Aminiya:
2025-06-15@13:43:08 GMT

Boko Haram ta kashe kwamandoji da mayaƙan ISWAP 31 a Borno

Published: 16th, February 2025 GMT

Ƙungiyar Boko Haram ta kashe kwamandoji da mayaƙan takwararta na ISWAP da dama yayin wani ƙazamin rikici da suka tafka ranar Juma’a a Ƙaramar Hukumar Kukawa da ke Jihar Borno.

Bayanai sun ce an kashe kwamandoji da mayaƙan ISWAP 31 yayin harin da mayaƙan Boko Haram suka kai ƙarƙashin jagorancin wani ta’adda mai suna Bakoura.

Dalilin da ’yan siyasa ke sauya sheƙa zuwa APC — Tambuwal Ɗan Nijeriya ya lashe kyautar Kundin Bajinta na Duniya a fagen ɗaukar hoto

Wata majiya ta shaida wa ƙwararren mai sharhi kan yaƙi da tayar da ƙayar baya, Zagazola Makama, cewa yaƙin da aka fara tun da sanyin safiyar ranar 14 ga watan Fabrairu ya haɗa da sansanonin ISWAP da ke Toumbun Gini da Toumbun Ali.

Mayaƙan Boko Haram, waɗanda rahotanni suka ce sun ragargaji sansanin na ISWAP  a wani ƙazamin faɗan ya ɗauki tsawon yini guda ana gwabzawa.

Majiyoyi sun tabbatar da cewa an kashe wasu manyan kwamandojin ISWAP musamman ‘yan kabilar Buduma a yayin harin.

A cewar majiyar, daga cikin ’yan ta’addan ISWAP da aka kashe sun haɗa da wasu manyan-manyan kwamandojin da ake kyautata zaton sun taka rawa wajen kisan kiyashin da aka yi wa manoma da dama a Kukawa a tsakanin 12 zuwa 13 ga watan Janairu na wannan shekara ta 2025.

Majiyar ta ce mayakan Boko Haram sun yi wa kungiyar ta ISWAP asara mai yawa bayan da suka mamaye sansaninsu, inda suka ƙwace makamai da kayan aiki.

A wani yunƙuri na faɗaɗa hare-haren nasu, an ce mayaƙan na Boko Haram daga tsibirin Bokorram sun ɗaura ɗamara domin tunkarar mayaƙan ISWAP a Gemu da Mallam Karamti.

Zagazola ya bayyana cewa akwai yiwuwar ana gab da samun ƙarin fadace-fadace, musamman a Ƙaramar Hukumar Kukawa, yayin da mayaƙan Boko Haram ke ƙara ƙaimi wajen yaƙar ISWAP.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram ISWAP jihar Borno da mayaƙan

এছাড়াও পড়ুন:

Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe

Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe, ta tabbatar da mutuwar mutum biyar da kuma jikkatar wasu 13, sakamakon tashin wutar lantarki a unguwar Tudun-Wada, Pantami a jihar.

Wutar ta tashi ne da safiyar ranar Asabar sakamakon matsala da ta taso daga wata tiransifoma a yankin, kamar yadda kakakin ’yan sandan jihar, DSP Buhari Abdullahi, ya bayyana.

Sojoji sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa

Cikin waɗanda suka rasa rayukansu har da Babban Sakatare na Ma’aikatar Ayyuka ta Musamman ta jihar, Alhaji Muhammad Yusuf Kulani, tare da ’ya’yansa da wasu mazauna unguwar.

Marigayin shi ne shugaban ƙungiyar ƙwararrun akantoci ta Jihar Gombe (ANAN).

’Yan sanda daga ofishin Low-Cost sun isa wajen don tabbatar da tsaro da kuma kai waɗanda suka jikkata zuwa asibiti.

Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, Bello Yahaya, ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan mamatan.

Ya kuma ce za su gudanar da cikakken bincike domin gano musabbabin tashin wutar da kuma ɗaukar matakan kare faruwar hakan a gaba.

Ya kuma roƙi al’umma da su kasance masu bin doka tare da bayar da haɗin kai yayin gudanar da binciken.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin
  • Harin Isra’ila a kan Iran ya jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin zama dar-dar
  • Nijeriya Ce Ta 3 A Manyan Kasashe Masu Karfin Masana’antu 10 Na Afirka
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara