Hukumar gudanarwar asibitin koyarwa na Aminu Kano ta ce ana kokarin ganin an dawo da ayyukan da masana’antar iskar Oxygen da asibitin ke yi.

 

A cewar Mataimakin Daraktan sashen (Biomedical/ kuma Shugaban Kwamitin Kula da Oxygen), Engr Ahmed Usman a madadin Hukumar, an sanya hannu kan wata yarjejeniya ta fahimtar juna tsakanin asibitin da Dodams Medical Equipt don kula da aikin na tsawon shekaru 2.

 

Ya bayyana cewa, a watan Janairun wannan shekara ne aka yi duk wani shiri da kuma biyan kudin jirgi, amma saboda hutun karshen shekara da Kamfanoni suka yi, an samu tsaiko wajen samar da wasu sassa musamman na’urar gudanarda aikin, wanda ya iso a ranar Litinin 10 ga Maris, 2025.

 

Ya ci gaba da cewa, tuni aka fara yi wa na’urar samar da iskar Oxygen aiki kamar yadda ya faru a jiya, wanda ya rage kawai na’urar kwampreso da kuma Oxygen buster, wadanda ke kan aiki.

 

A halin da ake ciki, a cikin wannan lokacin jirar Hukumar Kula da Asibitin ta fitar da iskar Oxygen a wani wuri musamman daga Kamfanin Loquat, kamar yadda ake yi a wasu asibitoci.

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Bincike ya nuna ’yan Najeriya ba su gamsu da gwamnatin Tinubu ba

Wani bincike da Cibiyar Bincike ta Africa Polling Institute (API), ta gudanar ya nuna cewa yawancin ’yan Najeriya ba su da ƙwarin gwiwa game da Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, Majalisar Dokoki da kuma ɓangaren shari’a.

An bayyana sakamakon Binciken Haɗin Kan Al’ummar Najeriya na 2025, a wani taron ƙasa da aka gudanar a Abuja.

Elon Musk zai kafa sabuwar jam’iyyar siyasa a Amurka Tinubu ya umarci sojoji su murƙushe ’yan ta’adda a faɗin Najeriya 

Bincike ya nuna kashi 83 cikin 100 na ’yan Najeriya ba su yadda da Gwamnatin Tarayya da Shugaba Tinubu ke jagoranta ba.

Haka kuma, kashi 82 cikin 100 ba su da ƙwarin gwiwa kan Majalisar Dokoki, wadda ke ƙarƙashin jagorancin Godswill Akpabio da Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas Tajudeen.

Ɓangaren shari’a, wanda Mai Shari’a Kudirat Kekere-Ekun ke jagoranta, ya nuna kashi 79 cikin 100 na mutane sun ce ba su yadda da sahihanci shari’a a ƙasar ba.

Rahoton ya nuna cewa Ma’aunin Haɗin Kan Al’umma a Najeriya ya tsaya a kashi 46.8 cikin 100, ƙasa da matsakaicin kashi 50 da ake buƙata ƙasa ta samu.

Wannan na nufin akwai matsaloli da dama da suka shafi rashin haɗin kai, rashin yadda da juna da rashin jin-ƙai a matsayin ’yan ƙasa ɗaya.

Darakta Janar na API, Farfesa Bell Ihua, ya bayyana cewa wannan shi ne mafi munin bincike wajen amincewa da gwamnati tun da suka fara gudanar da irin wannan bincike a shekarar 2019.

An gudanar da binciken ne daga watan Janairu zuwa Fabrairun 2025, inda aka zanta da mutum 5,465 a faɗin Najeriya.

An yi tambayoyin cikin harsunan gida irin su Hausa, Yarabanci, Igbo da Pidgin.

Binciken ya mayar da hankali kan ra’ayoyin jama’a game da abubuwa 14, kamar su yadda mutane ke kallon kansu, yadda suka yadda da gwamnati, shiga harkokin ƙasa, cin hanci, daidaito tsakanin jinsi da makomar ƙasar.

Matsin rayuwa ya haɗa kan ’yan Najeriya

Wahalhalun rayuwa sun haɗa kan jama’a a Najeriya, sai dai an samu rarrabuwar kai ta fuskar siyasa da ƙabilanci, amma mafi yawan ’yan Najeriya sun haɗu ne ta fuskar abin da ya shafi matsalar rayuwa.

Mutane da dama sun bayyana cewa suna fama da tsadar rayuwa musamman farashin abinci, sufuri da sauran abubuwan more rayuwa a ƙarƙashin abin da ake kira “Tattalin Arziƙin Tinubu”.

Rahoton ya ce kashi 53 cikin 100 na ’yan Najeriya sun ce suna takaicin yadda abubuwa suke a ƙasar, yayin da kashi 33 cikin 100 kacal ke alfahari da zama ’yan Najeriya.

Kashi 11 cikin 100 ne kacal suka nuna jin daɗin kasancewar ’yan Najeriya.

Rashin yadda da gwamnati da cin hanci

Duk da fargaba da rashin jin daɗin halin da ƙasar ke ciki, yawancin ’yan Najeriya har yanzu na yi mata fatan alheri.

Sakamakon binciken ya nuna cewa mutane da yawa na son shiga harkokin siyasa domin kawo canji.

Mutane da dama na goyon bayan auren juna tsakanin ƙabilu da addinai daban-daban domin samun haɗin kai.

Amma cin hanci da rashawa na ƙara ƙarfi. Mutum shida daga cikin 10 da aka tambaya sun ce cin hanci ya ƙaru cikin shekara guda.

Kashi 64 cikin 100 kuma sun ce gwamnati ba ta yin aiki yadda ya kamata wajen yaƙi da cin hanci.

Daidaiton jinsi da jagoranci

Game da batun daidaito tsakanin mata da maza, kashi 71 cikin 100 sun yadda cewa mata su ma za su iya riƙe madafun iko kamar maza.

Kashi 63 cikin 100 ma sun ce da za su samu dama za su kaɗa wa mata ƙuri’a domin zama shugabar ƙasa.

Amma kashi 39 cikin 100 kawai ke ganin cewa gwamnati na yin ƙoƙari wajen ganin an samu daidaito tsakanin jinsi.

Yi wa Najeriya fatan alheri

Duk da matsin rayuwa, kashi 56 cikin 100 na mutane suna yi wa Najeriya fatan alheri da burin ganin ta inganta.

Har ila yau, kashi 53 cikin 100 sun ce da za su samu dama, za su bar ƙasar tare da iyalansu. Yayin kashi 59 cikin 100 kuma sun ce ba sa jin daɗin irin rayuwar da suke yi yanzu.

Shawarar cibiyar API ga gwamnati

Cibiyar API ta bayar da shawarar cewa gwamnati ta kafa Hukumar Haɗin Kan Ƙasa wadda za ta kula da tsare-tsaren da za su taimaka wajen ɗinke ɓarakar da ke tsakanin ’yan ƙasa da kuma wanzar da amincewa da gwamnati.

Sannan ta ce gwamnati ta tabbatar da irin alƙawuran da take yi wa ’yan ƙasa, abin da ake kira yarjejeniya tsakanin gwamnati da al’umma domin kawo ƙarshen irin wannan rashin yadda.

Haka kuma, an buƙaci hukumomi irin su Hukumar Wayar da Kan Jama’a (NOA), Ma’aikatar Yaɗa Labarai, da Gidan Talabijin na (NTA( da su watsa shirye-shiryen da ke ƙarfafa haɗin kan al’umma da jin-ƙai.

Farfesa Ihua, ya jaddada rawar da ƙungiyoyin fararen hula za su iya takawa wajen dawo da amincewa, zaman lafiya da haɗin kai, wanda ya ce dole ne ’yan Najeriya su shiga harkokin al’umma da tattaunawa don samar da makoma ga ƙasar.

Wannan rahoton shi ne na huɗu da API ta fitar a jerin rahotanninta kan haɗin kai, bayan na shekarun 2019, 2021 da kuma 2022.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Kiyaye Hadura Ta Kasa Za Ta Aiki Da ‘Yan Jarida A Kano
  • Hukumar Abinci Ta Duniya ( WFP) Ta Jefa Wa Mutanane Kudancin Sudan Abinci Ta Sama
  • Zan Yi Ƙoƙarin Dawo Da Martabar Kano Pillars A Idon Duniya — Ahmed Musa
  • ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni
  • Hukumar Kula da Muhalli ta Jihar Jigawa ta Kwace Gurbatattun Kayayyaki na Miliyoyin Naira
  • Kano ta sami rahoton cin zarafin yara 351 – NHRC
  • Miliyoyin Yan Najeriya Ne Suka Gudanar da Tattakin Ashoora Wasu Kuma A Makarantunsu…
  • Bincike ya nuna ’yan Najeriya ba su gamsu da gwamnatin Tinubu ba
  •  Nijar: An Kashe Sojoji 10 A Wasu Hare-hare Biyu Na ‘Yan Ta’adda
  • Majalisar Dattawa ta gindaya sharaɗin dawo da Sanata Natasha