Leadership News Hausa:
2025-09-17@23:26:04 GMT

Ƙudirin Ƙirƙiro Sabbin Jahohi 31 Ya Jawo Cece-kuce A Nijeriya

Published: 14th, February 2025 GMT

Ƙudirin Ƙirƙiro Sabbin Jahohi 31 Ya Jawo Cece-kuce A Nijeriya

Sannan a kudu maso kudu, masu goyon bayan sabbin jihohi suna son a samar da jihohin Ogoja, Warri, da Bori daga jihohin Kuros Ribas, Delta da Ribas, da kuma Jihar Obolo daga jihohin Ribers da Akwa Ibom na yanzu.

Daga kudu maso yamma kuwa, akwai shawarwarin samar da sabbin jihohi shida. Jihohin da ake shirin kirkira sun hada da Toru-ebe da za a sassaka daga jihohin Delta da Edo da Ondo na yanzu, da kuma jihohin Ibadan da Lagoon da za a sassaka daga jihohin Oyo da Legas, bi da bi.

Sauran sun hada da Jihar Ijebu da za a samar daga Jihar Ogun ta yanzu da kuma jihohin Oke-Ogun da Ife-Ijesha da za a kirkiro daga jihohin Ogu da Oyo da Osun na yanzu.

Kwamitin majalisar kan sake fasalin kundin tsarin mulkin kasar nan, a wata sanarwa da ya aike wa mambobin majalisar wakilai, mai dauke da sa hannun mataimakin shugaban majalisar wakilai, Benjamin Kalu, wanda kuma shi ne shugaban kwamitin, ya umurci masu goyon bayan kirkiro sabbin jihohin da su sake gabatar da bukatarsu kamar yadda sashe na 8 (1) na kundin tsarin mulkin 1999 ya tanada.

“Kwamitin ya duba shawarwarin samar da sabbin jihohi kamar yadda sashe na 8(1) na kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya na shekarar 1999 ya tanada. Wannan sashe ya zayyana takamaiman bukatu wadanda dole ne a cika su don fara aikin kirkirar sabbin jihohi. Za a sake gabatar da shawarwari bisa la’akari da wadannan sharudda,” in ji Kalu.

Wasu ‘yan Nijeriya dai sun soki matakin, suna masu cewa abin da ya kamata shugabanni su mayar da hankali a kai shi ne, yadda za a mayar da kasar mulkin yanki ba wai samar da karin jihohi ba.

Masu yada wannan labari na ganin cewa Nijeriya ta fi samun shugabanci nagari a lokacin da ake tsarin milkin yankuna, lura da cewa samar da jihohi 12 daga yankuna hudu da gwamnatin mulkin soja ta Janar Yakubu Gowon ta yi ba don wani ci gaba ba ne, sai dai wani yunkuri ne na raunana yankin gabas a lokacin yakin Biafara.

Amma, akwai wadanda kuma suka yi jayayya cewa samar da jihohi yana kawo ci gaba ga mutanen da ke ganin an ware su kuma za su yi maraba da shawarwarin muddin sun bi ka’idojin kamar yadda ‘yan majalisar suka sake nanata a baya.

Haka kuma, akwai wasu da ba su yarda da samar da karin jihohi a Nijeriya gaba daya ba, amma suna da ra’ayin cewa a yi adalci a kara wa yankin kudu maso gabas karin jiha daya domin daidaita yankin da takwarorinsa.

kungiyoyin yankin biyu da suka yi kaurin suna wajen nuna adawa da matakin sun hada da kungiyar kabilar Yarbawa ta Afenifere da kuma kungiyar tuntuba ta Arewa (ACF). Dukkan bangarorin biyu sun bayyana shirin samar da jihar a matsayin abin dariya kuma ba amshesshe ba ne.

Sai dai kungiyar ta Afenifere ta bukaci majalisar dokokin kasar da ta mayar da hankali kan sauye-sauyen kundin tsarin mulkin kasar da zai raba madafun iko, da maido da albarkatun kasa a yankunan, da kuma bai wa jihohi ‘yancin cin gashin kansu domin su bunkasa cikin hanzari.

Haka zalika, kungiyar tuntuba ta Arewa, ta kuma bayyana rashin amincewarta da shirin samar da sabbin jihohi 31, inda ta bayyana ra’ayin a matsayin wanda bai kamata ba.

Amma, babbar kungiyar kare al’adun Igbo, Ohanaeze Ndigbo ta bi wata hanya ta daban. Tana da ra’ayin cewa a kara wa yankin kudu maso gabas sabbin jihohi domin magance kura-kuran da aka yi wa yankin dangane da batun samar da jihohi.

A nasa bangaren, Babban Lauyan Nijeriya kuma Farfesa a fannin shari’a, Cif Mike Ozekhome, ya bayyana hakan a matsayin almubazzaranci.

Shima da yake magana game da damuwar da ‘yan Nijeriya da dama ke da shi dangane da yadda ake tada zaune tsaye na samar da sabbin jihohi, Mista Osita Okechukwu, tsohon Darakta Janar na Muryar Nijeriya ya yaba da matakin a matsayin kyakkyawan misali ga hadin kan kasa.

Najeeb Bello ya kasa boye bacin ransa game da lmarin, inda ya ce, “Me zai hana smar da jihohi 311? A bari kowace karamar hukuma a Nijeriya ta zama jiha kawai.”

Bashir Ahmad yana goyan bayan samar da sabbin jihohi, amma ya bayar da shawara a kara karkasa Jihar Kano duba da yawan al’ummar da take da shi.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: samar da sabbin jihohi kundin tsarin mulkin samar da jihohi

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi

Wasu mutum shida sun shiga hannun ’yan sanda kan zargin satar zinari da kuɗinta ya haura Naira miliyan 109.5 a Jihar Kebbi.

Sashen binciken manyan laifuka na rundunar ’yan sanda a jihar Kebbi na tuhumar su da sace sarkoƙin zinare guda biyar sauran kayan zinare daga wani gida a garin Ka’oje, Ƙaramar Hukumar Bagudo.

Sauran sun haɗa da zobba huɗu da munduwar hannu tara, da nauyinsu ya kai gram 782.7 — dukkansu mallakar ’ya’ya da ’yan uwar mai gidan.

Wanda ake tuhuma ya amsa laifi

Bayan samun koken, jami’an suka kama Ibrahim Abubakar Ka’oje, jami’i a Hukumar Gyaran Hali ta Kasa, wanda a yayin bincike, ya amsa laifin.

’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu

Ya bayyana cewa ya sayar da kayan ga wasu mutane biyu, dukkansu daga Sakkwato, tare da wasu mutum biyu a Jihar Kebbi.

An kuma gano wanda  ya taimaka masa wajen sayar da wasu daga cikin kayan, inda ya karɓi naira miliyan 2.5 a matsayin lada.

Rundunar ’yan sanda ta bayyana cewa har yanzu tana neman sauran da suka gudu, bisa zargin taimakawa wajen sayar da kayan sata.

Ana zargin an sayi filaye biyu a Birnin Kebbi da kuɗin da aka samu daga sayar da kayan.

Abubuwan da aka ƙwato

Kayan da aka ƙwato sun haɗa da munduwar hannu biyu, babur ɗin Haouje, da kuma wayoyin iPhone 16, Samsung Galaxy Ultra da Samsung Flip.

Kwamishinan ’yan sanda na Jihar Kebbi, Bello M. Sani, ya jinjina wa jajircewar jami’ansa bisa wannan nasara.

Ya kuma yi kira gare su da su ci gaba da aiki tukuru domin cafke sauran da ake nema da kuma ƙwato dukkan kayan da suka rage.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • NECO ta saki sakamakon jarabawar 2025
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki Guda 5 A Wajen Taron Kolin kere-kere .
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara