Ana barazanar korar sojojin Isra’ila da ke neman a kawo ƙarshen yaƙin Gaza
Published: 16th, April 2025 GMT
Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu ya yi barazanar korar sojojin da ke neman kawo karshen yakin Gaza bayan sun rattaba hannu kan wasu takardu da ke nuna bukatar hakan.
A bayan nan dai fiye da sojoji 1,500 na rundunar da ke kula da tankokin yaƙi ta Isra’ila, ciki har da janar-janar, suka sanya hannu kan wata takardar neman gwamnatin Isra’ila ta mayar da hankali kan dawo da waɗanda aka yi garkuwa da su a Gaza, ko da hakan zai kai ga dakatar da yaƙin da ake yi a yankin Falasdinawa.
A cewar Jaridar Maariv a ranar Litinin, sojoji 1,525 daga rundunar tankokin sun sanya hannu kan wannan takardar, daga masu ɗauke bindiga har zuwa janar-janar.
Sun bukaci gwamnati “ta yi duk mai yiwuwa don tabbatar da an sako wadanda aka yi garkuwa da su — ko da hakan zai kai ga dakatar da yakin.”
Waɗanda suka sanya hannun sun hada da sojojin da suka yi aiki a rundunar kula da tankoki sannan suka koma rayuwar farar hula ba tare da zuwa makarantar jami’ai ba da tsofaffin sojoji da ƙananan kwamandoji, da kuma tsofaffin manyan jami’an sojin Isra’ila, ciki har da tsoffin shugabannin rundunar tankoki da kwamandojin sassa, kamar yadda Maariv ta bayyana.
Sunayen masu sanya hannu sun hada da tsohon Firaminista kuma tsohon shugaban sojoji Ehud Barak da tsohon shugaban rundunar tsakiya Amram Mitzna da tsohon shugaban hafsoshin tsaro Dan Halutz da tsohon shugaban leƙen asiri na soja Amos Malka da tsohon shugaban rundunar tsakiya Avi Mizrahi, da kuma tsohon kwamandan rundunar tankoki ta 14 Amnon Reshef.
Wannan takardar buƙatar ta kasance wani bangare na wani babban kira daga sojoji na yanzu da tsoffin sojojin Isra’ila da ke neman a dawo da wadanda aka yi garkuwa da su tare da kawo karshen yakin.
Tun daga ranar Alhamis, an fitar da kusan takardu goma daga sojoji da ke neman a kawo karshen yakin Gaza.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Benjamin Netanyahu Falasɗinawa Isra ila sanya hannu
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
Bug da kari Tinubu ya jinjina wa Shugaban jami’ar, Farfesa Wahab Olasupo Egbewole (SAN)da ‘yan tawagarsa wajen maida hankalin da suka yi na bunkasa Jami’ar da kumna kudurinta na muradun ci gaban da ake bukata.
Shi ma anashi jawabin Shugaban Jami’ar Sarkin Katsina, Alhaji. Abdulmumin Kabir Usman, wanda Wazirin Katsina, Sanata Ibrahim Idah ya wakilta, ya nuna jin dadinsa kan irin kokarin da UNILORIN saboda bunkasar ilimi da kumasamar wuraren koyon kaaratu masu kyau da kuma suka dace.
Ya yi ma kallon ayyukan da ak kaddamar a matsayin“ irin abubuwan da ake bukatar gani ke nan”da za su taimakawa lamarin koyarwa, koyo,da kuma bincike, inda ya kara da cewa yadda Jami’ar ta maida hankalinta wajen bunkasa dabarar koyon yin abubuwa zai taimakawa dalibai su tashi da sun koyi abubuwan da zasu yi baya rayuwar da suka yi cikin aji.
A nashi jawabin mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa. Egbewole ya nuna farin cikinsa da godew a Shugaban kasa Tinubu kan yadda ya amince da gaiyar da Jami’ar ta yi ma shi, da kuma taimaka mata wajen tafiyar da bunkasar abubuwan jin dadi.
“Muna nan muna sa ido saboda ci gaban samun abubwan da suke taimakawa ci gaba kwarai da gaske a kowace rana kamar yadda yace yana da amincewa da yardarm ci gaba da samun hakan’’.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA