Hukumar Sauraran Korafe-Korafe Ta Jigawa Za Ta Kulla Alaka Da Takwararta Ta Abuja
Published: 10th, February 2025 GMT
A kokarinta na karfafa hadin gwiwa da tabbatar da gaskiya da rikon amana, hukumar korafe-korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Jigawa (JG-PCACC) ta kai ziyarar ban girma ga takwararta da ke Abuja.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban sashen hulda da jama’a na JG-PCACC Alhaji Yusuf Suleiman ya bai wa gidan rediyon Najeriya a birnin Dutse na jihar Jigawa.
A cewarsa, sun kai ziyarar ce karkashin jagorancin shugaban PCACC, Barista Salisu Abdu, da zummar tantancewa da kuma cudanya da masu ruwa da tsaki a hukumar, tare da lalubo hanyoyin hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu.
Barista Salisu Abdu ya jaddada mahimmancin hadin gwiwar t domin hana cin zarafi da rashin adalci a hukumomi da cibiyoyin gwamnati.
“Mun yi imanin cewa ta hanyar yin aiki tare, za mu iya samun ci gaba da samar da ingantacciyar al’umma.
“Ziyarar da muka kawo a yau wata shaida ce da ke nuna aniyarmu ta hada kai da kuma kawar da jihar Jigawa daga kowane irin zalunci.
Barista Abdu ya kuma shaida wa babban kwamishinan cewa hukumarsa na son yin amfani da kwarewar hukumar korafe-korafen jama’a ta fannin horar da ma’aikata.
“Muna da tabbacin hukumarku za ta iya taimaka mana da shawarwari, da horarwa da goyon baya kan mafi kyawun ayyuka wajen tafiyar da koke-koken jama’a duba da nasarorin da kuka samu tsawon shekaru.” In ji Barr. Abdu.
Shugaban ya kuma bayyana cewa JG-PCACC na da ayyuka guda biyu da suka hada da sauraran korafe-korafen jama’a da kuma yaki da cin hanci da rashawa, inda ya ce tun farko hukumar ta karbi korafe-korafe sama da 150 tare da warware su cikin ruwan sanyi.
“Muna da tasiri sosai a fannin korafe-korafen jama’a, tun daga farko mun samu kararraki sama da 150 da suka hada da batutuwan aure, daGado, da karbo basussuka, da takaddamar ciniki, da dai sauransu, kuma da dama daga cikinsu an warwaresu.” In ji shugaban na JGPCACC.
A nasa jawabin, shugaban hukumar kula da korafe-korafen jama’a da ke Abuja (PCC), Bashir Abubakar ya bayyanawa jami’an hukumar korafe-korafen jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Jigawa irin tasirin da hukumarsa ta ke bi wajen magance rikice-rikice.
“Jihar Jigawa na daya daga cikin jihohin da suka fi zaman lafiya amma za ku iya taimakawa jihar wajen samun nasara idan kun yi amfani da fasahar sadarwa ta zamani wajen kawo korafe-korafe cikin sauki,” inji shi.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa korafe korafen jama a korafe korafe jihar Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha
Ministan harkokin wajen Iran ya gana da takwarorinsa na Qatar, Turkiyya, Pakistan da Lebanon a Doha fadar mulkin kasar Qatar
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya gana da takwaransa na Qatar a gefen taron ministocin harkokin wajen kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC a birnin Doha.
Doha ta sanar da cewa, fira ministan kasar Qatar kuma ministan harkokin wajen kasar ya yi nazari kan al’amuran yankin na baya-bayan nan yayin ganawarsa da ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi.
A yayin wannan taro, harin da yahudawan sahayoniyya suka kaddamar a birnin Doha shi ne babban abin da ake tattaunawa akai.
Araqchi yayi Allah wadai da harin da gwamnatin mamayar Isra’ila ta kai, yana mai tabbatar da goyon bayan Jamhuriyar Musulunci ta Iran da kuma goyon bayan gwamnati ga al’ummar Qatar.
A cikin wannan yanayi, Araqchi ya gana tare da tuntubar ministan harkokin wajen Turkiyya Hakan Fidan da ministan harkokin wajen Pakistan Muhammad Ishaq Dar a gefen taron kasa da kasa a birnin Doha.
An gudanar da wadannan tarukan ne domin karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu da kuma tattauna batutuwan da suka shafi yankin.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA September 15, 2025 Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar September 15, 2025 Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000 September 15, 2025 Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces September 15, 2025 Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar September 15, 2025 Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila September 15, 2025 Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa September 15, 2025 Sudan ta soki takunkuman da Amurka ta kakaba mata September 15, 2025 Dakarun Sojin Yamen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ramon Na Isra’ila. September 14, 2025 Isra’ila Za ta Gamu Da Mummunar Martani Idan Tayi Gigin Afkawa Iran September 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci