Hamas Ta Yi Maraba Da Shirin Sake Gina Gaza Da Taron Kasashen Larabawa Ya Gabatar
Published: 5th, March 2025 GMT
Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta yi maraba da shirin sake gina Gaza na Masar da aka amince da shi a wani taron gaggawa na kasahen Larabawa da aka yi a birnin Alkahira.
Hamas ta bayyana a cikin wata sanarwa cewa, taron na birnin Alkahira ya nuna wani muhimmin mataki na daidaita alaka tsakanin Larabawa da Musulunmi da Falasdinu, musamman a ci gaba da hare-haren da Isra’ila ke ci gaba da yi a zirin Gaza, da yammacin kogin Jordan da kuma al-Quds.
Kungiyar ta yabawa shugabannin kasashen Larabawa da suka yi watsi da yunkurin raba Falasdinawa da kasarsu, tana mai danganta da sako mai cike da tarihi.
Hamas ta yi marhabin da kiran tana mai bayyana shi a matsayin “tsari mai inganci don mai da Isra’ila saniyar ware tare da matsa mata lamba ta bi dokokin kasa da kasa.”
Hamas ta jaddada bukatar aiwatar da shirin sake gina yankin, da tabbatar da isar da kayan agaji cikin gaggawa, da kuma yin aiki don tabbatar da tsagaita bude wuta da kuma tabbatar da an bi sharuddan da aka cimma.
A taron da suka gabatar ne Shugabannin kasashen Larabawa suka amince da shirin sake gina Gaza, wanda ya tabbatar da kin amincewa da korar Falasdinawa daga kasarsu “a karkashin kowane irin yanayi.”
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
MDD Zata Aiwatar Da Hanyar Warware Rikicin Falasdinawa Da Yahudawan Sahayoniyya
Sanarwar New York ya jaddada alƙawarin kasa da kasa na kawo ƙarshen yaƙin a Gaza da aiwatar da hanyoyin samar da ƙasashe biyu
Majalisar Dinkin Duniya ta sanar a cikin “Sanarwar New York” da yarjejeniyar kasa da kasa kan matakan dole da suka dace don kawo karshen yakin Gaza da aiwatar da Shirin samar da kasashe biyu da zai kai ga kafa kasar Falasdinu mai cikakken ‘yanci, da sake gina Gaza, da tura tawagar tabbatar da zaman lafiya ta kasa da kasa karkashin kulawar Majalisar Dinkin Duniya.
Sanarwar karshe da taron Majalisar Dinkin Duniya ya gudanar kan sasanta rikicin Falasdinu cikin lumana ya sanar da amincewar kasashen duniya kan daukar matakai na bai daya don kawo karshen hare-haren wuce gona da iri kan Gaza da kuma bin hanyar warware matsalar samar da kasashe biyu a matsayin zabi daya tilo na samun daidaito a yankin.
A cikin wani abin da aka fi sani da “Sanarwar New York”, shugabanni da wakilan da suka taru a Majalisar Dinkin Duniya sun amince da yin aiki don samar da adalci dawwamamme, da kuma daidaita rikicin Falasdinu da Isra’ila, suna mai jaddada cewa al’amuran baya-bayan nan sun nuna mummunan hasarar bil’adama da kuma mummunan sakamakon rikicin da ake ci gaba da yi.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Birtaniya Ta Yi Barazanar Amincewa Da Kasar Falasdinu A Watan Satumba Idan Yanayin Gaza Bai Canza Ba July 30, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Lod Da Ke Jaffa Da Makami Mai Linzami July 30, 2025 Faransa Ta Bayyana Wuce Gona Da Irin ‘Yan Sahayoniyya Kan Falasdinawa Da Ayyukan Ta’addanci July 30, 2025 Jagora: Iran Ta Bayyana Karfinta Da Jajircewarta A Yakin Kwanaki 12 Ga Duniya July 29, 2025 Mutum daya Yayi Shahada 4 Sun Ji Rauna Sanadiyar Hare-Haren HKI A Lebanon July 29, 2025 EU Tace Zata Dakatar Da HKI Daga Cibiyar Bincikenta Saboda Gaza July 29, 2025 Ma’aikatar Leken Asirin JMI Ta Ce Ta Gano Shirin Kashe Manyan Mutane 35 a kasar July 29, 2025 Najeriya: Likitoci a Lagas Sun Shiga Yajin Aiki July 29, 2025 Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai July 29, 2025 Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu July 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci