Shirin Rigakafin Cututtuka Na UNICEF/GAVI Ya Sami Cikakken Hadin Kan Gwamnatin Jihar Jigawa
Published: 21st, February 2025 GMT
Gwamnatin jihar Jigawa ta yi alkawarin ci gaba da gudanar da ayyukan kiwon lafiya da aka gudanar karkashin hadin gwiwarta da Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF), da shirin samar da rigakafin cututtuka a kasashe masu tasowa(GAVI) a cikin shekaru uku da suka gabata.
Haɗin gwiwar wanda aka fara shi da yarjejeniyar fahimtar juna da aka rattaba hannu a shekarar 2022, an yi shi ne don haɓaka tsarin bada lafiya na jihar, da inganta tsarin rigakafi ta hanyar samar da kayan aiki da wadatattun ma’aikatan lafiya.
A wajen mika kayan aikin da aka gudanar a gidan gwamnati dake Dutse, Gwamna Umar Namadi ya ce shirin ya bayar da gudunmawa musamman wajen samar da inshorar lafiya na musamman ga mutane sama da dubu 143 a kananan hukumomi 27 na jihar.
Namadi wanda ya samu wakilcin mataimakinsa Injiniya Aminu Usman, ya ce manufofin yarjejeniyar sun yi daidai da ajandar gwamnatin jihar 12, wanda ya bai wa fannin lafiya fifiko ta hanyar sauya cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko tun daga tushe.
Mataimakin gwamnan wanda ya karbi tawagar UNICEF/GAVI karkashin jagorancin shugaban hukumar ta UNICEF a Najeriya, Dr Shyam Sharan-Pathak, ya ce gwamnatin za ta ci gaba da bullo da tsare-tsare don bunkasa harkar kiwon lafiya a fadin jihar.
Shi ma da yake jawabi, Kwamishinan Lafiya na Jihar, Dr Muhammed Abdullahi Kainuwa, ya ce aikin ya samu gagarumar nasara a tsawon wannan lokaci.
Ya ce an samu ingantacciyar hanyar adana alluran rigakafin, ta hanyar sayen kayayyakin adana sanyi na tafi da gidanka, da na’urorin sarrafa hasken rana kai tsaye.
Hakazalika Dakta Kainuwa ya ce, an samar da motoci 3 da suka rarraba kayayyakin aiki, sannan an dauki mutane 330 aiki.
Ya yabawa shugabannin addini da na gargajiya a jihar, bisa goyon bayan da suka bayar wajen wayar da kan jama’a a tsawon shekaru 3 da aka yi aikin.
A nasa jawabin babban sakataren ma’aikatar lafiya ta jihar Dr Kabiru Ibrahim, ya yabawa gwamna Namadi bisa jajircewarsa.
Dr Kabiru, ya lura cewa, kudurin gwamnatin na bin ka’idoji da manufofin ma’aikatar lafiya ta tarayya abin yabawa ne matuka.
Shi ma da yake nasa jawabin, babban sakataren hukumar kula da lafiya matakin farko na jihar, Dokta Shehu Sambo, ya ce yarjejeniyar ta jawo sabbin dokoki da suka shafi kiwon lafiya a jihar.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, shirin karfafa tsarin kula da lafiya a matakin farko shiri ne na hadin gwiwa na tsawon shekaru 3 (wato daga shekarar2022 zuwa watan Maris na 2025) tsakanin GAVI da jihohi 8 na Najeriya wanda jihar Jigawa na daga cikinsu.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa kiwon lafiya
এছাড়াও পড়ুন:
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
An rufe taron ministocin Sin da Afirka mai tabbatar da ci gaban hadin gwiwar da aka samu a dandalin tattaunawar hadin kan Sin da Afirka wato FOCAC, wanda aka gudanar daga ranekun 10 zuwa 12 a birnin Changsha na lardin Hunan, matakin da ya bayar da sabbin damammaki ga kasashen Afirka, bisa shirin “manyan ayyuka 10 na abota tsakanin Sin da Afirka”. Sa’an nan, bayan an kammala taron, nan take, an kaddamar da bikin baje kolin kayayyaki hajojin Sin da Afirka karo na 4, duk a birnin Changsha, matakin da ya zamo daya daga cikin jerin ayyukan da ake gudanar da su don aiwatar da shirin “manyan ayyuka 10”, inda aka baje kolin ci gaban da aka samu, da tattara damammaki da albarkatu wuri guda, domin gaggauta samun ingantacciyar bunkasar hadin gwiwar Sin da Afrika a bangaren ciniki da tattalin arziki.
A cikin shekaru 25 da suka gabata, tun kafuwar FOCAC a shekarar 2000, yawan kudin kayayyakin da ake shigarwa da na fitarwa tsakanin Sin da Afirka ya karu zuwa dalar Amurka biliyan 292.4 a shekarar 2024 daga dalar biliyan 13.9 a 2000, inda adadin ya karu da fiye da ninki 20. Kana a cikin wasikar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya aika don taya murnar cimma nasarar gudanar da taron ministoci na wannan karo, Xi ya sanar da shirin yafe harajin kwastam na kaso 100% a kan kayayyakin kasashen Afirka 53, wadanda suka kulla dangantakar diflomasiyya da Sin, matakin da zai kara saukaka wa kasashen Afirka a fannin fitar da kayayyakinsu zuwa kasar Sin.
Kazalika, a farkon watanni 5 na bana, yawan kudin da Sin ta kashe wajen shigo da kayayyakin Afrika zuwa cikin kasarta ya kai dalar Amurka biliyan 50.6, adadin da ya karu da kashi 1.6% bisa na makamancin lokacin bara. Hakan ya ba kasashen Afirka damar more babbar kasuwar Sin.
Hadin gwiwar Sin da Afirka na kara habaka, duba da yadda ake aiwatar da hakikanan matakai don tabbatar da manyan tsare-tsare da aka cimma, tare da mai da hankali matuka kan amfanar da al’ummun Afirka, da inganta karfin kasashen Afirka na samun bunkasuwa bisa dogaro da kai. Ma iya cewa, hadin gwiwar bangarorin Afirka da Sin ta fuskar ciniki da tattalin arizki na cikin wani yanayi mai armashi da dorewa, duk da kalubaloli, da sauye-sauyen yanayin da ake fuskanta a duniya, abin da sa ake samun cikakken kwarin gwiwa bisa hadin gwiwar kasashe masu tasowa da bunkasar duniya baki daya. (Mai zane da rubutu:MINA)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp