Kungiyar Tarayyar Makiyaya ta CORET ta ce zata tallafawa yara makiyaya 1,600 a makarantun makiyaya guda shida a Jihohin Kaduna da Jigawa a wani yunƙuri na rage ƙarancin abinci da rashin ingantaccen abinci.

 

Sakataren Janar na CORET, Mohammed Bello Tukur ne ya bayyana hakan a lokacin ƙaddamar da shirin ciyar da ɗalibai na haɗin gwiwa a Laddauga, wurin kiwon dabbobi na Kachia a Jihar Kaduna.

 

Ya bayyana cewa, manufar wannan shiri ita ce tallafa wa shirin ciyar da ɗalibai na makarantun makiyaya.

 

Sakatare Janar ya ƙara da cewa kashi 60 na waɗanda za su amfana ‘yan mata ne, kuma shirin zai ƙarfafa ilimin kyawawan ɗabi’u a fannin abinci mai gina jiki, tsafta, tsabtace muhalli, da kuma sarrafa albarkatun ƙasa yadda ya dace.

 

Mohammed Bello Tukur ya bayyana cewa shirin yana kuma da niyyar samar da damammakin tattalin arziki da haɗin kai ga mata a cikin al’ummomin makiyaya guda shida da aka zaɓa.

 

“Muna son rage nauyin ciyar da ɗalibai da ke kan iyaye da kuma ƙara yawan yara da ke shiga makaranta. Bayan Kaduna, muna kuma duba Jihar Jigawa, Katsina, Taraba, Adamawa da Neja. Mun haɗa al’umma don dorewar shirin. Muna son gudanar da shirin na tsawon watanni 36.”

 

A jawabin Ministan Raya Dabbobi, ya bayyana cewa wannan shiri ya zo a daidai lokaci, kuma zai samar da abinci mai gina jiki ga yara wanda zai ƙara musu basira.

 

“Shirin zai samar da abinci mai gina jiki ga yara wanda zai ƙara musu basira kuma zai ƙarfafa su wajen zuwa makaranta, wanda hakan zai rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta. Haka kuma zai sa su zama masu amfani ga al’umma.”

 

Ministan wanda ya samu wakilcin Mataimakinsa na Musamman, Dr. Ishaq Bello, ya bayyana cewa gwamnatin tarayya za ta ci gaba da bullo da manufofi da shirye-shiryen da za su inganta kiwon dabbobi a ƙasar.

 

Tun da farko, Daraktan Noma da Raya Kauyuka na ECOWAS, Alain Traore wanda Dr. Saater Kumaga ya wakilta ya bayyana cewa ECOWAS na aiwatar da ayyuka 127 a ƙasashe memba 15.

 

Ya bayyana cewa daga cikin waɗannan ayyuka, guda uku ana aiwatar da su ne a Jihar Kaduna.

 

Manajan shirin, Dr. Abdullahi Umar ya gode wa al’ummar Kachia, yana mai roƙon su su bayar da haɗin kai don nasarar shirin.

 

Hakimin Ladduga, Alhaji Ahmed Jibril ya tabbatar wa CORET da cikakken haɗin kai don nasarar shirin.

 

An aiwatar da shirin ne a Kachia, wurin kiwon dabbobi na Laddauga a Jihar Kaduna da kuma Maigatari Trans-boarder axis a Maigatari LGA Jihar Jigawa, tare da tallafin Hukumar ECOWAS – Cibiyar Raya Yankin Noma (RAAF) da haɗin gwiwar Kungiyar Taimakon Ci Gaba ta Sifen (SDC).

 

Makarantun da aka zaɓa a Kaduna sun haɗa da: Makarantar Firamare ta Makiyaya Wuro Nyako wurin kiwon dabbobi na Kachia, Makarantar Firamare ta Makiyaya Mbela Biradam Ladduga wurin kiwon dabbobi na Kachia, da Makarantar Firamare ta Makiyaya Tiggirde Ladduga wurin kiwon dabbobi na Kachia.

 

A Maigatari Trans-boarder axis a Jigawa kuwa sun haɗa da: Makarantar Firamare ta Makiyaya Lawan Dutsi, Makarantar Firamare ta Makiyaya Bulama Kauje da Makarantar Firamare ta Makiyaya Gidan Tinau.

 

COV: Adamu Yusuf

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Araqchi: Iran Zata Mayar Da Martanin Da Ba Zai Yiwu A Boye Ba  Kan Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kanta

Ministan harkokin wajen Iran ya jaddada cewa: Idan aka maimaita ta’asar kai hari kan Iran, za ta mayar da martani ta hanyar da ba za a iya boyewa ba

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya mayar da martani kan barazanar da jami’an Amurka suka yi a baya-bayan nan, inda ya ce idan aka sake kai hari kan Iran, za ta mayar da martani mai tsauri wanda ba zai yiwu a iya boye ba.

Araghchi ya kara da cewa a cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter a ranar Litinin din nan cewa: Iran, kasar da ke da al’adun gargajiyar da ta shafe shekaru dubu bakwai na wayewar kai, ba za ta taba mika kai ga barazana da tsoratarwa ba. Iraniyawa ba su taba mika kai ga kasashen waje ba kuma ba su bukatar komai sai girmamawa.

Ya ci gaba da cewa: “Iran ta san hakikanin abin da aka yi mata da kuma abin da makiya suka fuskanta a lokacin farmakin da ‘yan sahayoniyya da Amurka suka yi a baya-bayan nan, ciki har da yawan munanan hare-haren da ta kai a matsayin daukan fansa wadanda ake ci gaba da boyewa. Don haka idan makiya suka sake kuskuren kai hari kan Iran, babu shakka zasu fuskanci martani mai gauni da ba zai yiwu a iya boyewa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Tallafin Miliyoyin Naira Ga Ƴan NURTW da Mahauta a Jigawa
  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma
  • Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati
  • Ma’aikatar Leken Asirin JMI Ta Ce Ta Gano Shirin Kashe Manyan Mutane 35 a kasar
  • Araqchi: Iran Zata Mayar Da Martanin Da Ba Zai Yiwu A Boye Ba  Kan Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kanta
  • An kashe ’yan ta’adda 45 a Neja
  • Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin Bai Wa Malaman Manyan Makarantun Nijeriya Rancen Miliyan 10
  • Wulayati: Hanyar Zangezur Wata Shirin Amurka Ne Don Matsa lamba Kan Iran Da Rasha