Aminiya:
2025-05-21@20:35:54 GMT

Ana barazanar korar sojojin Isra’ila da ke neman a kawo ƙarshen yaƙin Gaza

Published: 16th, April 2025 GMT

Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu ya yi barazanar korar sojojin da ke neman kawo karshen yakin Gaza bayan sun rattaba hannu kan wasu takardu da ke nuna bukatar hakan.

A bayan nan dai fiye da sojoji 1,500 na rundunar da ke kula da tankokin yaƙi ta Isra’ila, ciki har da janar-janar, suka sanya hannu kan wata takardar neman gwamnatin Isra’ila ta mayar da hankali kan dawo da waɗanda aka yi garkuwa da su a Gaza, ko da hakan zai kai ga dakatar da yaƙin da ake yi a yankin Falasdinawa.

Budurwar da ke rayuwa a banɗaki don gudun biyan kuɗin hayar gida HOTUNA: Zulum ya karɓi baƙuncin Majalisar Sarakunan Arewa a Borno

A cewar Jaridar Maariv a ranar Litinin, sojoji 1,525 daga rundunar tankokin sun sanya hannu kan wannan takardar, daga masu ɗauke bindiga har zuwa janar-janar.

Sun bukaci gwamnati “ta yi duk mai yiwuwa don tabbatar da an sako wadanda aka yi garkuwa da su — ko da hakan zai kai ga dakatar da yakin.”

Waɗanda suka sanya hannun sun hada da sojojin da suka yi aiki a rundunar kula da tankoki sannan suka koma rayuwar farar hula ba tare da zuwa makarantar jami’ai ba da tsofaffin sojoji da ƙananan kwamandoji, da kuma tsofaffin manyan jami’an sojin Isra’ila, ciki har da tsoffin shugabannin rundunar tankoki da kwamandojin sassa, kamar yadda Maariv ta bayyana.

Sunayen masu sanya hannu sun hada da tsohon Firaminista kuma tsohon shugaban sojoji Ehud Barak da tsohon shugaban rundunar tsakiya Amram Mitzna da tsohon shugaban hafsoshin tsaro Dan Halutz da tsohon shugaban leƙen asiri na soja Amos Malka da tsohon shugaban rundunar tsakiya Avi Mizrahi, da kuma tsohon kwamandan rundunar tankoki ta 14 Amnon Reshef.

Wannan takardar buƙatar ta kasance wani bangare na wani babban kira daga sojoji na yanzu da tsoffin sojojin Isra’ila da ke neman a dawo da wadanda aka yi garkuwa da su tare da kawo karshen yakin.

Tun daga ranar Alhamis, an fitar da kusan takardu goma daga sojoji da ke neman a kawo karshen yakin Gaza.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Benjamin Netanyahu Falasɗinawa Isra ila sanya hannu

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Sudan Sun Gama Tsarkaka Birnin Khartoum Daga ‘Yan Tawayen Rapid Support Forces

Sojojin Sudan sun karbe iko da sansanin dakarun kai daukin gaggawa na karshe a birnin Khartoum fadar mulkin kasar

Sojojin Sudan sun ci gaba da dama a jihohin Kordofan da Darfur, inda suka bar birnin Nahud da ke yammacin Kordofan, wanda sojojin suka killace birnin ta kowane bangare.

Sojojin Sudan sun samu nasarar karbe ikon yankin Atrun mai mahimmanci a Arewacin Darfur, tare da bude hanyar shiga sauran garuruwan Darfur gaba daya.

Bayan kazamin fada tsakanin sojojin Sudan da dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces a yankin Al-Saliha da ke kudancin Omdurman, wanda ya dauki tsawon sama da wata guda ana gwabzawa, sojojin sun samu nasarar mamaye yankin gaba daya, sai dai wasu kananan yankuna da sojojin ke hadawa, a cewar kakakin rundunar sojin Sudan.

Rundunar kungiyar Rapid Support Forces ta dakaraun kai daukin gaggawa ta mayar da martani ta hanyar kai hari a wani ma’ajiyar makamai a tsakiyar Omdurman tare da wani jirgin sama maras matuki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji da ’yan siyasa na taimaka wa Boko Haram da bayanai — Zulum
  • Sojojin Sudan Sun Gama Tsarkaka Birnin Khartoum Daga ‘Yan Tawayen Rapid Support Forces
  • Sojojin Sudan Sun Sanar Da Kammala “Tsarkake” Birnin Kahartum Daga Dakarun  RSF
  •  Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kashe Falasdinawa ‘Yan Gudun Hijira A Lokacin Da Suke Bacci
  • Zulum zai saya wa sojoji da ’yan sa-kai ƙarin motoci don yaƙar Boko Haram
  • Hare-Haren Wuce Gona Da Irin Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Janyo Shahadan Falasdinawa Masu Yawa
  • ‘Yan Gwagwarmayar Falasdinawa Sun Halaka Sojojin Sahayoniyya Tare Da Jikkata Wasu A Beit Lahiya
  • Wasu Shugabannin Turai Sun Yi Barazanar Ladabtar Da Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Yeman ta yi barazanar killace tashar jiragen ruwan Haifa ta Isra’ila
  • Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto