Leadership News Hausa:
2025-06-15@23:15:41 GMT

Malamai Suna Takara Da ’Yan Siyasa Wajen Neman Mulki –Sule Lamido

Published: 21st, February 2025 GMT

Malamai Suna Takara Da ’Yan Siyasa Wajen Neman Mulki –Sule Lamido

Idan za a iya tunawa dai, malaman addini sun taka rawa wajen zaburar da jama’arsu domin yin rajistar masu zabe. Duk da haka, a babban zaben 2023 wanda yana daya daga cikin mafi zaben da ya janyo rarrabuwar kawuna a Nijeriya, masallatai da coci-coci sun taka rawar gani wajen tursasa mabiyansu su zabi nasu ‘yan takara.

Mafi yawancin wa’azi da khudubobi sun kasance wurin tattauna harkokin siyasa. A wasu majami’u, fastoci sun yi da’awar manzancin kan ‘yan takararsu, yayin da a cikin malaman addinin musulmi, limamai sun bukaci mabiya da su yi zabe ta hanyar addini. Abin mamaki, yawancin wadannan hasashen addini ba su tabbata ba.

A kwann nan dai an tafka cece-kuce kan taron da aka shirya gudanarwa a ranar 22 ga watan Fabrairun 2025 a Abuja, wanda ake sa ran za a hada mahardata alkur’ani har 30,000. An dage taron ne ba tare da saka wani lokaci ba, sakamakon kalubalantar lamarin da wasu malaman addinin Islama suka nuna, inda suka nuna shakku kan sahihancinsa tare da zargin cewa wani yunkuri ne na siyasa gabanin zaben shugaban kasa na 2027.

Idn za a iya tunawa dai, tikitin tsayawa takarar shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu na Musulmi-musulmi a shekarar 2023, wanda kusan ya wargaje tsarin fagen siyasa, a karshe ya tsira saboda gagarumin goyon baya daga malaman addini da suka tabbatar wa mabiyansu. Shi ma kabilanci da bangarenci, musamman a kudu maso yamma ya taka rawar gani.

A lokacin zaben 2023, abokan Tinubu a arewacin Nijeriya sun yi zawarcin manyan malaman ddinin Musulunci, inda suka samu goyon bayansu. Yanzu, da alama ana ci gaba da yin irin wannan kokarin, yayin da ‘yan wasan siyasa suka fara dabarun lashe zabe a 2027.

A daya hannun kuma, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi, ana kyautata zaton zai sake dauko abokin takararsa daga yankin arewacin kasar da galibinsu musulmai ne a zabe mai zuwa. Kasancewarsa yana halartar tarukan da suka shafi addinin Musulunci, ana kallonsa a matsayin wanda yake kokari wajen jawo hankalin malaman addini domin samun nasara.

Magoya bayan Obi sun ce baya ga zargin tafka magudin zaben da kuma gazawarsa wajen shigar da shugabannin addini a arewacin kasar ya taimaka matuka gaya wajen rashin nasararsa a 2023. Yayin da zaben 2027 ke gabatowa, da alama magoya bayansa sun kudiri aniyar kauce wa kuskuren da suka yi a zaben da ya gabata.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Siyasa takara

এছাড়াও পড়ুন:

Harin Benuwe: ’Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga

An shiga zaman ɗari-ɗari a garin Makurdi na Jihar Benuwe, bayan ’yan sanda sun harba barkonon tsohuwa domin tarwatsa wasu masu zanga-zanga a shataletalen Wurukum.

Masu zanga-zangar sun fara taruwa da misalin ƙarfe 9:30 na safe domin nuna fushinsu kan kisan mutane sama da 100 a garin Yelewata da ke Ƙaramar Hukumar Guma, a ranar Asabar.

Takarar Tinubu: Rikici ya ɓarke a APC bayan Ganduje ya ƙi goyon bayan Shettima HOTUNA: Yadda aka yi sulhu da ƙasurgumin ɗan fashin daji Ado Aliero a Katsina

Tun kafin fara zanga-zangar, jami’an tsaro daga hukumomi daban-daban sun mamaye manyan hanyoyi a birnin Makurdi.

Da safiyar ranar Lahadi da misalin ƙarfe 7 na safe jami’an tsaro, ciki har da motar yaƙi ta ‘yan sanda sun yi wa wajen tsinke.

An kuma hango sojoji a gadar kusa da wajen, yayin da jami’an NDLEA, NSCDC da sauran hukumomi suka kasance ɗauke da manyan makamai.

Rahotanni sun nuna cewa wannan matakin tsaro an ɗauke shi ne don hana zanga-zangar, amma da mutane suka fara taruwa, ‘yan sanda sun harba barkonon tsohuwa da misalin ƙarfe 11 na safe domin tarwatsa su.

Duk da haka, masu zanga-zangar ba su karaya ba, yayin da wani shahararren mai fafutuka a kafafen sada zumunta, VeryDarkMan, ya jagoranci zanga-zangar.

Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, Ifeanyi Enemari, ya isa wajen zanga-zangar sannan ya roƙi matasan da ke zanga-zangar da su zauna lafiya.

Ya ce jami’an tsaro na bakin ƙoƙarinsu don kawo ƙarshen kashe-kashen da ke faruwa a jihar.

Ya bayyana cewa Sufeto Janar na ’Yan Sanda ya tura rundunoni na musamman zuwa jihar domin taimakawa wajen tsaro, kuma wasu daga cikinsu sun isa jihar, sauran kuma na hanya.

Kwamishinan ya ce gwamnati ta bai wa jami’an tsaro goyon baya sosai kuma an riga an kama wasu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC
  • Harin Benuwe: ’Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga
  • Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki
  • DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
  • Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa
  • Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya
  • Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Bukatar Kara Yawan Masu Fitowa Kada Kuri’a A Zabuka Nan Gaba