Kungiyar Hamas Ta Ki Amincewa Da Kwance Damarar Kungiyar A Gaza
Published: 5th, March 2025 GMT
Kungiyar Hamas wacce take iko da zirin Gaza, ya yi watsi da bukatar HKI na kwance damarar dakarun kungiyan a matsayin sharadi na ci gaba da aiwatar da yarjeniyar 19 ga watan Jenerun shekara ta 2025. Kungiyar ta kara da cewa, kwance damara dakarun kungiyar jar layi ne a wajenta.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa HKI tana bukatar ta raba kungiyar da makamanta, kafin ta ci gaba da aiwatar da yarjeniyar ta watan Jeneru.
Yarjeniya ta yanzu dai, wacce ta faraaiki a ranar 19 ga watan Jenerun shekara ta 2025, kuma an tsara shi bisa marhaloli 3. Daga ciki har da tsarin yadda masu shiga tsakani zasu gabatar da musayar fursinoni da har zuwa janyewar sojojin HKI daga Gaza. Amma gwamnatin Natanyahu tace ba zata taba ficcewa daga Gaza ba.
Kakakin kungiyar Sami Abu Zuhri ya ce: Batun kwance damarar dakarun Izzudden Qassam, maganar banza ce. Makaman hamas jar laye ce, wand aba zata taba amincea da haka. Ministan harkokin wajen HKI, Gidion Sa’ar ya ce: Muna bukatar kwance damarar Hamasa da Jihadul Islamu da sauransu, sannan a mika mana yahudawan da ake garkuwa da su, idan sun yi haka, gobe ma a aiwatar da yarjeniyar.
Sannan wani kakakin kungiyar Hamas Hazem Qassem yace Hamas ba za ta amince da tsawaita marhala ta farko na yarjeniyar ba. Ya kuma bukaci a takurawa HKI don ta amince da ci gaba da aiwatar da marhaloli na gaba.
Natanyahu ya dauki yarjeniyar a matsayin na wucin gadi ne, don haka za’a iya komawa yaki a ko wani lokaci. A cikin makonni masu zuwa ne zamu gane, kan cewa, yarjeniyar zata ci gaba ko kuma za’a koma yaki.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: a aiwatar da
এছাড়াও পড়ুন:
Adadin Falasdinawan da Isra’ila take kashewa a Gaza yanzu ya haura 60,000
A ci gaba da hare-haren da dakarun Isra’ila ke kai wa a Zirin Gaza, yanzu adadin Falasdinawan da suka kashe ya kai 60,034.
A cewar wasu alkaluma daga Ma’aikatar Lafiya ta Gaza, baya ga wannan, adadin wadanda aka raunata kuma a yanzu sun haura 145,870.
Ma’aikatar ta kuma ce har yanzu ana zargin akwai mutanen kuma da ke karkashin baraguzan gine-ginen da aka rusa, wadanda ba za a iya ciro su daga ciki ba.
Fiye da kaso daya cikin uku na mutanen yankin na shafe kwanaki ba su ci abinci ba, kamar yadda wani rahoton samar da abinci mai lakabin IPC na Majalisar Dinkin Duniya ya tabbatar.
Rahoton ya ce ana samun karin hujjoji da ke nuna ana fama da yunwa da karancin abinci da kuma karuwar mace-mace masu alaka da yunwa a yankin da sama da mutum miliyan biyu da dubu dari daya ke rayuwa a cikinsa.
Hukumomi daban-daban na Majalisar Dinkin Duniya dai sun yi gargadin cewa ana fama da matsananciyar yunwar da aka kirkira da gangan a Gaza, inda a iya wannan watan, rahotanni suka tabbatar da mutuwar mutum 63, dalilin yunwar.
Hukumomin dai sun dora wa Isra’ila duk alhakin matsalolin, kasancewar ita ta yi wa yankin kawanya ta kuma hana a shigar da kayan agaji.
Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya, António Guterres, ya ce: “Abubuwa ne ga su nan a Zahiri, ba a boye suke ba. Falasdinawan da suke Gaza na cikin mawuyacin hali da tsananin bukatar agaji.
“Wannan ba wai gargadi muke yi ba. Gaskiya ce ga ta nan karara. Dole kayan agaji su ci gaba da kwarara. Abinci, ruwan sha, magunguna da man fetur dole su ci gaba da shiga ba tare da kowanne irin tarnaki ba,” in ji Guterres.