Taron lakca karo na 22 na kasar Sin da aka yi jiya Laraba a birnin Alkahiran Masar, ya hada malamai Sinawa da na kasar da jami’ai sama da 200, inda suka tattauna don gane da zurfafa hadin gwiwar Sin da Afrika, wajen daukaka zamanantar da kasashe masu tasowa.

Cibiyar nazarin dangantakar Sin da Afrika da cibiyar Confucius ta jami’ar Suez Canal ta Masar ne suka karbi bakuncin taron mai taken “Zurfafa hadin gwiwar Sin da Afrika domin jagorantar zamanantar da kasashe masu tasowa.

” Taron ya mayar da hankali ne kan karfafa dangantakar Sin da Masar, da fadada musaya tsakanin masana, da bunkasa tallafin ilimi ga kokarin kasashe masu tasowa na zamanantar da kansu.

Tattaunawar ta kuma jaddada batun kara inganta hadin gwiwar Sin da Afrika yayin da ake fama da sauye-sauye a duniya.

Da yake tsokaci, Hassan Rajab, daraktan cibiyar Confucius ta jami’ar Suez Canal, ya nanata raya al’adun bangarori daban daban a matsayi mai muhimmanci ga dangantakar Sin da Afrika, yana mai alakanta ta da shawarar wayewar kan al’ummar duniya da Sin ta gabatar. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Shin Amurka Na Iya Komawa Kan Kadaminta A Matsayin Cibiyar Masana’antun Duniya?

Bari mu dauki dala a matsayin misali, tattalin arzikin Amurka na dogara ne kacokan da girman dalar Amurka. Yayin da kasafin kudinta ke gazawa wajen biyan bukatunta na cikin gida, kuma tana da al’adar dogaro da kasashen waje kan kudaden da take kashewa da ke da alaka da jingina gazawar mulkinta ga sauran kasashen duniya, kamar yadda ta yi a lokacin rikicin hada-hadar kudi na duniya a shekarar 2008, ta yaya masana’antunta za su farfado bisa wannan tsarin?

 

Hakazalika, babu yadda za a yi Amurka ta sake zama cibiyar masana’antun duniya bayan da ta yi watsi da matsalolin da ake fuskanta a zahiri kamar sauyin yanayi, wanda ayyukan masana’antu ne suka haifar da shi tun farko. Bari mu dauka cewa Trump zai iya cimma nasarar aiwatar da manyan gyare-gyare game da tsarin kasar lokaci guda, zuwa kyakkyawan tsarin siyasa da tattalin arzikin kasar duk da cewa akwai rashin jituwa tsakanin jam’iyyun kasar. Kana bari mu dauka cewa mutanen Amurka da ma duniya baki daya za su koma sayen yawancin kayayyakin da ake samarwa a Amurka. Har yanzu an bar mu da wata tambaya, shin za a samu isassun Amurkawa da za su yarda su yi aiki a masana’antunta, kuma za su yi hakan kan albashi mara tsoka idan aka kwatanta da sauran kasashen duniya, bayan da Trump ya kori kaso da dama na baki daga kasar ta Amurka? (Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Najeriya Wajen Yin Watsi Da Kariyar Cinikayya Da Yin Adawa Da Danniya Da Cin Zarafi
  • Kar A Mika Wuya Ga “Damisar Takarda”
  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030
  •  Manyan Malaman Roman Katolika Sun Fara Taron Zabar Paparoma
  • Wang Yi: Neman Sulhu Da Ja Da Baya Riba Ne Ga Masu Son Cin Zali
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • Shin Amurka Na Iya Komawa Kan Kadaminta A Matsayin Cibiyar Masana’antun Duniya?
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
  • Akwai Ƙarin Gishiri A Yawan  Masu Sauyin Jam’iyya Zuwa APC – El-Rufai
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA