Aminiya:
2025-07-09@05:46:36 GMT

Malaman Tsangaya Sun Bai wa Gwamna Inuwa Lambar Yabo Ta ‘Khadimul Qur’an’

Published: 9th, March 2025 GMT

Ƙungiyar Malaman Tsangaya a Jihar Gombe ta karrama Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya lambar yabo ta ‘Khadimul Qur’an’ a matsayin girmamawa ga goyon bayansa maras misaltuwa ga ilimin Alƙur’ani da kuma matakan da ya ɗauka wajen kyautata tsarin Almajiranci.

Ƙungiyar Malaman Tsangaya ta miƙa wannan girmamawa ga Gwamnan yayin wani taron buɗa-baki na musamman da aka shirya musu a Fadar Gwamnati da ke Gombe, wanda ya tattaro shugabannin malaman Tsangaya daga faɗin jihar.

Ta’addancin yankin Sahel ya ninka na sauran sassan duniya — Rahoto Yadda masana’antun Arewa suka koma kufai

Wannan taron na cikin tsarin shekara-shekara na Gwamna Inuwa Yahaya na shirya shan ruwa tare da jama’a, wanda hakan wani mataki ne da yake ƙara haɗin kai, zaman lafiya, da hulɗa a tsakanin al’ummar Musulmi.

A jawabinsa bayan buɗa-bakin azumi, Gwamna Inuwa Yahaya ya sake jaddada ƙudurin gwamnatinsa na kyautata jin daɗin malaman Tsangaya da kuma yara Almajirai.

Ya bayyana muhimmancin ilimin Alƙur’ani ga al’umma tare da jaddada buƙatar samar da yanayi mai ɗaukaka koyo da koyarwa.

Gwamnan ya yi bayanin yadda gwamnatinsa ta yi gagarumin ƙoƙari wajen gina manyan makarantun Tsangaya da ƙananan makarantun Almajirai a faɗin jihar, tare da haɗa ilimin Alƙur’ani da na zamani cikin tsarin karatu.

Haka kuma, ya yi nuni da cewa yara Almajirai an sanya su cikin shirin lafiya na Go-Health, wanda ke ba su damar samun kulawar lafiya kyauta domin tabbatar da lafiyarsu.

“Mu a matsayin gwamnati mun fahimci muhimmiyar rawa da makarantun Tsangaya ke takawa wajen tarbiyya da cigaban ilimi ga yaranmu.

“Wannan ne ya sanya muka fifita jin daɗinsu ta hanyoyi daban-daban, ciki har da gina makarantun Tsangaya da kuma shigar da su cikin shirin Go-Health domin samun ingantacciyar kulawar lafiya ba tare da wata matsala ba,” in ji Gwamna Inuwa.

Da yake magana a madadin malaman Tsangaya, Goni Mai Babban Allo ya yaba wa Gwamna Inuwa Yahaya kan goyon bayan da yake bayarwa ba dare ba rana.

Ya kuma bayyana cewa Gwamnan ya ɗauki matakai na musamman, ciki har da gina makarantun Tsangaya, sanya fitilu masu aiki da hasken rana a makarantun, da haɗa Almajirai cikin shirin kula da lafiya na jihar Gombe.

“Ba mu taɓa samun gwamnati da ta damu da jin daɗin malaman Tsangaya da ɗalibanmu kamar wannan ba,” in ji Goni Mai Babban Allo.

A cikin girmamawa ga ƙoƙarinsa da kuma sadaukarwarsa, Ƙungiyar Alarammomi ta naɗa Gwamna Inuwa Yahaya sarautar ‘Khadimul Qur’an’, alamar kasancewarsa bawan Alƙur’ani mai sadaukarwa.

Tun da farko, a jawabinta na maraba, Sayyada Amina Sheikh Dahiru Bauchi, mai bai wa gwamna shawara ta musamman kan harkokin Tsangaya da Ilimin Almajiranci, ta yi kira ga Alarammomi da su ƙara yin addu’o’in zaman lafiya da ci gaban Jihar Gombe.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamna Inuwa Yahaya jihar Gombe malaman tsangaya Gwamna Inuwa Yahaya makarantun Tsangaya malaman Tsangaya a makarantun Tsangaya da

এছাড়াও পড়ুন:

Kira ga Haƙuri: A Dakatar da Ƙirƙirar Sabbin Masarautu a Jihar Bauchi

Saboda matsin lamba na doka da kuma la’akari da mahimman batutuwan siyasa, ya zama dole Gwamnatin Jihar Bauchi ta dakatar da duk wani ci gaba na aikin kwamitin da aka kafa a ranar 4 ga Yuli 2025 domin duba yiwuwar ƙirƙirar sabbin masarautu ko sauye-sauye ga tsarin majalisun gargajiya—musamman a yankunan da har yanzu ke fuskantar shari’a a kotu.

Ci gaba da wannan lamari mai sarkakiya alhali wasu muhimman ƙarar shari’a na ci gaba a kotuna, ba wai kawai zai saɓa wa kundin tsarin mulki da ikon shari’a ba, har ila yau, zai iya haddasa tayar da jijiyoyin wuya a cikin al’umma, musamman a yankunan da ke da tarihi na rikice-rikicen ƙabilanci kamar Tafawa Balewa da kewaye.

Wannan kira na haƙuri yana da tushe duka a doka da alhaki domin kare zaman lafiya da mutunta doka.

Shari’o’in da ke Gaban Kotu:

A bayyane yake cewa akwai manyan shari’o’i guda biyu da har yanzu ba a yanke hukunci kansu ba a Babbar Kotun Shari’a ta Jihar Bauchi, kuma akwai yiwuwar ɗaukaka ƙara zuwa Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke Jos:

Shari’o’in biyu sun haɗa da mai lamba: BA/191/2011 da ke gudana tsakanin Hon. Barr. Bukata Zhyadi da wasu 3 a ɓangare ɗaya, sai kuma Gwamnan Jihar Bauchi da wasu 15 a ɗaya ɓangaren.

Akwai kuma shari’a mai lamba: BA/173/2012 – wadda ake yi tsakanin Alhaji Maigida Abdullahi (Sarkin Tafawa Balewa) da wasu 4 a ɓangare ɗaya, da kuma Baba Garba Vurmi da wasu 7 a ɗaya ɓangaren.

Waɗannan shari’o’in suna da tushe a cikin dogon tarihin rikice-rikicen ƙabilanci a Tafawa Balewa, wanda tun daga 1959 ake fama da tarzoma lokaci zuwa lokaci, wanda ya haddasa salwantar rayuka da dukiya, sakamakon saɓani kan masarautun gargajiya, iyakokin ƙabilu da matsalolin ganewa tsakanin al’umma.

Ka’idar Haramta Tsoma Baki a Shari’ar Da ke Gaban Kotu:

Dangane da ka’idar (sub judice) wadda ta haramta tsoma baki a shari’ar da ke gaban kotu da kuma tanade-tanaden Kundin Tsarin Mulkin Tarayyar Najeriya na 1999 (wanda aka gyara), musamman sashe na 6(6)(b) — wanda ya ba da cikakken ikon yanke hukunci ga kotuna kawai.

Sai sashe na 14(2)(b) — wanda ya bayyana tsaron lafiya da walwalar jama’a a matsayin babban dalilin kafa gwamnati,

Ya zama rashin ɗa’a a doka, rashin adalci a akhlaƙi, da kuma sakaci a siyasa, a ci gaba da wani aiki na gwamnati ko na dokar majalisa wanda zai iya kawo cikas ga hukuncin da kotu take jira.

Bugu da ƙari, Kotun Koli ta Najeriya a hukuncinta na Gwamnan Legas a zamanin mulkin soji da kuma Ojukwu (1986) 1 NWLR (Pt. 18) 621, ta tabbatar da cewa babu wani ɓangare, har da gwamnati, da ya dace ya ɗauki mataki kai-tsaye a kan batutuwan da ke gaban kotu, domin hakan na raina ikon kotu da tsarin doka.

Ƙirƙirar sabbin masarautu ko ɗaukar matakin dokoki masu sarkakiya a yankunan da ake rigima da su, na iya sake tayar da tarzoma, karya zaman lafiya da rushe ƙoƙarin da aka daɗe ana yi na sasanta rigingimu a Kudancin Bauchi.

Shawarwari:

i) Gwamnatin Jihar Bauchi, Majalisar Zartarwa da Majalisar Dokoki su dakatar da duk wani tunani ko mataki kan ƙirƙirar sabbin masarautu ko sauya tsarin majalisun gargajiya a yankunan da abin ya shafa;

ii) Hukumomin tsaro da ƙungiyoyin wanzar da zaman lafiya su kasance cikin shiri da lura da duk wani yunƙuri da zai iya haddasa rikici a cikin al’umma;

iii) Sarakunan gargajiya, ƙungiyoyin al’umma da dattawan yankuna su tallafa wa bin doka da tafiyar da mulki bisa zaman lafiya.

Kammalawa:

Gwamnatin Jihar Bauchi ya kamata ta tuna cewa matakin da aka ɗauka cikin gaggawa ko wulaƙanta tsarin shari’a, na iya fuskantar soke daga kotu, kuma illar hakan ga rayukan al’umma da hadin kai na jama’a ba za a iya aunawa ba.

A bar kotu ta yanke hukunci. A bar zaman lafiya ya ɗore.

Saƙo daga Mukhtar Abubakar Tafawa Balewa Bauchi, Najeriya

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Malaman firamare sun janye yajin aiki a Abuja
  • Kotu Ta Ɗage Yanke Hukunci Kan Neman Izinin Jinyar Yahaya Bello
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Yace Mutanen Kasarsa Suna Cikin Shiri Don Kare Kansu Da Karfi
  • HKI Tana Tana Son Ci Gaba Da Yaki Kuma Trump Yana Tare Da Shi
  • Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%
  • Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Manya Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%
  • Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar
  • Kira ga Haƙuri: A Dakatar da Ƙirƙirar Sabbin Masarautu a Jihar Bauchi
  • China Ta Maida Martani da Haka Kayakin Kiwon Lafiya Na Tarayyar Turai Shigowa Kasar
  • Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC