HausaTv:
2025-06-15@07:49:57 GMT

Kungiyar Hamas Ta Ki Amincewa Da Kwance Damarar Kungiyar A Gaza

Published: 5th, March 2025 GMT

Kungiyar Hamas wacce take iko da zirin Gaza, ya yi watsi da bukatar HKI na kwance damarar dakarun kungiyan a matsayin sharadi na ci gaba da aiwatar da yarjeniyar 19 ga watan Jenerun shekara ta 2025. Kungiyar ta kara da cewa, kwance damara dakarun kungiyar jar layi ne a wajenta.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa HKI tana bukatar ta raba kungiyar da makamanta, kafin ta ci gaba da aiwatar da yarjeniyar ta watan Jeneru.

Wannan  bukatar dai ta sa tababa a cikin yiyuwar tsagaita wuta tsakanin HKI da Hamas ya dore.

Yarjeniya ta yanzu dai, wacce ta faraaiki a ranar 19 ga watan Jenerun shekara ta 2025, kuma an tsara shi bisa marhaloli 3. Daga ciki har da tsarin yadda masu shiga tsakani zasu gabatar da musayar fursinoni da har zuwa janyewar sojojin HKI daga Gaza. Amma gwamnatin Natanyahu tace ba zata taba ficcewa daga Gaza ba.

Kakakin kungiyar Sami Abu Zuhri ya ce: Batun kwance damarar dakarun Izzudden Qassam, maganar banza ce. Makaman hamas jar laye ce, wand aba zata taba amincea da haka. Ministan harkokin wajen HKI, Gidion Sa’ar ya ce: Muna bukatar kwance damarar Hamasa da Jihadul Islamu da sauransu, sannan a mika mana yahudawan da ake garkuwa da su, idan sun yi haka, gobe ma a aiwatar da yarjeniyar.

Sannan wani kakakin kungiyar Hamas Hazem Qassem yace Hamas ba za ta amince da tsawaita marhala ta farko na yarjeniyar ba. Ya kuma bukaci a takurawa HKI don ta amince da ci gaba da aiwatar da marhaloli na gaba.

Natanyahu ya dauki yarjeniyar a matsayin na wucin gadi ne, don haka za’a iya komawa yaki a ko wani lokaci. A cikin makonni masu zuwa ne zamu gane, kan cewa, yarjeniyar zata ci gaba ko kuma za’a koma yaki.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: a aiwatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe

Dakarun Operation Haɗin Kai sun kama mut biyar da ake zargin suna taimaka wa ’yan ta’adda da kayan aiki.

Daga cikinsu har da wani ɗan ƙasar China da ya ce shi mai harkar ma’adinai ne.

Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya

An kama su ne a lokacin kai wani samame da aka gudanar daga 5 zuwa 7 ga watan Yuni a ƙananan hukumomin Kukawa da Ngala na Jihar Borno, da kuma Geidam a Jihar Yobe.

A lokacin wannan aiki, dakarun sun ƙwato wasu kayayyaki da suka haɗa da mota, babur, wayoyin salula, fasfo na ƙasar China, da kuma kuɗi Naira 10,000.

Shugaban sashen yaɗa labaran tsaro, Manjo Janar Edward Markus Kangye, ya bayyana hakan a wata ganawa da manema labarai a Abuja.

Ya ce sojojin sun kuma kai farmaki wasu yankuna bisa bayanan sirri da suka samu, ciki har da Gwoza da Abadam a Borno da kuma Nangere a Yobe, daga 6 zuwa 9 ga watan Yuni.

Ya ƙara da cewa daga 6 zuwa 11 ga watan Yuni, wasu maza da mata da yara da dama sun miƙa wuya ga dakarun Najeriya.

Kangye ya bayyana cewa rundunar ta kuma kai wasu hare-hare tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro a Ngala, Marte, Gwoza a Jjihar Borno da Bade da Gujba a Jihar Yobe daga 6 zuwa 10 ga watan Yuni.

A wannan lokaci, sun lalata sansanonin ’yan ta’adda, sun ƙwato makamai da alburusai.

Manjo Janar Kangye ya ce sojojin Najeriya za su ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin ’yan ƙasa tare da tabbatar da doka da oda.

“Mun ƙudiri aniyar kare martabar Najeriya da tabbatar da zaman lafiya a kowane yanki na ƙasar nan. Wannan aiki namu na ci gaba da yin tasiri,” in ji shi.

Ya buƙaci haɗin kan jama’a wajen taimaka wa sojoji su ci gaba da yaƙi da ’yan ta’adda.

Ya ce idan jama’a da hukumomi suka haɗa kai, Najeriya za ta samu zama lafiya da wadata.

“Zamu ci gaba da sanar da al’umma duk wani ci gaba da muka samu wajen yaƙar ta’addanci,” in ji Kangye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka 
  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Bukatar Kara Yawan Masu Fitowa Kada Kuri’a A Zabuka Nan Gaba
  • Leroy Sane ya koma Galatasaray
  • Hamas : Ziyarar ministan Isra’ila Ben-Gvir a masallacin al-Aqsa kan iya tayar da yakin addini
  • Isra’ila ta hana ayarin motocin agaji na arewacin Afrika shiga Gaza
  •   Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki