku yana nan yana kyallin goshi?

Duk da cewa, na fahimci halin da da ‘yan adawa ke ciki, amma kuma hakan ba yana nuna cewa, a rika dora wa wani laifin da ba nasa ba. Har yanzu akwai sauran shekara biyu, da za a iya yin wani abu. Yunkurin da Peter Obi ya yi na tsawon wata tara a babban zaben da ya gabata da kuma tasirin da jam’iyyar ta LP ta yi ya nuna cewa, masu kada kuri’a a lokacin zabe na da matukar tasiri wajen kawo sauyi. Wannan mai yiwuwa ne. Ba jam’iyyar da ‘yan son rai ke jagoranta ba, wadanda ba su da wani aiki sai shinshine-shinshine.

Kana iya fadan duk abin da kake so a kan Tinubu, amma tuni shi ya samu daukaka a siyasa tsawon shekaru 30 da suka wuce, domin kuwa ya iya tsayuka da kafarsa ba tare da jingina da wani ba, ya kuma kai labari tare barin kyakkyawan tarihi.

Tafi Atiku, Tafi

Idan har PDP na son yin abin arziki a nan gaba, sannan kuma Atiku ya damu da ita, to lallai ne ya gaggauta janye burinsa na sake tsayawa takara. Wannan buri dai, shi ne musabbabin rigingimun da ke faruwa a jam’iyyar; shi yasa ma PDP ta dare gida uku a jajiberin zaben da ya gabata; wannan tasa ya kasa yin wani tasiri tsawon shekaru biyu. Sannan kuma, shi ne dan takarar shugaban qasa na farko a Nijeriya da wadanda suka tsaya a matsayin mataimakansa suka sauya sheqa daga jam’iyyar. Don haka, babu wani dalili na zargin Tinubu ko nuna fushi a kan Okowa, don ya yi amfani da damar da ya samu. PDP za ta iya farfadowa ne kadai, bayan Atiku ya ja da baya, ya bar ta ta shaki iska. Amma idan ba haka ba, za a ci gaba da bata lokaci ne kawai.

Ishiekwene, shi ne Babban Edita kuma Babban Mataimakin Shugaban Kamfanin LEADERSHIP, sannan marubucin littafin ‘Writing for Media and Monetising It’.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: a jam iyyar

এছাড়াও পড়ুন:

An Yaba Da Kwazon Shugaba Bola Ahmad Tinubu

Masu ruwa da tsakin Arewa sun yaba da kwazon Tinubu, inda suka bukaci a kara karfafa gwiwar ‘yan kasa a taron Kaduna.

 

Masu ruwa da tsaki a Arewacin Najeriya sun yaba wa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa irin ci gaban da ta samu wajen cika alkawuran zabe, musamman a muhimman batutuwan da suka shafi tsaron kasa, samar da ababen more rayuwa, da sake fasalin tattalin arziki.

 

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun babban darakta na gidauniyar tunawa da Sardaunan Sakkwato Sir Ahmadu Bello, Engr. Abubakar Gambo Umar, kuma ya rabawa manema labarai a karshen taron tattaunawa na kwanaki biyu da aka gudanar a Arewa House, Kaduna.

 

Ya yaba wa gwamnatin Shugaba Tinubu saboda nuna gaskiya da kuma kyakkyawan aiki, yayin da ta bukaci ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da daidaito, adalci, da hadin gwiwar yanki.

 

Mahalarta taron sun kuma yaba da irin ci gaban da gwamnatin ta samu kan manyan ayyuka irin su bututun iskar gas na AKK, da aikin hako mai na Kolmani, da kuma ayyukan noman rani na karkara wadanda ke amfana da al’ummar Arewa kai tsaye.

 

Ya tabbatar da cewa, kawancen ’yan kasa da na gwamnati na da matukar muhimmanci wajen dorewar dimokuradiyya, da hadin kan kasa, da kuma ci gaba mai dorewa.

 

Har ila yau, ya haifar da damuwa game da matsalolin da ke addabar yara da ba sa zuwa makaranta a Arewa da kuma gaggawar karfafa sarkar darajar noma don samar da ayyukan yi da samar da abinci.

 

Daga cikin muhimman kudurori, taron ya yi kira da a samar da tsare-tsare na yau da kullum na gwamnati da ‘yan kasa, a matakin kasa da na jihohi.

 

Har ila yau, ta ba da shawarar inganta harkokin zuba jari a fannin ilimi, musamman don magance tsarin Almajirai da kuma matsalar rashin makaranta da ke addabar Arewacin Nijeriya.

 

Mahalarta taron sun bayar da shawarar kara hadin gwiwa tsakanin gwamnatocin tarayya da na jihohi, da goyon bayan kishin kasa, dabarun da suka shafi al’umma don sauye-sauyen tattalin arziki da tsaro, tare da karfafa gwiwar kungiyoyin farar hula, na gargajiya, da shugabannin addinai da su kara taka rawa wajen bayar da shawarwarin manufofin jama’a.

 

Shugaban kungiyar gwamnonin Najeriya kuma gwamnan jihar Kwara Abdulrahman Abdulrazaq ne ya wakilci shugaba Bola Tinubu a wajen taron.

 

Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya wakilci Dakta Aliyu Modibbo Umar, mai ba da shawara na musamman kan ayyuka na musamman, yayin da gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya kasance babban mai masaukin baki.

 

Gwamnan jihar Gombe kuma shugaban kungiyar gwamnonin jihohin Arewa, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya halarta a matsayin babban bako na musamman.

 

Manyan jami’an gwamnatin tarayya sun hada da Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), Sanata George Akume, wanda ya jagoranci tawagar. Sauran manyan wadanda suka halarci taron sun hada da mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, mambobin majalisar ministocin tarayya, shugabannin hukumomin tsaro, da manyan jami’an tsaro daga Arewacin Najeriya.

 

A jawabin da ya gabatar, Farfesa Tijjani Mohammed Bande, ya bayyana yadda Najeriya ke da karfin gwiwa a cikin kalubale kamar rashin tsaro, talauci, da gibin ilimi.

 

Ya bukaci shugabannin Arewa da su tabbatar da muradun su a cikin tsarin kasa ta hanyar daidaitawa da ingantattun manufofin ci gaba masu amfani ga gamayya.

 

Babban zaman taron ya tattauna batutuwan da suka shafi kasa baki daya da suka hada da tsaro, shugabanci, farfado da tattalin arziki, noma, samar da ababen more rayuwa, da ci gaban bil Adama.

 

Adamu Yusuf

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa
  • PDP ta mutu murus a Kano — Shugaban NNPP
  • Tinubu Ya Cika Alƙawurran Da Ya Ɗauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa
  • Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin
  • Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
  • 2027: Ba Mu Kafa Haɗakarmu Don Cika Burin Atiku Ba – ADC
  • An Yaba Da Kwazon Shugaba Bola Ahmad Tinubu
  • Wasu ’yan siyasa na sukar Tinubu saboda ɗan Kudu ne — Onanuga
  • Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina