Domin magance wannan kalubale, Muhammed ya ba da shawarar ka da a bar mutane su dauki kudi fiye da naira 50,000 a rumfunan zabe.

“Sayen kuri’u na daya daga cikin manyan barazana ga sahihin zabe a Nijeriya. Muna bukatar dokar da ba wai kawai ta haramta wannan dabi’ar ba har ma da sanya matakan kariya,” in ji Muhammed.

Bayan sayen kuri’u, jami’an INEC sun sake jaddada bukatar da suka dade suna yi na a kafa hukumar da ke yaki da laifukan zabe, suna masu cewa hukumar zabe ba ta da karfin gurfanar da masu laifi a gaban kotu.

A cewar Muhammed, “INEC na iya bakin kokarinta wajen ganin an gurfanar da masu laifukan zabe a gaban kotu, amma muna bukatar wata cibiya mai kwazo da ke da hurumin shari’a da kayan aiki domin gudanar da bincike tare da hukunta masu aikata laifukan zabe. Samar da hukumar zai tabbatar da cewa hukuncin sayen kuri’u, satar kuri’u, da sauran laifuffuka cikin gaggawa”.

Kwamishinan ‘yansanda mai kula da tsare-tsare da tantance harkokin zabe, Abayomi Shogunle, wanda ya wakilci babban sufetan ‘yansanda, ya yi nuni da cewa rashin isassun kayan aiki ya kan kawo cikas ga kokarin tabbatar da doka a lokacin zabe. “Muna fuskantar manyan kalubalen kayan aiki, tun daga tura jami’ai zuwa lunguna da sako da kuma tabbatar da sadarwa a lokacin zabe. Wadannan batutuwa ne da ya kamata a magance su idan ana son a aiwatar da dokokin zabe yadda ya kamata,” in ji Shogunle.

Da yake mayar da martani kan matsalolin da suka taso, shugaban kwamitin majalisar kan harkokin zabe, Hon. Adebayo Balogun, ya bayar da tabbacin cewa za a magance dukkan batutuwan da aka tattauna tare da sake fasalin zabe a nan gaba.

“Dokar zaben 2022, tana da matukar muhimmin wajen ci gaba, amma aiwatar da ita a babban zaben da ya gabata ya nuna wuraren da ke bukatar gyara. Mun himmatu wajen karfafa dokokin zabenmu don nuna gaskiyar dimokuradiyyarmu,” in ji Balogun.

Ya jaddada cewa, baya ga garambawul na majalisar, akwai bukatar kara wayar da kan jam’iyyun siyasa, jami’an INEC, da kungiyoyin fararen hula kan illolin da ke tattare da sayen kuri’u da sauran kura-kurai a zaɓen ƙasar nan.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Zaɓe

এছাড়াও পড়ুন:

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Kwanan baya, jagoran yankin Taiwan na kasar Sin Lai Cing-te, ya fitar da wani bayani a fili, inda a ciki ya canja asalin tarihin kasar Sin, kana ya musanta cewa yankin Taiwan wani yanki ne na kasar Sin tun da da can, kuma, ya kauce wa yin tsokaci kan jerin takardun dokoki na kasashen duniya, wadanda suka bayyana yankin Taiwan a matsayin wani yanki na kasar Sin bayan yakin duniya na biyu.

Kazalika, ya kalubalanci kuduri mai lamba 2758 na babban taron MDD da dokokin kasashen duniya. Babu shakka, abin da Lai Cing-te ya yi ya sa ya zama abokin gaban dukkan al’ummomin kasar Sin, da yawansu ya zarce biliyan 1 da miliyan 400, kana ya mai da shi kansa a matsayin mai adawa da tsarin kasa da kasa da yanayin adalci na duniya.

Sai dai, ko me mahukuntan gwamnatin Lai Ching-te za su yi, ba zai canja anihin batun ba, wato yankin Taiwan wani yanki ne na kasar Sin, kuma ba zai canja ra’ayin gamayyar kasa da kasa ba na tsayawa tsayin daka kan manufar “kasar Sin kasa daya tak” a duniya, balle hana dunkulewar kasar Sin baki daya. (Mai Fassara: Maryam Yang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya
  • Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
  • Iran ta Ki Amincewa Da Ziyarar Shugaban Hukumar IAEA Zuwa Kasar
  • Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko
  • Bom ya kashe mutum hudu da raunata 21 a Yobe
  • Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba
  • Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
  • NDLEA ta kafa cibiyar kula da masu shaye-shaye a Yobe 
  • Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP
  • Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji