Aminiya:
2025-09-17@23:44:26 GMT

Ba abin da zai faru idan aka tsige Fubara – Wike

Published: 12th, March 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Jihar Ribas kuma Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya ce idan buƙatar tsige Gwamna Siminalayi Fubara ta zama tilas za a iya yi.

Wike ya bayyana haka a wata tattaunawa da manema labarai a ranar Laraba, inda ya jaddada cewa siyasa ba wasa ba ce, kuma ya kamata a bi ƙa’ida wajen tafiyar da mulki.

Zulum ya bai wa ƙananan ’yan kasuwa tallafin 1bn a Borno HOTUNA: An hana Gwamna Fubara shiga Majalisar Dokokin Ribas

Hakazalika, ya soki maganar cewa ‘yan majalisa ƙalilan za su iya zama domin yin dokokin jiha.

“Siyasa ba wasa ba ce. Idan har ya aikata abin da ya cancanci a tsige shi, to sai a tsige shi. Ba laifi ba ne,” in ji Wike.

“Ba zan yarda cewa a cikin wannan ƙasa, mutane na tunanin ‘yan majalisa uku za su zauna su yi doka, sannan su ce suna shirin zuwa Kotun Ƙoli.

“Shin har yanzu muna buƙatar yin aiki?” ya tambaya.

Rigimar siyasa a Jihar Ribas ta tsananta bayan da Kotun Ƙoli ta amince da sahihancin ‘yan majalisa 27 da ke goyon bayan Wike tare da soke zaɓen ƙananan hukumomin da aka gudanar a watan Oktoban 2024.

Har ila yau, Wike ya jinjina wa waɗanda suka ƙalubalanci abin da ya kira rashin bin doka, inda ya bayyana cewa dole ne a mutunta zaɓaɓɓun shugabanni.

“Shugabannin majalisa da ‘yan majalisa ba yara ba ne; an zaɓe su ne, kuma ba yaran kowa ba ne.

“Ya kamata a zauna da su, a gina dangantaka da su,” in ji shi.

Alaƙa dai na ci gaba da zafi tsakanin Wike da yaronsa Fubara, tun bayan da bar mulkin Jihar Ribas.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Fubara Siminalayi Fubara Siyasa yan majalisa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

Majalisar dattawa ta dakatar da Sanata Akpoti-Uduaghan a ranar 6 ga Maris, 2025, na tsawon watanni shida. Duk da cewa an kalubalanci lamarin a kotu, amma babbar kotun tarayya ba ta bayar da wani umarni na soke dakatarwar ba ko kuma tilasta sake dawo da ita bakin aiki.

 

A ranar 4 ga Satumba, 2025, Sanatar ta sanar da ofishin magatakarda akan aniyar ta na ci gaba da ayyukan majalisa, nan take, ofishin ya mika wasikar ga shugabannin majalisar dattawan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas
  • Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo
  • Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar