Aminiya:
2025-08-01@15:19:07 GMT

Fusatattun matasa sun ƙone ofishin ’yan sanda a Ondo

Published: 17th, February 2025 GMT

Wasu fusatattun matasa sun banka wa ofishin ’yan sanda na yankin Ifon, da ke Ƙaramar Hukumar Ose wuta a Jihar Ondo.

Lamarin ya faru ne bayan da ake zargi ’yan sanda da azabtar da wani matashi har ya mutu a hannunsu.

An tsinci gawar ɗan sanda a Otal a Ogun NAFDAC ta gano wajen da ake sabunta magungunan da suka lalalce a Abiya

Ana zargin al’amarin ya faru ne da yammacin ranar Asabar, amma ba a samu cikakken bayani ba sai zuwa ranar Lahadi.

Wani mazaunin Ifon, wani gari da ke iyaka da Jihar Edo, ya shaida wa Aminiya cewa mutuwar matashin ta sa al’umma da abokansa yin bore.

Wani da ya nemi a sakaya sunansa ya bayyana cewa rikicin ya samo asali ne tun a ranar masoya.

Samun labarin mutuwar matashin ke da wuya, sai matasan suka ɗunguma zuwa ofishin ’yan sanda..

Ya ce ’yan sandan sun kasa shawo kan masu boren da suka mamaye ofishin, inda suka banka masa wuta a fusace.

Da ta ke tabbatar da faruwar lamarin, kakakin rundunar ’yan sandan jihar, Funmilayo Odunlami-Omisanya, ta ce an tura ƙarin jami’an tsaro zuwa yankin.

Ta kuma ƙara da cewa Kwamishinan ’yan sandan jihar, Wilfred Afolabi, na kan hanyarsa ta zuwa Ifon domin ta tabbatar da zaman lafiya da kuma hana sake aukuwar wani tashin hankali.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda ’yan bindiga suka tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina

’Yan bindiga sun tarwatsa kauyuka sama da 10 da ke zagaye da ƙaramar hukumar Bakori ta jihar Katsina sannan suka mayar da sama da 6,000 ’yan gudun hijira.

Maharan dai sun rika kashe mazauna kauyukan sannan su sace wasu su yi garkuwa da su domin karɓan kuɗin fansa.

Bayanai na cewa a ’yan kwanakin nan, ’yan bindigar na cin karensu babu babbaka a inda suka tarwatsa kauyuka kamar su Guga da Kandarawa da Kakumi da kuma Monono.

Gwamnatin Tinubu ta mayar da Arewa saniyar ware – ACF DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure

Har ila yau lamarin ya shafi ƙauyukan anguwar ’Yar Dabaru da anguwar Ɗan Marka, da Sabon Gida da ƙauyan Doma da dai sauran su.

Hakan dai ya haifar da kauracewa ƙauyukan ga mazaunansu da suke da sauran numfashi inda a yanzu haka ake da ’yan gudun hijira sama da 3,500 da ke neman mafaka a cikin garin Bakori.

Kazalika, rahotanni sun kuma ce akwai wasu sama da 2,500 da ke garin Guga don neman mafaka.

’Yan gudun hijirar wadanda akasarinsu mata ne da ƙananan yara sun watsu a wurare daban daban.

Aminiya ta zagaya unguwan Kafaɗi da unguwar Ma’aru da ke Sabuwar Abuja a cikin garin na Bakori, inda wakilinmu ya tarar da cincirindon mata da ƙananan yara a rakuɓe, a gidajen ’yan uwa, wasu kuma a makarantun firamaren gwamnati da ke karamar hukumar ta Bakori.

A tattaunawar Wakilinmu da wasu daga cikin ’yan gudun hijira wadanda suka fito daga kauyaku daban-daban na jihar, sun nuna alhininsu game da yadda ’yan bindigar ke cin karensu ba babbaka a yankin.

Imrana Shafi’u wanda ’yan bindigar suka harbe shi a ƙafa har wuri biyu, wanda shi ya yi hijira ne daga kauyan Ɗan Marka, ya ce lamarin na da ban tsoro matuƙa.

A cewarsa, “Ni ma Allah ne ya sa zan rayu domin ’yan bindigan sun zaci na mutu ne.

“Domin da suka zo kanmu harbin kan mai uwa da wabi, suka yi ta yi, inda suka kashe mutane da dama.

“Ni ma dai Allah ne ya tsirar dani, domin duk wadanda nake tare da su duk an kashe su, ni kadai na tsira cikin ikon Allah,” in ji shi.

Ita kuwa Malama Marawiya wacce ta yi gudun hijira daga kauyan ’Yar Dabaru ta ce da rana tsaka ’yan bindiga suka keto cikin kauyan nasu, suka tarwatsasu sa’ilin da suka tasa ƙeyar mata sama da 10 kuma duk yawancinsu suna ɗauke da goyo suka yi cikin daji da su.

Marawiya ta kara da cewa kusan kwanakin matan 10 ke nan a hannun su kuma sun ce sai an biya kudin fansa har Naira miliyan daya da rabi kan kowanne mutum daya kafin a sake su.

Ta Kara da cewa “A da in suka dauki mutum bai wuce su ce a ba su Naira dubu ɗari biyar ba amma a wannan karon sai suka ce sai an biya har sama da naira miliyan daya da rabi ga kowanne mutum,” in ji ta.

Yusuf Usman, wanda suka yi sansani a wata makarantar Firamare ta Nadabo da ke cikin garin Bakori, ya ce kusan su ɗari uku ne suka yi gudun hijira daga kauyan Doma, cikinsu har da tsofaffi.

Ya kuma ce, “A haka muka tako da ƙafa muka yini muna tafiya tare da mata da yaran kanana har Allah ya kawo mu garin Bakori,” in ji shi.

Ya kara da cewa kusan shekara biyar kenan suna fama da wannan matsalar ta tsaro, kuma ba dare ba rana bare damina ko rani, haka ake shigowa kauyakun su ana kashe su sannan kuma a tasa ƙeyar su a tafi da su daji domin karɓan kuɗin fansa.

Shugaban kwamitin da ƙaramar hukumar Bakori ta kafa domin kula da ’yan gudun hijirar, Mallam Mamman Yaro Bakori, ya ce adadin ’yan gudun hijirar sun kai 3,500 a garin Bakori.

Ya Kara da cewa a garin Guga Kuma akwai akalla kimanin mutane 2,500 da suke gudun hijira a can.

Shugaban ya ce kuma kusan a kullum yawan su ƙaruwa yake yi, sannan suna warwatse ne a wurare daban daban a inda wasu suke zaune a gidajen ‘yan uwansu wasu kuma suna zaune ne a makarantar firamare ta Nadabo a cikin garin Bakori.

Sai dai ya ce tuni Shugaban ƙaramar hukumar Bakori, Abubakar Barde ya bayar da umurnin kai masu tallafin kayan abinci sau uku a rana tare da kudin cefane don saukaka masu rayuwar da suke ciki.

Wasu na bayyana cewa a ‘yan kwanakinnan ’yan bindigar na cin karensu babu babbaka a inda suka kafa sansaninsu a dajin Guga da Kandarawa da Kakumi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Cika Alƙawurran Da Ya Ɗauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa
  • Taɓarɓarewar Tarbiyyar Matasa A Arewa: Ƙalubalen Da Ke Gaban Iyaye Da Shugabanni
  • Kare Ya Ciji Tsohon Ɗan Wasan Barcelona A Mazakuta
  • ‘Yan Sandan Niger Sun Hada ‘Yan’uwa Mutanen 35 Da Aka Ceto Da Iyalansu 
  • Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine
  • Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • Yadda ’yan bindiga suka tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina
  • Shugaban SUBEB Yayi Alkawarin Bayar Da Tallafin Ilimi A Jihar Nasarawa