Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta yi maraba da shirin sake gina Gaza na Masar da aka amince da shi a wani taron gaggawa na kasahen Larabawa da aka yi a birnin Alkahira.

Hamas ta bayyana a cikin wata sanarwa cewa, taron na birnin Alkahira ya nuna wani muhimmin mataki na daidaita alaka tsakanin Larabawa da Musulunmi da Falasdinu, musamman a ci gaba da hare-haren da Isra’ila ke ci gaba da yi a zirin Gaza, da yammacin kogin Jordan da kuma al-Quds.

Kungiyar ta yabawa shugabannin kasashen Larabawa da suka yi watsi da yunkurin raba Falasdinawa da kasarsu, tana mai danganta da sako mai cike da tarihi.

Hamas ta yi marhabin da kiran tana mai bayyana shi a matsayin “tsari mai inganci don mai da Isra’ila saniyar ware tare da matsa mata lamba ta bi dokokin kasa da kasa.”

Hamas ta jaddada bukatar aiwatar da shirin sake gina yankin, da tabbatar da isar da kayan agaji cikin gaggawa, da kuma yin aiki don tabbatar da tsagaita bude wuta da kuma tabbatar da an bi sharuddan da aka cimma.

A taron da suka gabatar ne Shugabannin kasashen Larabawa suka amince da shirin sake gina Gaza, wanda ya tabbatar da kin amincewa da korar Falasdinawa daga kasarsu “a karkashin kowane irin yanayi.”

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote

Mai kuɗin Afrika kuma Shugaban Matatar Mai ta Ɗangote, Alhaji Aliko Ɗangote, ya zargi wasu manyan masu harkar mai da shirya maƙarƙashiya domin kashe matatarsa.

Ɗangote ya yi zargin cewa miyagun ’yan kasuwan suna ƙoƙarin kashe matatar mansa mai darajar dala biliyan 20, kamar yadda aka kashe masana’antar tufafi ta ƙasar.

Ya bayyana haka ne a ranar Litinin a Legas yayin bikin cika shekara ɗaya da fara samar da fetur a matatar, inda ya ce tafiyar ta kasance cike da ƙalubale tun daga farko.

“A gaskiya tafiyar shekara ɗaya da ta wuce ta yi mana matuƙar wuya. Mun zo mu sauya tsarin kasuwancin man ƙasa. Amma wasu na ganin mun raba su da hanayar cin abinci bakinsu,” in ji shi.

’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba

Ya ci gaba da cewa, “Amma abin da muka yi shi ne mun sa Najeriya da nahiyar Afirka gaba ɗaya su yi alfahari.”

Ɗangote ya ce matatar ta riga ta fitar da lita biliyan 1.8 na man fetur zuwa ƙasashen waje cikin watanni uku da suka gabata, sannan tana da isasshen ƙarfi wajen cika buƙatar cikin gida.

Ya ce tun daga fara aikin matatar a watan Satumbar 2024, dogayen layukan man fetur da suka fi shekaru 50 ana fama da su a Najeriya sun zama tarihi.

Ɗangote ya ƙara da cewa farashin fetur ya sauka daga kusan Naira 1,100 zuwa N841 a wasu jihohi, kuma da zarar sabbin motocin gas (CNG) masu dakon mai sun fara aiki a duk faɗin ƙasar, rage farashin zai fi tasiri.

Ya kuma bayyana cewa sabbin motocin CNG 4,000 za su samar da aƙalla ayyukan yi 24,000, ciki har da direbobi, makanikai da sauran ma’aikata.

“Ba mu kore kowa daga aiki ba, sai dai muna ƙara samar da ayyuka,” in ji shi.

Ɗangote ya zargi masu harkar mai da haɗa kai da ’yan kasuwa na cikin gida da na waje da ƙoƙarin hana nasarar matatar.

“Yadda aka hallaka masana’antar yadi, haka suke ƙoƙarin kashe matatar mu,” in ji shi.

A kan zargin cewa bai wadatar da ƙasa da fetur ba, sai ya mayar da martani da cewa: “Idan ba mu da ƙarfin samar da mai, me ya sa muke fitarwa zuwa ƙasashen waje?”

Ya kuma yi ba’a ga Ƙungiyar Ma’aikatan Mai (NUPENG) wadda ta ce rage farashin fetur na matatar Dangote “kyautar Girka ce.” Dangote ya ce: “Ko da kuwa kyautar Girka ce, ai kyauta ce, za ta kuma ci gaba da kasancewa.”

Ya jaddada cewa abin da Najeriya ke buƙata yanzu shi ne kare masana’antunta, domin ci-gaban tattalin arziki da kuma rage dogaro da shigo da kaya daga waje.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Gaza: HKI Tana Ci Gaba Da Yi Wa Falasdinawa  Kisan Kiyashi A Gaza
  • Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano
  • Hamas Ta Karyata Gwamnatin Mamayar Isra’ila Kan Shirga Karya Don Kare Muggan Manufofinta
  • Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza
  • Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki Guda 5 A Wajen Taron Kolin kere-kere .
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana
  • Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu
  • Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar
  • Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila