Leadership News Hausa:
2025-11-03@07:47:58 GMT

Malamai Suna Takara Da ’Yan Siyasa Wajen Neman Mulki –Sule Lamido

Published: 21st, February 2025 GMT

Malamai Suna Takara Da ’Yan Siyasa Wajen Neman Mulki –Sule Lamido

Idan za a iya tunawa dai, malaman addini sun taka rawa wajen zaburar da jama’arsu domin yin rajistar masu zabe. Duk da haka, a babban zaben 2023 wanda yana daya daga cikin mafi zaben da ya janyo rarrabuwar kawuna a Nijeriya, masallatai da coci-coci sun taka rawar gani wajen tursasa mabiyansu su zabi nasu ‘yan takara.

Mafi yawancin wa’azi da khudubobi sun kasance wurin tattauna harkokin siyasa. A wasu majami’u, fastoci sun yi da’awar manzancin kan ‘yan takararsu, yayin da a cikin malaman addinin musulmi, limamai sun bukaci mabiya da su yi zabe ta hanyar addini. Abin mamaki, yawancin wadannan hasashen addini ba su tabbata ba.

A kwann nan dai an tafka cece-kuce kan taron da aka shirya gudanarwa a ranar 22 ga watan Fabrairun 2025 a Abuja, wanda ake sa ran za a hada mahardata alkur’ani har 30,000. An dage taron ne ba tare da saka wani lokaci ba, sakamakon kalubalantar lamarin da wasu malaman addinin Islama suka nuna, inda suka nuna shakku kan sahihancinsa tare da zargin cewa wani yunkuri ne na siyasa gabanin zaben shugaban kasa na 2027.

Idn za a iya tunawa dai, tikitin tsayawa takarar shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu na Musulmi-musulmi a shekarar 2023, wanda kusan ya wargaje tsarin fagen siyasa, a karshe ya tsira saboda gagarumin goyon baya daga malaman addini da suka tabbatar wa mabiyansu. Shi ma kabilanci da bangarenci, musamman a kudu maso yamma ya taka rawar gani.

A lokacin zaben 2023, abokan Tinubu a arewacin Nijeriya sun yi zawarcin manyan malaman ddinin Musulunci, inda suka samu goyon bayansu. Yanzu, da alama ana ci gaba da yin irin wannan kokarin, yayin da ‘yan wasan siyasa suka fara dabarun lashe zabe a 2027.

A daya hannun kuma, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi, ana kyautata zaton zai sake dauko abokin takararsa daga yankin arewacin kasar da galibinsu musulmai ne a zabe mai zuwa. Kasancewarsa yana halartar tarukan da suka shafi addinin Musulunci, ana kallonsa a matsayin wanda yake kokari wajen jawo hankalin malaman addini domin samun nasara.

Magoya bayan Obi sun ce baya ga zargin tafka magudin zaben da kuma gazawarsa wajen shigar da shugabannin addini a arewacin kasar ya taimaka matuka gaya wajen rashin nasararsa a 2023. Yayin da zaben 2027 ke gabatowa, da alama magoya bayansa sun kudiri aniyar kauce wa kuskuren da suka yi a zaben da ya gabata.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Siyasa takara

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta tsige dan majalisar wakilai, Abubakar Gummi daga kujerarsa saboda sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa APC.

Gummi yana wakiltar mazabar Gummi/Bukkuyum ta Jihar Zamfara a majalisar wakilai.

An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku

Mai shari’a Obiora Egwuatu ne, ya yanke hukuncin, inda ya umarci kakakin majalisar wakilai, Tajudeen Abbas, da ya daina amincewa da Gummi a matsayin dan majalisar da ke wakiltar mazabar Gummi/Bukkuyum.

Haka kuma ya umarci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ta shirya sabon zabe cikin kwanaki 30 domin cike gurbin kujerar dan majalisar.

Jam’iyyar PDP tare da shugaban ta na jihar Zamfara, Jamilu Jibomagayaki, ne suka shigar da karar dan majalisar.

Sun ce bai dace Gummi ya ci gaba da zama a kujerar ba bayan barin jam’iyyar da ta tsayar da shi takara.

Gummi, ta bakin lauyansa ya ce ya fice daga PDP ne saboda rikicin cikin gida da jam’iyyar ke fama da shi a matakin kasa da kuma a mazabarsa.

Amma kotu ta yi watsi da wannan hujjar, inda ta bayyana cewa babu takaddama da za ta ba shi damar ya sauya sheka.

A hukuncin da ya yanke, Mai shari’a Egwuatu ya ce ’yan siyasa dole su mutunta zabin jama’ar da suka kada musu kuri’a a karkashin jam’iyyar da ta tsayar da su takara.

Ya ce doka ba ta yadda da dan siyasa ya bar jam’iyyar da ta taimaka masa wajen lashe zabe sannan ya koma wata jam’iyya ba tare da ajiye mukaminsa ba.

Ya kara da cewa kuri’un da aka kada don dan takarar na jam’iyya ne, ba nasa ne na kashin kansa ba.

“Idan mutum yana son sauya sheka, ka da ya dauki amanar jama’ar da ta zabe shi ya tafi da ita,”  in ji alkalin.

Kotu ta kuma umarci Gummi da ya daina karbar albashi da wasu hakkoki a matsayin dan majalisa, tare da mayar da duk kudaden da ya karba daga ranar 30 ga watan Oktoba, 2024, zuwa ranar da aka yanke hukuncin.

Haka kuma, ya gabatar da hujjar mayar da kudaden ga kotu cikin kwanaki 30.

Mai shari’a Egwuatu ya kuma ci Gummi tarar Naira N500,000, domin biyan PDP kudaden da ta kashe wajen shigar da kara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
  • Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • Zargin Kisan Kiristoci: Maganar Trump a kan Najeriya tsagwaron ƙarya ce — Shehu Sani
  • Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
  • Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP