’Yan daba sun hallaka matashi ana sallar Tahajjud a Kaduna
Published: 22nd, March 2025 GMT
Wasu da ake kyautata zaton ’yan daba ne sun kai hari wani masallaci da ke yankin Rigasa a Jihar Kaduna, inda suka kashe wani matashi yayin da ake tsaka da sallar Tahajjud.
Sai dai rundunar ’yan sandan jihar, sun kama mutum 12 da ake zargi da hannu a kai hari masallacin.
Mace ta farko ta zama shugabar ƙasar Namibia An wawushe motar abinci ta Hukumar WFP a BornoKakakin rundunar, Mansir Hassan, ya ce ’yan daban sun fito daga unguwanni daban-daban kamar Malalin Gabas, Tudun Wada, Rafin Guza, da Unguwar Baduko.
Sun kai farmaki Masallacin Layin Bilya, titin Makwa a Rigasa da misalin ƙarfe 2 na dare yayin da masu mutane ke sallar Tahajjud.
Kafin jami’an tsaro su isa wajen, sun sun daɓa wa wani matashi mai shekara 28, Usman Mohammed, wuƙa har lahira.
Rundunar tare da haɗin gwiwar JTF sun ɗauki mataki cikin gaggawa, inda suka kama mutum 12 kuma ana bincike a kansu.
Haka kuma, an samu makamai a hannu waɗanda aka kama.
An fara bincike domin gano gaskiyar lamarin da tabbatar da cewa an hukunta waɗanda suka aikata laifin.
Sakamakon haka, ’yan sanda sun ƙara tsaurara matakan tsaro a wuraren ibada da sauran wuraren da ake ganin za su iya fuskantar barazana.
Hukumomi sun buƙaci al’umma da su kasance masu sanya ido tare da gaggauta kai rahoto idan sun ga wani abun zargi.
’Yan sanda sun kuma gargaɗi masu aikata laifi da su daina ko su fuskanci hukunci mai tsanani.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: hari Sallar Tahajjud Tudun Wada
এছাড়াও পড়ুন:
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
Ban da haka, shugaban na Sin ya ce, kasarsa na son yin kokari tare da bangarori daban daban, wajen aiwatar da ra’ayin raya kasa na kirkiro sabbin fasahohi, da tabbatar da daidaito, da kare muhalli, da bude kofa, gami da haifar da alfanu ga kowa, ta yadda za a kafa wata al’ummar bai daya ta yankin Asiya da na tekun Pasifik.
Duk a wajen taron, yayin wani bikin mika damar karbar bakuncin taron kungiyar APEC, shugaba Xi Jinping ya sanar da cewa, kasar Sin za ta karbi bakuncin kwarya-kwaryar taron shugabannin kungiyar APEC karo na 33, wanda ake sa ran gudanar da shi a birnin Shenzhen na kasar Sin a watan Nuwamba na shekarar 2026. (Bello Wang)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA