Idan Kunne Ya Ji, Jiki Ya Tsira
Published: 6th, March 2025 GMT
Har ila yau, jim kadan bayan ficewar Zelenskyy daga Washington, shugabannin kasashen Turai da suka hada da na Jamus da Faransa da Italiya da kuma Birtaniya suka yi gaggawar mara masa baya, yayin da wasu ‘yan majalisar dokokin Amurka suka yi kakkausar suka ga Ukraine wanda a cewar Sanata Lindsey Graham na jam’iyyar Republican ta South Carolina, “sanadiyyar wannan ganawar da ta bar baya da kura, ka iya kawo karshen goyon bayan Washington ga Kyiv.
Shin abin tambaya a nan, da gaske ne wannan yunkurin na Amurka don kawo karshen rikici ne a tsakanin Ukraine da Rasha ko kuwa don amfanin kanta ne? Me ya sanya gwamnatin Trump ta fara wani gangamin tonon silili mai zafi kan Zelenskyy?
Kwanakin baya sakataren tsaron Amurka Pete Hegseth ya yi nuni da cewa, yunkurin Ukraine na shiga kungiyar NATO abu ne mara tabbas, tare da bai wa Kyiv shawarar daina fatan mallakar wani yankin kasa daga Rasha. Washington ta tattauna da Moscow a Saudi Arabia ba tare da Kyiev ba, wanda hakan ke nuna cewa za a iya yanke shawarar makomar Ukraine ba tare da saninta ba.
Bugu da kari, Trump ya kira Zelenskyy a matsayin “mai mulkin kama karya,” yana zargin Kyiv da fara tsokano rikici da Moscow. Sannan ya bukaci Zelenskyy ya rattaba hannu kan yarjejeniyar ma’adinai da Amurka da sauri, in ba haka ba, zai iya rasa duka kasarsa ga Rasha. A yayin ganawarsu ta ranar Juma’a, Trump ya zargi Zelenskyy da yunkurin kawo yakin duniya na uku. Duk wannan barazanar don cimma muradan son zuciyar Amurka na matsawa Kyiev rattaba hannu kan yarjejeniyar ma’adanai.
Wannan a fili yake, Amurka tana son dawo da kudadenta na tallafin soji da ta bai wa Ukraine na tsawon shekaru ba don neman zaman lafiyar yankin ba.
Don haka, Trump ya ki la’akari da bukatar Zelenskyy na neman tabbatar masa da tsaro sai dai matsa masa kan amincewa da yarjejeniyar hakar ma’adanan Ukraine.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Sudan ta soki takunkuman da Amurka ta kakaba mata
Gwamnatin Sudan ta soki takunkuman da Amurka ta kakaba wa wasu daidaikun mutane da kamfanoni na kasar.
Cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen kasar ta fitar, ta ce irin wannan mataki da bangare guda ya dauka ba zai taimaka wajen cimma abubuwan da ake buri ba, ciki har da cimma zaman lafiya a Sudan, da kare tsaro da zaman lafiyar duniya.
Sanarwar ta ce, gwamnatin Sudan na bayyana cewa, hanya mafi dacewa ta warware rikici ita ce tattaunawa kai tsaye, maimakon dogaro da zato, wanda wasu masu manufa ta siyasa suka kitsa, wadanda ba su dace da muradun al’ummar Sudan ba.
Sanarwa ta nanata cewa, samun zaman lafiya a kasar, babban batu ne da al’ummarta a ko ina ke buri.
Ta kara da tabbatar da cewa, hakkin gwamnatin Sudan ne cika burin tabbatuwar zaman lafiya ta kowacce hanya, ciki har da tattaunawa da hada hannu da dukkan bangarori.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Dakarun Sojin Yamen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ramon Na Isra’ila. September 14, 2025 Isra’ila Za ta Gamu Da Mummunar Martani Idan Tayi Gigin Afkawa Iran September 14, 2025 Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Larabawa Da Na Musulmi Sun Fara Taro A Qatar. September 14, 2025 Gwamnatin Najeriya Ta Sanar Da Sabon Sharadi Na Bude Asusun Banki September 14, 2025 An Zabi Issa Tchiroma A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A Kamaru September 14, 2025 Kasar Iran Ta Yi Fatali Da Zarge-Zargen Da Kungiyar G7 Da Kawayenta Suka Yi Kanta September 14, 2025 Iran Ta Bayyana Shirinta Na Halartar Taron Shekara-Shekara Na Hukumar Makamashin Nukiliya September 14, 2025 Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Bayyana Rashin Halarta Tawagarta A Kada Kuri’a Kan Batun Falasdinu September 14, 2025 Tsananin Masifar Da Falasdinawa Ke Ciki A Gaza Saboda Hare-Haren Gwamnatin Mamayar Isra’ila September 14, 2025 Amurka Ta Ce; Harin Isra’ila Kan Birnin Doha Ba Zai Shafi Kawancenta Da Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya Ba September 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci