Aminiya:
2025-11-03@08:13:38 GMT

N50,000 aka biya ni don safara harsasai zuwa Abuja – Matashj

Published: 12th, February 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Filato, ta kama wani matashi tare da wasu mutum uku kan zargin safarar harsasai daga Jos zuwa Abuja.

Matashin ya bayyana cewa ’yan ta’adda sun biya shi Naira 50,000 domin ya karɓo harsasai daga Jos zuwa Abuja.

Majalisa na neman rushe ƙudirin ƙara kuɗin kira da data Noman rani ne zai kawar da yunwa a Yankin Tafkin Chadi — Zulum

“Ni mazaunin Abuja ne.

Makonni biyu da suka wuce, wani mutum ya aike ni domin karɓo masa harsasai a Jos zuwa Abuja.

“Ya tabbatar min babu wata matsala da zan fuskanta, amma a hanya jami’an tsaro suka kama mu ni da wasu mutum uku,” in ji matashin.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, yayin da yake holen waɗanda ake zargi, ya ce an kama su ne bayan samun rahoton sirri kan ayyukansu.

“Mun kama waɗanda ake zargin ne bayan samun sahihan bayanan sirri.

“Rundunar na ci gaba da bincike, kuma da zarar an kammala, za a miƙa su zuwa kotu domin fuskantar hukunci.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Harsasai Masu Safarar Makamai matsalar matsalar tsaro Safara

এছাড়াও পড়ুন:

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

A 2022, kasashe shida ne suka daina yanke hukuncin kisa, ko dai gaba daya ko kuma wani bangare.

Hudu daga cikinsu; Kazakhstan, Papua New Guinea, Saliyo, Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, sun jingine shi kwatakwata.

Ekuatorial Guinea da Zambia sun ce za a rika amfani da shi ne kawai kan laifuka mafiya kololuwar muni.

A watan Afrilun 2023, majalisar dokokin Malaysia ta kada kuri’ar daina amfani da shi a matsayin tilas kan laifuka 11, ciki har da kisa da kuma ta’addanci.

Majalisar dokokin Ghana ma ta kada kuri’ar soke hukuncin kisa a watan Yulin 2023.

 

Wadanne kasashe ne suka fi yanke hukuncin kisa?

Kasashe 20 ne suka zartar da hukunbcin kisa a 2022, idan aka kwatanta da 18 da suka yi hakan a 2021.

Kungiyar kare hakki ta Amnesty International ta ce jimillar mutum 1,518 aka zartar wa hukuncin kisa a duniya, inda aka samu karin kashi 32 cikin 100. Sai dai ta ce hakikanin adadin ya zarta haka sosai saboda yadda kasashe ke boye batun.

Bayan China, Amnesty ta ce kasashen da suka fi kashe mutane a 2024 su ne Iran (972), da Saudiyya (345), da kuma Iraki (63). Su ne suka zartar da kashi 91 cikin 100 na duka kasashen duniya.

Ana yi wa China kallon kasar da ta zarta kowacce aiwatar da hukuncin kisa a duniya, amma ba a sanin hakikanin adadin mutanen, saboda gwamnati ba ta bayyana su.

Kasashen Koriya ta Arewa da Bietnam ma na amfani da hukuncin kisa sosai amma ba su bayyanawa a hukumance.

Amnesty ta ce ta samu rahoton zartar da hukuncin kisa a bainar jama’a akalla sau uku a 2022 a Iran.

Ta ce Iran din ta kashe akalla mutum biyar saboda laifukan da suka aikata a lokacin da suke kasa da shekara 18 da haihuwa.

Saudiyya ta kashe mutane mafiya yawa a duniya a 2022 cikin shekara 30.

Kasashe biyar; Bahrain, Comoros, Laos, Nijar, Koriya ta Kudu – su ne suka yanke wa mutane hukuncin kisa a 2022 bayan sun shafe tsawon lokaci ba su yi amfani da shi ba.

Duk da cewa adadin na raguwa a Amurka, amma ya karu a 2021, amma duk da haka ya yi kasa sosai idan aka kwatanta da shekarar 1999.

 

Mutum nawa aka kashe saboda safarar miyagun kwayoyi?

Amnesty International ta ce sama da kashi 40 cikin 100 na mutanen da aka zartar wa hukuncin kisa a 2024 saboda laifukan ta’ammali da miyagun kwayoyi ne.

A 2022, an kashe mutum 325 saboda laifukan da suka shafi miyagun kwayoyi. Kasashen da suka aikata hakan su ne:Iran 255 Saudiyya – 57 – Singapore – 11

A 2023, Singapore ta zartar da hukuncin kisa kan mace ta farko cikin shekara 20. A 2018 aka kama Saridewi Djaman da laifin safarar hodar ibilis.

 

Ta yaya kasashe ke zartar da hukuncin kisa?

Saudiyya ce kadai ta zayyana fille kai a matsayin hanyar aiwatar da hukuncin kisa a 2022.

Sauran hanyoyin sun hada da rataya, da allura mai guba, da kuma harbi da bindiga.

A watan Janairun 2024 jihar Alabama ta Amurka ta zartar wa wani mai laifin kisa Kenneth Smith hukuncin kisa ta hanyar amfani da iskar nitrogen gas.

Ya zama mutum na farko a duniya da aka zartar wa hukuncin ta irin wannan hanyar, a cewar cibiyar Death Penalty Information Center da ke Amurka.

Lauyoyin Mista Smiths sun ce salon da ba a taba gwadawa ba kafinsa “rashin imani ne”.

Alabama da wasu jihohin Amurka biyu ne suka amince da amfani da iskar gas din saboda kwayoyin da ake amfani da su wajen yi wa mutum allura mai guba ba sa samuwa cikin sauki.

 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su November 2, 2025 Manyan Labarai Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya November 2, 2025 Manyan Labarai Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka November 2, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matar aure ta yanka wuyan mijinta, ta fasa masa ido da wuƙa a Neja
  • Yadda matata ta ɓace a Abuja aka tsince ta a Sakkwato
  • Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare