Aminiya:
2025-05-01@04:36:20 GMT

Malaman Firamare sun sake tsunduma yajin aiki kan rashin albashi a Abuja

Published: 13th, February 2025 GMT

Ƙungiyar Malaman Makarantu ta Ƙasa (NUT) da Ƙungiyar Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi ta Ƙasa (NULGE), sun umarci malaman makarantun firamare da ke ƙarƙashin Sashen Ilimin Ƙananan Hukumomi (LEA) da su sake tsunduma yajin aiki.

Haka kuma an umarci ma’aikatan ƙananan hukumomi shida na Babban Birnin Tarayya, da su dakatar da aiki daga ranar Alhamis, 13 ga watan Fabrairu, 2025, sakamakon rashin biyan mafi ƙarancin albashin Naira 70,000 da shugabannin ƙananan hukumomi suka yi.

An yanke hukuncin sare hannun matashi kan sare hannun yaro a Gombe Ba zan daina sukar gwamnatin Tinubu ba — Farfesa Yusuf

Shugaban Ƙungiyar NUT reshen Abuja, Kwamared Mohammed Shafas, ya bayyana cewa ƙungiyoyin sun yanke shawarar sake komawa yajin aikin ne saboda gazawar shugabannin ƙananan hukumomi shida wajen aiwatar da mafi ƙarancin albashi.

Ya tunatar da cewa malaman firamare da ma’aikatan ƙananan hukumomi sun dakatar da yajin aiki a ranar 12 ga watan Disamban 2024 ne, bayan da aka sanya hannu kan yarjejeniya tsakanin ƙungiyoyin ƙwadago da shugabannin ƙananan hukumomi.

Ya ce an yi yarjejeniyar ne domin fara aiwatar da biyan albashin Naira 70,000 daga watan Janairun 2025.

Sai dai, duk da hakan, shugabannin ƙananan hukumomin sun yi watsi da yarjejeniyar.

Kwamared Shafas, ya ƙara da cewa ba wai rashin aiwatar da mafi ƙarancin albashin ne kaɗai ya jawo yajin aikin ba, har da gazawar shugabannin wajen biyan wasu haƙƙoƙin ma’aikata.

Ya ce buƙatun da ba a biya ba sun haɗa da kashi 40 na alawus-alawus, ƙarin albashi na kashi 25 da 35.

Ya ce, sai an biya waɗannan haƙƙoƙi kafin malaman firamare da ma’aikatan ƙananan hukumomi su koma bakin aiki a Abuja.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ma aikatan Ƙananan Hukumomi malaman firamare

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya ta ayyana hutu gobe Alhamis

Gwamnatin Nijeriya ta ayyana gobe Alhamis 1 ga watan Mayu a matsayin ranar hutu ga ma’aikatan ƙasar albarkacin bikin murnar Ranar Ma’aikata ta Duniya.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da Ministan Harkokin Cikin Gida na ƙasar, Olubunmi Tunji-Ojo, ya fitar a yammacin wannan Larabar.

AU ta janye takunkumin da ta ƙaƙaba wa Gabon Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu

Sanarwar ta ambato ministan yana yaba wa ma’aikatan ƙasar kan sadaukarwa da jajircewar da suke yi wajen gudanar da ayyukansu.

Ministan ya kuma yaba musu kan gudunmawar da suke bayarwa wajen ciyar da Nijeriya gaba.

Ana dai gudanar da bikin Ranar Ma’aikata a ranar 1 ga watan Mayun kowace shekara a sassan duniya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya ta ayyana hutu gobe Alhamis
  • Iran ta sha alwashin ci gaba da aiwatar da manufofinta na raya dangantakarta da Nijar
  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu
  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  •  Manyan Malaman Roman Katolika Sun Fara Taron Zabar Paparoma
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Shirya Fara Tantance ‘Yan Fansho
  • Sin Za Ta Aiwatar Da Matakan Daidaita Samar Da Guraben Ayyukan Yi Da Raya Tattalin Arziki
  • Ma’aikata 240 na karɓar albashi biyu, wasu 217 na amfani da lambar BVN ɗaya a Kano
  • Iran Da Rasha Sun Jaddada Yin Aiki Tare A Fagen Kiwon Lafiya