Falasdinawa 80,000 ne suka halarci sallar Juma’a a mako na uku na Ramadan a masallacin Al-Aqsa
Published: 22nd, March 2025 GMT
An gudanar da Sallar Juma’a a mako na uku na watan Ramadan a Masallacin Al-Aqsa, duk kuwa da tsauraran takunkumin da gwamnatin yahudawan sahyoniya ta dauka, tare da halartar Palasdinawa 80,000.
Kamfanin dillancin labaran Al-Naba y bayar da rahoton cewa, dubun dubatar Falasdinawa ne suka gudanar da sallar Juma’a ta uku na watan Ramadan a masallacin Al-Aqsa, duk da matakai na kawo cikas da sojojin mamaya na Haramtacciyar Kasar Isra’ila suka dauka da kuma yanayin sanyi da ruwan sama a birnin Kudus.
Hukumar kula da lamurran addinin Musulunci a birnin Kudus ta bayar da bayanin cewa, masallata 80,000 ne suka gudanar da sallar Juma’a ta uku na watan Ramadan a masallacin Al-Aqsa.
Sheikh Khalid Abu Juma, limamin masallacin Al-Aqsa, ya ce a cikin hudubar sallar: “Watan Ramadan yana kawo azama da azama a cikinmu; Musulmai sun bar al’adun da suka saba a cikin saurin watanni; Suna nisantar da kansu daga al’adun da suka saba, tare da karfafa ayyukan tsarkeke ruhi da kusanci ga Allah.
Abu Juma ya jaddada cewa azumi yana karfafa nufi da kuma inganta azama, ya kara da cewa: Imani da azama suna da alaka da ruhi.
Ya ce: Yunkurin da makiya suke yi na rusa zaman lafiya da kwanciyar hankali ya sabawa koyarwar addinin muslunci da dukkanin addinai da aka saukar daga sama.
Sannan kuma ya yi ishara da abin da ke faruwa a Gaza, yana bayyana shi a matsayin aiwatar da wani mummunan kudiri na makiya a kan al’ummar musulmi na Gaza da ma Falastinu baki daya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Ramadan a masallacin Al Aqsa sallar Juma a
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
Sojojin Najeriya sun kashe aƙalla mayakan ƙungiyar ISWAP 8, ciki har da manyan kwamandojinta biyu a Jihar Borno.
Wata majiyar leƙen asiri daga rundunar haɗin kai ta OPHK ta bayyana cewa an kashe ’yan ta’addan ne a wata arangama da suka yi da sojojin a kan hanyar Maiduguri zuwa Baga a safiyar ranar Litinin.
DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabalaA cewar majiyoyin, an yi arangamar ce a kusa da Garin Giwa da ke gab da ƙauyen Kauwa, lokacin da ’yan ta’addan suka yi wa dakarun da ke sintiri kwanton ɓauna.
“A yayin wannan artabu, an kashe ’yan ta’adda takwas, ciki har da Munzirs biyu (kwamandojin filin daga na ƙungiyar) da kuma Qaid ɗaya (shugaban sashe).
“An kashe Modu Dogo, Munzir daga Dogon Chukun, wani Munzir da ba a bayyana ba, da Abu Aisha, shugaban sashe (Qaid) daga Tumbun Mota,” in ji wata majiya.
Majiyar ta ƙara da cewa wasu mayaƙa da dama sun samu raunuka, musamman waɗanda suka tsere da ƙafa bayan sun yi watsi da babura 14 da sojojin suka ƙwato.