HausaTv:
2025-11-02@16:57:39 GMT

Kungiyar Hamas Ta Ki Amincewa Da Kwance Damarar Kungiyar A Gaza

Published: 5th, March 2025 GMT

Kungiyar Hamas wacce take iko da zirin Gaza, ya yi watsi da bukatar HKI na kwance damarar dakarun kungiyan a matsayin sharadi na ci gaba da aiwatar da yarjeniyar 19 ga watan Jenerun shekara ta 2025. Kungiyar ta kara da cewa, kwance damara dakarun kungiyar jar layi ne a wajenta.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa HKI tana bukatar ta raba kungiyar da makamanta, kafin ta ci gaba da aiwatar da yarjeniyar ta watan Jeneru.

Wannan  bukatar dai ta sa tababa a cikin yiyuwar tsagaita wuta tsakanin HKI da Hamas ya dore.

Yarjeniya ta yanzu dai, wacce ta faraaiki a ranar 19 ga watan Jenerun shekara ta 2025, kuma an tsara shi bisa marhaloli 3. Daga ciki har da tsarin yadda masu shiga tsakani zasu gabatar da musayar fursinoni da har zuwa janyewar sojojin HKI daga Gaza. Amma gwamnatin Natanyahu tace ba zata taba ficcewa daga Gaza ba.

Kakakin kungiyar Sami Abu Zuhri ya ce: Batun kwance damarar dakarun Izzudden Qassam, maganar banza ce. Makaman hamas jar laye ce, wand aba zata taba amincea da haka. Ministan harkokin wajen HKI, Gidion Sa’ar ya ce: Muna bukatar kwance damarar Hamasa da Jihadul Islamu da sauransu, sannan a mika mana yahudawan da ake garkuwa da su, idan sun yi haka, gobe ma a aiwatar da yarjeniyar.

Sannan wani kakakin kungiyar Hamas Hazem Qassem yace Hamas ba za ta amince da tsawaita marhala ta farko na yarjeniyar ba. Ya kuma bukaci a takurawa HKI don ta amince da ci gaba da aiwatar da marhaloli na gaba.

Natanyahu ya dauki yarjeniyar a matsayin na wucin gadi ne, don haka za’a iya komawa yaki a ko wani lokaci. A cikin makonni masu zuwa ne zamu gane, kan cewa, yarjeniyar zata ci gaba ko kuma za’a koma yaki.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: a aiwatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

 

Ban da haka, shugaban na Sin ya ce, kasarsa na son yin kokari tare da bangarori daban daban, wajen aiwatar da ra’ayin raya kasa na kirkiro sabbin fasahohi, da tabbatar da daidaito, da kare muhalli, da bude kofa, gami da haifar da alfanu ga kowa, ta yadda za a kafa wata al’ummar bai daya ta yankin Asiya da na tekun Pasifik.

 

Duk a wajen taron, yayin wani bikin mika damar karbar bakuncin taron kungiyar APEC, shugaba Xi Jinping ya sanar da cewa, kasar Sin za ta karbi bakuncin kwarya-kwaryar taron shugabannin kungiyar APEC karo na 33, wanda ake sa ran gudanar da shi a birnin Shenzhen na kasar Sin a watan Nuwamba na shekarar 2026. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka October 31, 2025 Daga Birnin Sin Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa October 31, 2025 Daga Birnin Sin Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza
  • Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 
  • Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • Israila Ta Kai Hari  Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda
  • Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma