Kungiyar Hamas Ta Ki Amincewa Da Kwance Damarar Kungiyar A Gaza
Published: 5th, March 2025 GMT
Kungiyar Hamas wacce take iko da zirin Gaza, ya yi watsi da bukatar HKI na kwance damarar dakarun kungiyan a matsayin sharadi na ci gaba da aiwatar da yarjeniyar 19 ga watan Jenerun shekara ta 2025. Kungiyar ta kara da cewa, kwance damara dakarun kungiyar jar layi ne a wajenta.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa HKI tana bukatar ta raba kungiyar da makamanta, kafin ta ci gaba da aiwatar da yarjeniyar ta watan Jeneru.
Yarjeniya ta yanzu dai, wacce ta faraaiki a ranar 19 ga watan Jenerun shekara ta 2025, kuma an tsara shi bisa marhaloli 3. Daga ciki har da tsarin yadda masu shiga tsakani zasu gabatar da musayar fursinoni da har zuwa janyewar sojojin HKI daga Gaza. Amma gwamnatin Natanyahu tace ba zata taba ficcewa daga Gaza ba.
Kakakin kungiyar Sami Abu Zuhri ya ce: Batun kwance damarar dakarun Izzudden Qassam, maganar banza ce. Makaman hamas jar laye ce, wand aba zata taba amincea da haka. Ministan harkokin wajen HKI, Gidion Sa’ar ya ce: Muna bukatar kwance damarar Hamasa da Jihadul Islamu da sauransu, sannan a mika mana yahudawan da ake garkuwa da su, idan sun yi haka, gobe ma a aiwatar da yarjeniyar.
Sannan wani kakakin kungiyar Hamas Hazem Qassem yace Hamas ba za ta amince da tsawaita marhala ta farko na yarjeniyar ba. Ya kuma bukaci a takurawa HKI don ta amince da ci gaba da aiwatar da marhaloli na gaba.
Natanyahu ya dauki yarjeniyar a matsayin na wucin gadi ne, don haka za’a iya komawa yaki a ko wani lokaci. A cikin makonni masu zuwa ne zamu gane, kan cewa, yarjeniyar zata ci gaba ko kuma za’a koma yaki.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: a aiwatar da
এছাড়াও পড়ুন:
Kotu Ta Kori Ƙarar Neman Diyyar N1bn A Kan Buhari Da Emefiele Kan Sauya Fasalin Naira
Haka kuma ya nemi kotu da ta bayar da umarnin ci gaba da amfani da tsoffin takardun kuɗi na Naira 200, 500 da kuma 1000.
Baya ga haka, ya buƙaci a umarci su da su nemi gafara ta hanyar wallafa bayani a manyan jaridu biyu na ƙasa.
Amma a zaman kotu na ranar Litinin, wanda ya shigar da ƙarar da lauyansa ba su halarci zaman kotu ba.
Lauyan da ke kare Emefiele da CBN, Mista Chikelue Amasiani, ya sanar da kotu cewa tun da aka shigar da ƙarar, mai ƙarar da lauyansa ba su nuna wata alama ta son ci gaba da shari’ar ba.
Ya roƙi kotun da ta kori ƙarar.
Mai shari’a Ekwo ya amince da buƙatar kuma ya kori ƙarar, inda ya bayyana cewa mai ƙarar zai iya dawo da ita idan ya shirya yin shari’ar da gaske.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp