Aminiya:
2025-08-01@08:05:23 GMT

’Yan daba sun hallaka matashi ana sallar Tahajjud a Kaduna

Published: 22nd, March 2025 GMT

Wasu da ake kyautata zaton ’yan daba ne sun kai hari wani masallaci da ke yankin Rigasa a Jihar Kaduna, inda suka kashe wani matashi yayin da ake tsaka da sallar Tahajjud.

Sai dai rundunar ’yan sandan jihar, sun kama mutum 12 da ake zargi da hannu a kai hari masallacin.

Mace ta farko ta zama shugabar ƙasar Namibia An wawushe motar abinci ta Hukumar WFP a Borno

Kakakin rundunar, Mansir Hassan, ya ce ’yan daban sun fito daga unguwanni daban-daban kamar Malalin Gabas, Tudun Wada, Rafin Guza, da Unguwar Baduko.

Sun kai farmaki Masallacin Layin Bilya, titin Makwa a Rigasa da misalin ƙarfe 2 na dare yayin da masu mutane ke sallar Tahajjud.

Kafin jami’an tsaro su isa wajen, sun sun daɓa wa wani matashi mai shekara 28, Usman Mohammed, wuƙa har lahira.

Rundunar tare da haɗin gwiwar JTF sun ɗauki mataki cikin gaggawa, inda suka kama mutum 12 kuma ana bincike a kansu.

Haka kuma, an samu makamai a hannu waɗanda aka kama.

An fara bincike domin gano gaskiyar lamarin da tabbatar da cewa an hukunta waɗanda suka aikata laifin.

Sakamakon haka, ’yan sanda sun ƙara tsaurara matakan tsaro a wuraren ibada da sauran wuraren da ake ganin za su iya fuskantar barazana.

Hukumomi sun buƙaci al’umma da su kasance masu sanya ido tare da gaggauta kai rahoto idan sun ga wani abun zargi.

’Yan sanda sun kuma gargaɗi masu aikata laifi da su daina ko su fuskanci hukunci mai tsanani.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hari Sallar Tahajjud Tudun Wada

এছাড়াও পড়ুন:

INEC Ta Gudanar da Taron Masu Ruwa da Tsaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi na Babura/Garki

A wani ɓangare na shirin gudanar da zaɓen cike gurbi na Babura/Garki a Majalisar Tarayya, Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) reshen Babura ta shirya muhimmin taron masu ruwa da tsaki domin tabbatar da sahihin zaɓe mai inganci da haɗin kai.

 

A jawabinsa yayin taron, jami’in zaɓe na ƙaramar hukumar Babura, Malam Hafiz Khalid, ya gabatar da cikakken jadawalin ayyukan zaɓen.

Ya jaddada muhimmancin haɗin kai da gaskiya a kowane mataki, yana mai bayyana zaɓen a matsayin aikin gama gari da ke buƙatar goyon bayan duk masu ruwa da tsaki.

 

Mahalarta taron sun bayar da shawarwari masu amfani tare da gabatar da muhimman tambayoyi da suka shafi inganta sahihanci da nasarar zaɓen.

 

Wasu daga cikin batutuwan da aka tattauna sun haɗa da shirye-shiryen kayayyakin aiki, tsaro, wayar da kan masu zaɓe, da sauransu.

An kammala taron da sabunta ƙudurorin haɗin guiwa daga dukkan mahalarta, wajen tabbatar da gudanar da zaɓen cike gurbi cikin lumana, ‘yanci, adalci, da sahihanci a yankin Babura/Garki.

 

Wakilin Rediyon Najeriya  ya bayyana cewa, taron da aka gudanar a ofishin INEC na Babura, ya samu halartar masu ruwa da tsaki da suka haɗa da Hakimin Babura, jami’an tsaro, wakilan jam’iyyun siyasa, jami’ai daga Ƙungiyar Direbobin Ƙasa (NURTW), Ƙungiyar Masu Motocin Haya (NARTO), ƙungiyoyin farar hula (CBOs), da sauran jami’an INEC.

 

Usman Muhammad Zaria

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • INEC Ta Gudanar da Taron Masu Ruwa da Tsaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi na Babura/Garki
  • Kwara Ta Kwashe Mabarata Daga Titunan Jihar Su 94
  • Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Kwamandan NDA Ya Bukaci Dalibai Su Dage da Karatu a Taron FGC Malali
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • ’Yan bindiga sun tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina
  • Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu
  • ‘Yan Sanda A Kano Sun Kama Kasurgumin Dan Fashin Nan Barga Da Wasu Mutum 14
  • Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata