Hukumar gudanarwar asibitin koyarwa na Aminu Kano ta ce ana kokarin ganin an dawo da ayyukan da masana’antar iskar Oxygen da asibitin ke yi.

 

A cewar Mataimakin Daraktan sashen (Biomedical/ kuma Shugaban Kwamitin Kula da Oxygen), Engr Ahmed Usman a madadin Hukumar, an sanya hannu kan wata yarjejeniya ta fahimtar juna tsakanin asibitin da Dodams Medical Equipt don kula da aikin na tsawon shekaru 2.

 

Ya bayyana cewa, a watan Janairun wannan shekara ne aka yi duk wani shiri da kuma biyan kudin jirgi, amma saboda hutun karshen shekara da Kamfanoni suka yi, an samu tsaiko wajen samar da wasu sassa musamman na’urar gudanarda aikin, wanda ya iso a ranar Litinin 10 ga Maris, 2025.

 

Ya ci gaba da cewa, tuni aka fara yi wa na’urar samar da iskar Oxygen aiki kamar yadda ya faru a jiya, wanda ya rage kawai na’urar kwampreso da kuma Oxygen buster, wadanda ke kan aiki.

 

A halin da ake ciki, a cikin wannan lokacin jirar Hukumar Kula da Asibitin ta fitar da iskar Oxygen a wani wuri musamman daga Kamfanin Loquat, kamar yadda ake yi a wasu asibitoci.

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Yajin aiki: Jami’ar KASU ta shiga rudani

Jami’ar Jihar Kaduna (KASU) ta shiga rudani a ranar Alhamis bayan da aka samu rahotanni masu karo da juna game da matsayin yajin aikin da reshenta na Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) ke yi.

Shugaban Jami’ar, Farfesa Abdullahi Ibrahim Musa, ya gudanar da taron manema labarai inda ya sanar da cewa ASUU-KASU ta dakatar da yajin aikin nata, kuma za a ci gaba da karatun nan take.

Ya danganta matakin janye yajin aikin da shiga tsakani da Gwamna Uba Sani ya yi, wanda ya amince da biyan Naira miliyan 50 miliyan don walwalar ma’aikata, tare da fitar da N146 miliyan don biyan wasu albashin da aka rike da kuma alawus-alawus na shirin koyon makamar aiki na dalibai (SIWES).

Farfesa Musa ya yaba wa wadannan matakan a matsayin “jaruntaka da ba a taba gani ba,” kuma ya jinjinawa gwamnan saboda “halinsa na ban mamaki game da halin da dalibai ke ciki, yanayin ilimi, da walwalar ma’aikatan ilimi da wadanda ba na ilimi ba.”

Layya: Farashin raguna na iya tashin gwauron zabo Ɗaukar fansa: Sojoji sun ragargaji Boko Haram a Dajin Sambisa

Ya kuma bayyana cewa an kafa kwamitin sasantawa karkashin jagorancin Mataimakiyar Gwamna Dokta Hadiza Balarabe, don tattaunawa da dukkan kungiyoyin jami’ar domin warware matsalolin da suka dade suna ci mata tuwo a kwarya.

Sai dai jim kadan kuma, ckin kakkausan harshe, ASUU-KASU ta musanta sanarwar Shugaban Jami’ar, inda ta bayyana ta a matsayin katsalandan kuma kuma mara izini.

A cikin wata sanarwa da Mukaddashin Shugaban kungiyar Kwamared Abubakar Abdullahi da Sakatare Kwamared Peter M. Waziri suka sanya wa hannu, kungiyar ta shawarci jama’a da su yi watsi da ikirarin da hukumar gudanarwar jami’ar ta yi.

Kungiyar ta bayyana cewa, “Ba hukumar gudanarwar Jami’ar ce ta kaddamar da yajin aikin ba, don haka ba ta da ikon dakatar da shi.”

Kungiyar ta nanata cewa har yanzu tana jiran shawarar Majalisar Zartarwarta ta Kasa (NEC) bayan taron majalisar da aka gudanar a ranar 15 ga Mayu, 2025.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunana
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunato
  • Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Ginin Babban Asibitin Anka Da Aka Inganta
  • Jami’ar FUDMA Ta Ƙara Fadawa Cikin Rikicin Shuagabanci A Katsina
  • Jami’ar FUDAMA Ta Ƙara Fadawa Cikin Rikicin Shuagabanci A Katsina
  • Mutum 3 Sun Rasu, Wasu Sun Jikkata Yayin Da Bama-bamai Suka Tashi A Hanyar Borno
  • Yajin aiki: Jami’ar KASU ta shiga rudani
  • Dalilin Tsame Daya Cikin Uku Na Ma’aikatan Ƙasar Nan A Tsarin Sauye-sauyen Biyan Haraji – Czar
  • Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci
  • Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025