Ƙungiyar malamai ta NUT-FCT da ma’aikatan ƙananan hukumomi na NULGE sun fara yajin aiki na dindin a yau Alhamis, sakamakon gazawar shugabannin ƙananan hukumomi wajen aiwatar da sabon albashi mafi ƙarancin na ₦70,000 da aka amince da shi tun Disamba 2024.

Ƙungiyoyin sun koka cewa duk da cewa sauran ma’aikatan FCT sun fara karɓar sabon albashin, an bar malaman firamare da ma’aikatan ƙananan hukumomi a baya.

Sun ce sun ba shugabannin isasshen lokaci domin su cika alƙawarin da suka ɗauka amma sun kasa, don haka suka yanke shawarar ci gaba da yajin aiki har sai an biya su hakkokinsu.

Yadda Jami’an Tsaro Suka Fara Gyara Wa ‘Yan Jari Bola Zama A Abuja… Hukumar FCTA Ta Rufe Asibitin Da Ke Aiki Ba Bisa Ka’ida Ba A Kuje

A sakamakon yajin aikin, an rufe makarantu a sassa daban-daban na FCT, inda malamai suka sallami ɗalibai. Wata malama, Mrs. Ene Igado, ta ce malaman firamare na L.E.A ana yi musu babbar wariya idan aka kwatanta da takwarorinsu na UBEB, duk da cewa su ne ke yin mafi yawan aiki.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Harin Kan Cibiyar Makamashin Nukiliya Cin Amanar Diflomasiyya Ce

Ministan harkokin wajen Iran ya jaddada cewa: Hare-haren da Amurka ta kai kan cibiyoyin nukiliyar Iran cin amanar diflomasiyya ce

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana harin da sojojin Amurka suka kai kan cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran na zaman lafiya a matsayin cin amanar diflomasiyya da kuma cewa wani mataki ne da ba a taba ganin irinsa ba ga tsarin doka da hakkin kasa da kasa da kuma tsarin hana yaduwar makaman nukiliya.

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi da Ronald Lamola, ministan hulda da kasa da kasa da hadin gwiwa na Jamhuriyar Afirka ta Kudu, sun tattauna batutuwan baya-bayan nan da ke faruwa a yankin Gabas ta Tsakiya bayan dakatar da hare-haren soji da yahudawan sahayoniyya da Amurka suka yi kan Iran a wata tattaunawa ta wayar tarho a ranar Laraba.

Araqchi ya bayyana jin dadinsa ga matsayin Afrika ta Kudu wajen yin Allah wadai da zaluncin sojin gwamnatin ‘yan sahayoniyya masu nuna wariyar al’umma suka dauka na kai wa kasar Iran hari, yana mai cewa: Hare-haren wuce gona da iri da gwamnatin ‘yan sahayoniyya ta dauka a kan Iran, sakamakon rashin hukunta ta ce da kuma gazawar kasashen duniya wajen mayar da martani kan laifukan da take aikatawa a Gaza da kuma hare-haren da take kai wa Lebanon da Siriya, kuma tabbas dukkanin masu goya mata baya suna da hannu wajen aikata laifukan da take aikatawa.

Ya yi nuni da cewa: Harin da sojojin yahudawan sahayoniyya suka kai wa Iran ya faru ne a cikin shawarwari da kuma goyon bayan gami da taimakon Amurka. Daga nan ne Amurka ta kaddamar da harin soji kan cibiyoyin nukiliyar Iran na zaman lafiya, tare da jaddada cewa matakin da Amurka ta dauka ya zama cin amanar diflomasiyya da kuma wani matakin da ba a taba ganin irinsa ba na rashin bin doka da oda, da take hakkin kasa da kasa, da kuma tsarin hana yaduwar makaman nukiliya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja
  • Kotu ta umarci a mayar da Sanata Natasha majalisa
  • Kotu ta ci tarar Natasha N5m saboda kin bin umarninta
  • ’Ya’yana na da ’yancin mallakar filaye a Abuja – Wike
  • Jalali: Mun  Hana Fitowar Sanadarorin Nukiliya Ta Hanyar Aiki Da Ka’idojin Tsaro
  • Majalisar Jigawa Ta Isa Roni A Ci Gaba Da Rangadin Kananan Hukumomi
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Harin Kan Cibiyar Makamashin Nukiliya Cin Amanar Diflomasiyya Ce
  • ’Yansanda Sun Ceto Ɗan Ghana, Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 3
  • Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar
  • An Hori Ma’aikatan Lafiya Su Kara Kokari Wajen Rike Aikin su