Kungiyar Tarayyar Makiyaya ta CORET ta ce zata tallafawa yara makiyaya 1,600 a makarantun makiyaya guda shida a Jihohin Kaduna da Jigawa a wani yunƙuri na rage ƙarancin abinci da rashin ingantaccen abinci.

 

Sakataren Janar na CORET, Mohammed Bello Tukur ne ya bayyana hakan a lokacin ƙaddamar da shirin ciyar da ɗalibai na haɗin gwiwa a Laddauga, wurin kiwon dabbobi na Kachia a Jihar Kaduna.

 

Ya bayyana cewa, manufar wannan shiri ita ce tallafa wa shirin ciyar da ɗalibai na makarantun makiyaya.

 

Sakatare Janar ya ƙara da cewa kashi 60 na waɗanda za su amfana ‘yan mata ne, kuma shirin zai ƙarfafa ilimin kyawawan ɗabi’u a fannin abinci mai gina jiki, tsafta, tsabtace muhalli, da kuma sarrafa albarkatun ƙasa yadda ya dace.

 

Mohammed Bello Tukur ya bayyana cewa shirin yana kuma da niyyar samar da damammakin tattalin arziki da haɗin kai ga mata a cikin al’ummomin makiyaya guda shida da aka zaɓa.

 

“Muna son rage nauyin ciyar da ɗalibai da ke kan iyaye da kuma ƙara yawan yara da ke shiga makaranta. Bayan Kaduna, muna kuma duba Jihar Jigawa, Katsina, Taraba, Adamawa da Neja. Mun haɗa al’umma don dorewar shirin. Muna son gudanar da shirin na tsawon watanni 36.”

 

A jawabin Ministan Raya Dabbobi, ya bayyana cewa wannan shiri ya zo a daidai lokaci, kuma zai samar da abinci mai gina jiki ga yara wanda zai ƙara musu basira.

 

“Shirin zai samar da abinci mai gina jiki ga yara wanda zai ƙara musu basira kuma zai ƙarfafa su wajen zuwa makaranta, wanda hakan zai rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta. Haka kuma zai sa su zama masu amfani ga al’umma.”

 

Ministan wanda ya samu wakilcin Mataimakinsa na Musamman, Dr. Ishaq Bello, ya bayyana cewa gwamnatin tarayya za ta ci gaba da bullo da manufofi da shirye-shiryen da za su inganta kiwon dabbobi a ƙasar.

 

Tun da farko, Daraktan Noma da Raya Kauyuka na ECOWAS, Alain Traore wanda Dr. Saater Kumaga ya wakilta ya bayyana cewa ECOWAS na aiwatar da ayyuka 127 a ƙasashe memba 15.

 

Ya bayyana cewa daga cikin waɗannan ayyuka, guda uku ana aiwatar da su ne a Jihar Kaduna.

 

Manajan shirin, Dr. Abdullahi Umar ya gode wa al’ummar Kachia, yana mai roƙon su su bayar da haɗin kai don nasarar shirin.

 

Hakimin Ladduga, Alhaji Ahmed Jibril ya tabbatar wa CORET da cikakken haɗin kai don nasarar shirin.

 

An aiwatar da shirin ne a Kachia, wurin kiwon dabbobi na Laddauga a Jihar Kaduna da kuma Maigatari Trans-boarder axis a Maigatari LGA Jihar Jigawa, tare da tallafin Hukumar ECOWAS – Cibiyar Raya Yankin Noma (RAAF) da haɗin gwiwar Kungiyar Taimakon Ci Gaba ta Sifen (SDC).

 

Makarantun da aka zaɓa a Kaduna sun haɗa da: Makarantar Firamare ta Makiyaya Wuro Nyako wurin kiwon dabbobi na Kachia, Makarantar Firamare ta Makiyaya Mbela Biradam Ladduga wurin kiwon dabbobi na Kachia, da Makarantar Firamare ta Makiyaya Tiggirde Ladduga wurin kiwon dabbobi na Kachia.

 

A Maigatari Trans-boarder axis a Jigawa kuwa sun haɗa da: Makarantar Firamare ta Makiyaya Lawan Dutsi, Makarantar Firamare ta Makiyaya Bulama Kauje da Makarantar Firamare ta Makiyaya Gidan Tinau.

 

COV: Adamu Yusuf

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Hajj 2025: Kaduna Ta Gaddamar Da Ayarin Likitoci Da Za Su Kula Da Alhazan Jihar

Gwamna Uba Sani na Jihar Kaduna ya kaddamar da ayarin likitoci su tara domin kula da lafiyar maniyata aikin hajjin na wannan shekaran.

Shugaban Hukumar Jin Daɗin Alhazan Jihar Kaduna, Malam Salihu S. Abubakar, ne ya bayyana hakan bayan ganawar farko da ayarin da kuma shugabannin hukumar.

Ayarin likitocin ƙarƙashin jagorancin Dr. Bello Jamoh, za su gudanar da cikakken binciken lafiyar maniyata kafin tafiyar su zuwa kasa mai tsarki da zai gudana a sansanin alhazai da ke Mando, Kaduna.

Sannan kuma za su bayar da taimakon gaggawa a kasar Saudiyya tare da haɗin gwiwar Ayarin likitocin daga Hukumar Hajji ta Kasa (NAHCON).

Shugaban hukumar ya ce mambobin ayarin za su kasance cikin tsari na duba lafiyar mahajjata a tsawon lokacin aikin hajjin.

“Lafiya maniyata aikin hajjin tana da matuƙar muhimmanci, mun zaɓi ayarin ne bisa ƙwarewarsu, kuma muna da tabbacin za su bayar da ingantaccen kulawa ta lafiya a lokacin aikin hajjin,” In ji shi.

Shugaban ya ƙara da cewa za a gudanar da cikakken gwajin lafiya ga dukkan masu niyyar zuwa aikin Hajj, musamman don gano mata masu juna biyu.

Babu sassauci ko kaɗan wajen barin mata masu juna biyu su tafi Hajj.” in ji Malam Salihu, yana mai jaddada cewa gudunmuwar da ayarin likitocin za su bada wajen tabbatar da wannan doka, na da muhimmanci don bin ƙa’idodin aikin Hajjin.

Ya ja hankalin ayarin likitocin su gudanar da aikinsu cikin ƙwarewa da sadaukarwa, domin tabbatar da cewa mahajjata sun samu aikin hajji mai sauƙi cikin koshin lafiya.

 

Adamu Yusuf

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hajj 2025: Kaduna Ta Gaddamar Da Ayarin Likitoci Da Za Su Kula Da Alhazan Jihar
  • Ma’aikatar Sharia A Nan Iran Zata Bayyana Abinda ya farsu A Tashar Jiragen Ruwa Na Shahid Rajae
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna
  • Za A Yi Allurar Rigakafi Ga Dabbobi Sama Da Miliyan Daya A Babura
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Shirya Fara Tantance ‘Yan Fansho
  • Gwamna Namadi Ya Nada Aisha Mujaddadi Sabuwar Shugabar Hukumar InvestJigawa
  • Hajjin 2025: An Fara Yi Wa Maniyyata Allurar Rigakafi A Jigawa
  • Hajjin 2025: Gwamna Namadi Ya Nada Sarkin Kazaure Amirul Hajj
  • Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026
  • Iran Da Rasha Sun Jaddada Yin Aiki Tare A Fagen Kiwon Lafiya