Fusatattun matasa sun ƙone ofishin ’yan sanda a Ondo
Published: 17th, February 2025 GMT
Wasu fusatattun matasa sun banka wa ofishin ’yan sanda na yankin Ifon, da ke Ƙaramar Hukumar Ose wuta a Jihar Ondo.
Lamarin ya faru ne bayan da ake zargi ’yan sanda da azabtar da wani matashi har ya mutu a hannunsu.
An tsinci gawar ɗan sanda a Otal a Ogun NAFDAC ta gano wajen da ake sabunta magungunan da suka lalalce a AbiyaAna zargin al’amarin ya faru ne da yammacin ranar Asabar, amma ba a samu cikakken bayani ba sai zuwa ranar Lahadi.
Wani mazaunin Ifon, wani gari da ke iyaka da Jihar Edo, ya shaida wa Aminiya cewa mutuwar matashin ta sa al’umma da abokansa yin bore.
Wani da ya nemi a sakaya sunansa ya bayyana cewa rikicin ya samo asali ne tun a ranar masoya.
Samun labarin mutuwar matashin ke da wuya, sai matasan suka ɗunguma zuwa ofishin ’yan sanda..
Ya ce ’yan sandan sun kasa shawo kan masu boren da suka mamaye ofishin, inda suka banka masa wuta a fusace.
Da ta ke tabbatar da faruwar lamarin, kakakin rundunar ’yan sandan jihar, Funmilayo Odunlami-Omisanya, ta ce an tura ƙarin jami’an tsaro zuwa yankin.
Ta kuma ƙara da cewa Kwamishinan ’yan sandan jihar, Wilfred Afolabi, na kan hanyarsa ta zuwa Ifon domin ta tabbatar da zaman lafiya da kuma hana sake aukuwar wani tashin hankali.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi
Wani wanda ake zargi da safarar sassan jikin ɗan Adam ya shaida wa jami’an tsaro cewa ya shafe sama da shekara 10 yana sayar da sassan jikin mutum don samun kuɗi.
Dubun mutumin sun cika ne a ranar Asabar din da ta gabata inda sojoji suka kama shi a yankin Kulanla Odomoola da ke Jihar Ogun.
A furucinsa da ya amsa laifin, wanda ake zargin ya amince da sayar da sassan jikin mutum ga masu buƙata don samun kuɗin shiga.
“Na dogara ne da sayar da sassan jikin mutum tsawon shekaru 10 da suka gabata. Yawancin sassan da nake sayarwa ina tono su ne daga sabbin kaburbura a makabartu, yayin da wasu kuma nake samun su daga gawarwakin da aka watsar a gefen hanyoyi,” in ji shi.
Aminu Bayero ya naɗa Sanusi a matsayin Galadiman Kano Dukan farar hula saboda sanya kayan sojoji laifi ne — Janar Chibuisi NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”Wanda ake zargin, wanda ya amsa laifinsa ga wani taron jama’a da suka yi yunƙurin kashe shi kafin sojoji su cece shi, ana zargin yana kan hanyarsa ne na kai wani sassan jiki ga wani mai siye lokacin da aka kama shi.
Daga nan aka miƙa wanda ake zargin ga ’yan sanda a yankin Noforija don ƙarin bincike da kuma gurfanar da shi a gaban kotu.
Laftanar Kanar Olabisi Olalekan Ayeni, Mataimakin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Rundunar Sojin Najeriya ta 81, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya bayan kama wanda ake zargin daga baya an miƙa shi tare da kayayyakin da aka samu a wurinsa, ga ’yan sandan Najeriya don ƙarin bincike da kuma gurfanar da shi a gaban kotu.
“Sojojin sun ceto wanda ake zargin daga wani taron jama’a da suka yi yunƙurin kashe shi,” in ji shi.