Gwamna Namadi Ya Bukaci Wadanda Suka Amfana Da Tallafin Mazabu Su Zama Masu Dogaro Da Kai
Published: 25th, February 2025 GMT
Gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa ya bukaci wadanda suka ci gajiyar shirin bayar da tallafi a mazabun jihar da su yi amfani da damar da suka samu domin dogaro da kai.
Ya bayyana hakan ne a wajen kaddamar da shirin da majalisar da ke wakiltar mazabar Kaugama ya yi.
Malam Umar Namadi wanda ya samu wakilcin Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Jigawa, Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin, ya ce shirin samar da tallafin a mazabu zai kara inganta manufofi 12 na gwamnatin jihar wadanda suka hada da karfafawa al’umma don bunkasa zamantakewa da tattalin arziki a kowane mataki.
Ya yi fatan wannan karimcin zai yi kyakkyawan tasiri ga mutane 1,200 da suka ci gajiyar tallafin.
A jawabinsa, dan majalisa mai wakiltar mazabar Kaugama a majalisar dokokin jihar Jigawa, Alhaji Sani Sale Zaburan, ya yabawa gwamna Umar Namadi bisa dimbin ayyuka da shirye-shiryen da aka aiwatar a karamar hukumar Kaugama.
A cewarsa, an ware sama da naira miliyan 30 domin gudanar da shirin kuma wadanda suka ci gajiyar shirin sun hada da kananan ‘yan kasuwa, masu karamin karfi da dai sauransu.
A jawabin maraba shugaban karamar hukumar Kaugama Alhaji Usman Masaki Dansule ya yabawa bangaren zartaswa da na majalisa bisa yadda suka fara shirin ,wanda zai ci gaba da bunkasa tattalin arzikin al’umma da ke karkara.
Don haka Dansule ya bukaci wadanda suka ci gajiyar tallafin da su yi amfani da kudaden don inganta rayuwarsu.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa da suka ci gajiyar wadanda suka
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kungiyar Hizbullah Ya Abbaci Abubuwa 3 Wadanda Yakamata Kasar Ta Maida Hankali A Kansu
Shugaban kungiyar hizbullah ta kasar Lebanon Sheikh Na’imKasim ya bayyana cewa, kungiyarsa tare da Sojojin kasar da kuma mutanen kasar ne zasu tabbatar da ci gaban kasar Lebanon a wannan halin da ake ciki.
Tashar talabijin ta Al-Mayadeen ta nakalto sheikh Na’im kasim yana fadar haka a wani jawabin da ya gabatar a jiya Litinin, jawabinda kafafen yada labarai da damaa suka watsa kai tsaye.
Sheikh Qasim kasar Lebanon zata ci gaba da zama mai karfi idan gwamnatin kasar ta dakatar da hare-haren da HKI take ci gaba da kawowa a kan kasar, da kwato dukkan yankunan kasar da aka mamaye, har’ila yau da kuma ci gaba da hadin kai tsakanin masu gwagwarmaya, sojoji da kuma mutanen kasar.
Shugaban kungiyar ya jadda bukatar sake gina wuraren da HKI ta rusa a yankunan daban daban a kasar, ya ce gwamnatin kasar ta yi alkawalin zata sake gina wuraren da HKI ta rusa a yakin da hizbullah a baya-bayan nan.
Kuma ya ce rashin yin haka nuna bambanci ne a tsakanin mutanen kasar. Ya ce dangane da wadanda aka rusa gidajensu kungiyar ta bada kudaden haya ga 50,755 , sannan ta gyura wasu 332 da aka lalata, wanda duk aikin gwamnati ne ta yi hakan. Don haka akwai bukatar gwamnati ta aikata wajibin da ya hau kanta.