Leadership News Hausa:
2025-07-31@22:29:09 GMT

Malamai Suna Takara Da ’Yan Siyasa Wajen Neman Mulki –Sule Lamido

Published: 21st, February 2025 GMT

Malamai Suna Takara Da ’Yan Siyasa Wajen Neman Mulki –Sule Lamido

Idan za a iya tunawa dai, malaman addini sun taka rawa wajen zaburar da jama’arsu domin yin rajistar masu zabe. Duk da haka, a babban zaben 2023 wanda yana daya daga cikin mafi zaben da ya janyo rarrabuwar kawuna a Nijeriya, masallatai da coci-coci sun taka rawar gani wajen tursasa mabiyansu su zabi nasu ‘yan takara.

Mafi yawancin wa’azi da khudubobi sun kasance wurin tattauna harkokin siyasa. A wasu majami’u, fastoci sun yi da’awar manzancin kan ‘yan takararsu, yayin da a cikin malaman addinin musulmi, limamai sun bukaci mabiya da su yi zabe ta hanyar addini. Abin mamaki, yawancin wadannan hasashen addini ba su tabbata ba.

A kwann nan dai an tafka cece-kuce kan taron da aka shirya gudanarwa a ranar 22 ga watan Fabrairun 2025 a Abuja, wanda ake sa ran za a hada mahardata alkur’ani har 30,000. An dage taron ne ba tare da saka wani lokaci ba, sakamakon kalubalantar lamarin da wasu malaman addinin Islama suka nuna, inda suka nuna shakku kan sahihancinsa tare da zargin cewa wani yunkuri ne na siyasa gabanin zaben shugaban kasa na 2027.

Idn za a iya tunawa dai, tikitin tsayawa takarar shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu na Musulmi-musulmi a shekarar 2023, wanda kusan ya wargaje tsarin fagen siyasa, a karshe ya tsira saboda gagarumin goyon baya daga malaman addini da suka tabbatar wa mabiyansu. Shi ma kabilanci da bangarenci, musamman a kudu maso yamma ya taka rawar gani.

A lokacin zaben 2023, abokan Tinubu a arewacin Nijeriya sun yi zawarcin manyan malaman ddinin Musulunci, inda suka samu goyon bayansu. Yanzu, da alama ana ci gaba da yin irin wannan kokarin, yayin da ‘yan wasan siyasa suka fara dabarun lashe zabe a 2027.

A daya hannun kuma, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi, ana kyautata zaton zai sake dauko abokin takararsa daga yankin arewacin kasar da galibinsu musulmai ne a zabe mai zuwa. Kasancewarsa yana halartar tarukan da suka shafi addinin Musulunci, ana kallonsa a matsayin wanda yake kokari wajen jawo hankalin malaman addini domin samun nasara.

Magoya bayan Obi sun ce baya ga zargin tafka magudin zaben da kuma gazawarsa wajen shigar da shugabannin addini a arewacin kasar ya taimaka matuka gaya wajen rashin nasararsa a 2023. Yayin da zaben 2027 ke gabatowa, da alama magoya bayansa sun kudiri aniyar kauce wa kuskuren da suka yi a zaben da ya gabata.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Siyasa takara

এছাড়াও পড়ুন:

Za a fara yi wa ɗaliban jami’o’i gwajin ƙwaya — Gwamnatin Nijeriya

Gwamnatin Nijeriya ta bayanna cewa za ta soma yi wa ɗaliban jami’o’in ƙasar nan gwajin miyagun ƙwayoyi a wani mataki na daƙile yaɗuwar ta’ammali da ƙwayoyin.

Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya NAN ya ruwaito cewa, Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya tare da haɗin gwiwar Hukumar Yaƙi da Fataucin Miyagun Kwayoyi NDLEA ne za su jagoranci aikin.

Sarkin Gudi na Jihar Yobe, Isa Bunuwo Ibn Khaji ya rasu Gwamnatin Jigawa ta horas da malamai 20,000 fasahar sadarwar zamani

Hakan na zuwa ne bayan ganawar Shugaban Hukumar NDLEA, Birgediya Janar Buba Marwa mai ritaya da kuma ministan ilimin ƙasar, Olatunji Alausa a jiya Laraba.

Ɓangarorin biyu sun kuma amince da ɓullo da daftarin koyar da darasin ilimin ta’ammali da ƙwayoyi a makarantun sakandiren ƙasar.

Buba Marwa wanda ya jagoranci tawagar jagororin hukumar NDLEA ya bayyana cewa gwajin ƙwayar zai shafi duk ɗaliban jami’o’in da sabbin da za su shiga.

Yayin da yake jawabi a wajen ganawar, Buba Marwa ya ce za su mayar da hankali ne kan makarantun ƙasar, waɗanda ya ce akwai miliyoyin yara da ke ƙarƙashin kulawar ma’aikatar ilimin ƙasar.

Buba Marwa ya ce rashin daƙile ta’ammali da miyagun ƙwayoyi daga wajen ƙananan yara ya taimaka wajen jefa matasan ƙasar cikin ayyukan ta’addanci da fashin daji da sauran miyagun laifuka.

Ya bayyana mummunan tasirin shan miyagun ƙwayoyi a kan matasan ƙasar, yana mai cewa yaƙi da miyagun ƙwayoyi yaki ne don ceton rayukan matasan Nijeriya.

Marwa ya ce a yanzu hankalin hukumar zai fi karkata ne zuwa makarantu da cibiyoyin ilimi, yana mai ƙarawa da cewa akwai miliyoyin yaran Nijeriya da ke ƙarƙashin kulawar ma’aikatar ilimi, kuma wannan abu ne mai matuƙar muhimmanci.

Shugaban hukumar ta NDLEAn ya ce a dalilin goyon bayan da suka samu karkashin Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu a tsawon shekaru biyu da suka gabata, hukumar ta kama mutane 40,887 da ake zargi da aikata laifuka, ta daure 8,682, kuma ta kwace tan 5,507 na miyagun ƙwayoyi.

A cewarsa, tun daga watan Janairu bara, an ƙwace ƙwayar tramadol da ta wuce ƙwaya biliyan ɗaya, wanda kudinta ya fi naira tiriliyan ɗaya.

Shugaban NDLEA ya jaddada cewa Shugaba Tinubu yana kuma tallafa wa hukumar wajen gina cibiyoyi bakwai na gyaran masu fama da shan miyagun ƙwayoyi, baya ga sauran cibiyoyi 30 da ke karkashin umarnin NDLEA a faɗin ƙasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za a fara yi wa ɗaliban jami’o’i gwajin ƙwaya — Gwamnatin Nijeriya
  • Sarkin Gudi na Jihar Yobe, Isa Bunuwo Ibn Khaji ya rasu
  • Gwamnatin Jigawa ta horas da malamai 20,000 fasahar sadarwar zamani
  • Kassim: Duk Wanda Yake Neman Hizbullah Ta Ajiye Makamanta Yana Yi Wa Isra’ila Aiki
  • An Yaba Da Kwazon Shugaba Bola Ahmad Tinubu
  • Wasu ’yan siyasa na sukar Tinubu saboda ɗan Kudu ne — Onanuga
  • Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana
  • Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu
  • Shugaban SUBEB Yayi Alkawarin Bayar Da Tallafin Ilimi A Jihar Nasarawa
  • Kasar Iran Ta Musanta Yin Katsalandan A Tattaunawar Neman Tsagaita Bude Wuta A Gaza