Leadership News Hausa:
2025-06-17@05:50:02 GMT

Atiku Ne Rikitacce Ba Tinubu Ba

Published: 2nd, May 2025 GMT

Atiku Ne Rikitacce Ba Tinubu Ba

Sai dai kuma, idan Atiku da sauran ‘yan adawa suka ji tsoro, wanda hakan mai yiwuwa ne, kuma Tinubu ya sake cin zaven 2027, wanda shi ma zai iya yiwuwa, hakan ba zai zama saboda sauya sheka ba ne; domin kuwa tuni Atiku ya share fagen ruguza PDP, don kuwa ya nuna shi ne yake da jam’iyyar, abin da ba a cika fada ba, saboda yana jin dadin qalubalantar Tinubu.

*Damar Da Ta Kuvuce

Misali, jigo a jam’iyyar PDP, Sule Lamido a ranar Talata ya bayyana cewa; “Ya kamata shugaban qasa ya yi adalci, ya ceci ‘yan adawa daga murkushewa. Ba ni da tabbacin nawa Lamido zai biya Tinubu, saboda zaluntarsa.Wani abin mamaki shi ne, xaya daga cikin wadanda suka kafa PDP, bai san cewa wasu tsiraru daga cikin wadanda suka kafa tan sun ruguza ta ba, sannan babu wanda zai iya farfado da ita sai wasu daga cikinta.

Mafi kyawun damar da ta samu tun bayan rasa mulki shekaru 10 da suka wuce, shi ne shekarar 2023 lokacin da APC ta tsinci kanta cikin mawuyacin hali. Daidai lokacin Gwamnatin Muhammadu Buhari ta dauki mamayar da PDP ta yi a matsayin tamkar wani kisan kai. Saboda haka, Lamido ya fi kowa sanin cewa, Atiku ya saki hanya.

Mirgina Dutse Wurin Da Babu Gansa-kuka

Bayan ya tsaya takara a jam’iyyar APC ya fadi a zaven 2014, Atiku ya sake sauya sheka zuwa jam’iyyar PDP a shekarar 2017, ya kuma sake tsayawa takarar fidda gwani a 2019. A wancan lokacin PDP ta fara farfadowa daga mummunan kayen da ta sha a 2015, inda ta rasa jihohi tara daga cikin 22 da kuma kujeru 93 na majalisar dokoki ta kasa.

A tsarin zaven shugaban kasa kuwa, PDP ta sha mummunan kaye, lokacin Atiku baya nan. Sai dai, a hankali an sake gina jam’iyyar musamman da gudunmawar Gwamnan Jihar Ribas na wancan lokacin, Nyesom Wike. Har lokacin da Atiku ya dawo jam’iyyar, ba ta farfado ta koma kamar yadda take a baya ba. Rikicin da jam’iyyar APC ta samu a karkashin shugaba Buhari, da bangaren jam’iyyar kafin zaven 2023, da kuma yanayin da ake ciki a wancan lokacin ya nuna cewa; Nijeriya na cikin mawuyacin hali. Kasar ta gaji da mulkin APC.

Amma Atiku da yake shi Atiku ne, yana jin cewa ya zama dole a tabbatar da hasashen da aka yi a shekarar 1998 na cewa; wata rana zai zama shugaban kasa.Babu shakka, wannan neman shugabanci ya haifar masa da matsala tsakaninsa da Shugaban Kasa Olusegun Obasanjo a 2003; tsananin son mulkin nasa ne yasa ya fice daga PDP zuwa ACN, daga bisani kuma ya sake komawa APC. A karshe kuma, kishirwar wannan mulki ce tasa shi sake dawowa PDP.

Neman Wanda Za A Xora Wa Laifi

Ya riga ya zama tarihi, PDP ta sha kasa. Jam’iyyar da ta bugi kirji cewa, ita ce babbar jam’iyya a Afirka, wadda za ta yi mulki na tsawon shekara 60, yanzu ta kare mata, ta fada cikin rubibi, ‘ya’yanta sun koma neman mafaka da inda za su samu su huta a duk inda suka samu kansu.Ta yaya za a danganta wannan matsala da Tinubu, bayan Atiku yana nan yana kyallin goshi?

Duk da cewa, na fahimci halin da da ‘yan adawa ke ciki, amma kuma hakan ba yana nuna cewa, a rika dora wa wani laifin da ba nasa ba. Har yanzu akwai sauran shekara biyu, da za a iya yin wani abu. Yunkurin da Peter Obi ya yi na tsawon wata tara a babban zaben da ya gabata da kuma tasirin da jam’iyyar ta LP ta yi ya nuna cewa, masu kada kuri’a a lokacin zabe na da matukar tasiri wajen kawo sauyi. Wannan mai yiwuwa ne. Ba jam’iyyar da ‘yan son rai ke jagoranta ba, wadanda ba su da wani aiki sai shinshine-shinshine.

Kana iya fadan duk abin da kake so a kan Tinubu, amma tuni shi ya samu daukaka a siyasa tsawon shekaru 30 da suka wuce, domin kuwa ya iya tsayuka da kafarsa ba tare da jingina da wani ba, ya kuma kai labari tare barin kyakkyawan tarihi.

Tafi Atiku, Tafi

Idan har PDP na son yin abin arziki a nan gaba, sannan kuma Atiku ya damu da ita, to lallai ne ya gaggauta janye burinsa na sake tsayawa takara. Wannan buri dai, shi ne musabbabin rigingimun da ke faruwa a jam’iyyar; shi yasa ma PDP ta dare gida uku a jajiberin zaben da ya gabata; wannan tasa ya kasa yin wani tasiri tsawon shekaru biyu. Sannan kuma, shi ne dan takarar shugaban qasa na farko a Nijeriya da wadanda suka tsaya a matsayin mataimakansa suka sauya sheqa daga jam’iyyar. Don haka, babu wani dalili na zargin Tinubu ko nuna fushi a kan Okowa, don ya yi amfani da damar da ya samu. PDP za ta iya farfadowa ne kadai, bayan Atiku ya ja da baya, ya bar ta ta shaki iska. Amma idan ba haka ba, za a ci gaba da bata lokaci ne kawai.

Ishiekwene, shi ne Babban Edita kuma Babban Mataimakin Shugaban Kamfanin LEADERSHIP, sannan marubucin littafin ‘Writing for Media and Monetising It’.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: a jam iyyar

এছাড়াও পড়ুন:

Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Kakkabo Jiragen Yakin Isra’ila Biyu Kirar F-35

Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta zama kasa ta farko a duniya da ta harbo jiragen saman yaki kirar F-35

Iran ta zama kasa ta farko a duniya da ta yi nasarar harbo jiragen yaki kirar F-35, bayan da ta yi nasarar auna wasu jiragen saman yakin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila kirar F-35 guda biyu, kuma ta barar da su kasa.

Gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta yi amfani da wadannan jirage masu tsananin ci gaban zamani wajen kai hare-haren wuce gona gona da iri kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran da safiyar ranar Juma’a, wanda hare-haren suka yi sanadiyyar shahadar wasu manyan jami’an sojan Iran da masana kimiyyar nukiliya da fararen hula da suka hada da mata da kananan yara.

Ma’aikatar hulda da jama’a ta rundunar sojojin Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta sanar a cikin wata sanarwa da ta fitar cewa: Dakarun tsaron saman Iran sun harbo jiragen saman yaki kirar F-35 guda biyu, baya ga wasu jiragen saman yakin yahudawan sahayoniyya marasa matuka ciki.

Sanarwar ta nuna cewa: Jami’an tsaron Iran sun kame daya daga cikin matukan jiragen wacce mace ce, kuma ana kan bincike domin sanin makomar matukin daya jirgin.

Abin lura shi ne cewa: Jiragen yakin kirar F-35 da ‘yan sahayoniyya ke amfani da su na daga cikin wadanda suka ci gaba a duniya kuma ake gwada su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta kasa ɗaukar matakin da ya dace a kan kashe-kashen Benuwe — Atiku
  • Tinubu ya bayar da umarnin binciken hare-haren Benuwe
  • Tinubu ya bayar umarnin binciken hare-haren Benuwe
  • KADSEMA da IOM sun fara tantance ɓarnar da ambaliya ta yi a Kaduna
  • APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu
  • Takarar Tinubu: Rikici ya ɓarke a APC bayan Ganduje ya ƙi goyon bayan Shettima
  • Abokin Takarar Tinubu: Rikici ya ɓarke a APC bayan Ganduje ya ƙi goyon bayan Shettima
  • Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila
  • Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa
  • Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Kakkabo Jiragen Yakin Isra’ila Biyu Kirar F-35