Boko Haram ta kashe kwamandoji da mayaƙan ISWAP 31 a Borno
Published: 16th, February 2025 GMT
Ƙungiyar Boko Haram ta kashe kwamandoji da mayaƙan takwararta na ISWAP da dama yayin wani ƙazamin rikici da suka tafka ranar Juma’a a Ƙaramar Hukumar Kukawa da ke Jihar Borno.
Bayanai sun ce an kashe kwamandoji da mayaƙan ISWAP 31 yayin harin da mayaƙan Boko Haram suka kai ƙarƙashin jagorancin wani ta’adda mai suna Bakoura.
Wata majiya ta shaida wa ƙwararren mai sharhi kan yaƙi da tayar da ƙayar baya, Zagazola Makama, cewa yaƙin da aka fara tun da sanyin safiyar ranar 14 ga watan Fabrairu ya haɗa da sansanonin ISWAP da ke Toumbun Gini da Toumbun Ali.
Mayaƙan Boko Haram, waɗanda rahotanni suka ce sun ragargaji sansanin na ISWAP a wani ƙazamin faɗan ya ɗauki tsawon yini guda ana gwabzawa.
Majiyoyi sun tabbatar da cewa an kashe wasu manyan kwamandojin ISWAP musamman ‘yan kabilar Buduma a yayin harin.
A cewar majiyar, daga cikin ’yan ta’addan ISWAP da aka kashe sun haɗa da wasu manyan-manyan kwamandojin da ake kyautata zaton sun taka rawa wajen kisan kiyashin da aka yi wa manoma da dama a Kukawa a tsakanin 12 zuwa 13 ga watan Janairu na wannan shekara ta 2025.
Majiyar ta ce mayakan Boko Haram sun yi wa kungiyar ta ISWAP asara mai yawa bayan da suka mamaye sansaninsu, inda suka ƙwace makamai da kayan aiki.
A wani yunƙuri na faɗaɗa hare-haren nasu, an ce mayaƙan na Boko Haram daga tsibirin Bokorram sun ɗaura ɗamara domin tunkarar mayaƙan ISWAP a Gemu da Mallam Karamti.
Zagazola ya bayyana cewa akwai yiwuwar ana gab da samun ƙarin fadace-fadace, musamman a Ƙaramar Hukumar Kukawa, yayin da mayaƙan Boko Haram ke ƙara ƙaimi wajen yaƙar ISWAP.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram ISWAP jihar Borno da mayaƙan
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
Bug da kari Tinubu ya jinjina wa Shugaban jami’ar, Farfesa Wahab Olasupo Egbewole (SAN)da ‘yan tawagarsa wajen maida hankalin da suka yi na bunkasa Jami’ar da kumna kudurinta na muradun ci gaban da ake bukata.
Shi ma anashi jawabin Shugaban Jami’ar Sarkin Katsina, Alhaji. Abdulmumin Kabir Usman, wanda Wazirin Katsina, Sanata Ibrahim Idah ya wakilta, ya nuna jin dadinsa kan irin kokarin da UNILORIN saboda bunkasar ilimi da kumasamar wuraren koyon kaaratu masu kyau da kuma suka dace.
Ya yi ma kallon ayyukan da ak kaddamar a matsayin“ irin abubuwan da ake bukatar gani ke nan”da za su taimakawa lamarin koyarwa, koyo,da kuma bincike, inda ya kara da cewa yadda Jami’ar ta maida hankalinta wajen bunkasa dabarar koyon yin abubuwa zai taimakawa dalibai su tashi da sun koyi abubuwan da zasu yi baya rayuwar da suka yi cikin aji.
A nashi jawabin mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa. Egbewole ya nuna farin cikinsa da godew a Shugaban kasa Tinubu kan yadda ya amince da gaiyar da Jami’ar ta yi ma shi, da kuma taimaka mata wajen tafiyar da bunkasar abubuwan jin dadi.
“Muna nan muna sa ido saboda ci gaban samun abubwan da suke taimakawa ci gaba kwarai da gaske a kowace rana kamar yadda yace yana da amincewa da yardarm ci gaba da samun hakan’’.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA