A kokarinta na karfafa hadin gwiwa da tabbatar da gaskiya da rikon amana, hukumar korafe-korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Jigawa (JG-PCACC) ta kai ziyarar ban girma ga takwararta da ke Abuja.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban sashen hulda da jama’a na JG-PCACC Alhaji Yusuf Suleiman ya bai wa gidan rediyon Najeriya a birnin Dutse na jihar Jigawa.

A cewarsa, sun kai  ziyarar ce karkashin jagorancin shugaban PCACC, Barista Salisu Abdu,  da zummar tantancewa da kuma cudanya da masu ruwa da tsaki a hukumar, tare da lalubo hanyoyin hadin gwiwa  tsakanin bangarorin biyu.

Barista Salisu Abdu ya jaddada mahimmancin hadin gwiwar t domin hana cin zarafi da rashin adalci a hukumomi da cibiyoyin gwamnati.

“Mun yi imanin cewa ta hanyar yin aiki tare, za mu iya samun ci gaba da samar da ingantacciyar al’umma.

“Ziyarar da muka kawo a yau wata shaida ce da ke nuna aniyarmu ta hada kai da kuma kawar da jihar Jigawa daga kowane irin zalunci.

Barista Abdu ya kuma shaida wa babban kwamishinan cewa hukumarsa na son yin amfani da kwarewar hukumar korafe-korafen jama’a ta fannin horar da ma’aikata.

“Muna da tabbacin hukumarku za ta iya taimaka mana da shawarwari,  da horarwa da goyon baya kan mafi kyawun ayyuka wajen tafiyar da koke-koken jama’a duba da nasarorin da kuka samu tsawon shekaru.” In ji Barr. Abdu.

Shugaban ya kuma bayyana cewa JG-PCACC na da ayyuka guda biyu da suka hada da sauraran korafe-korafen jama’a da kuma yaki da cin hanci da rashawa, inda ya ce tun farko hukumar ta karbi korafe-korafe sama da 150 tare da warware su cikin ruwan sanyi.

“Muna da tasiri sosai a fannin korafe-korafen jama’a, tun daga farko mun samu kararraki sama da 150 da suka hada da batutuwan aure, daGado, da karbo basussuka, da  takaddamar ciniki, da dai sauransu, kuma da dama daga cikinsu an warwaresu.” In ji shugaban na JGPCACC.

A nasa jawabin, shugaban hukumar kula da korafe-korafen jama’a da ke Abuja (PCC), Bashir Abubakar ya bayyanawa jami’an hukumar korafe-korafen jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Jigawa irin tasirin da hukumarsa  ta ke bi wajen magance rikice-rikice.

“Jihar Jigawa na daya daga cikin jihohin da suka fi zaman lafiya amma za ku iya taimakawa jihar wajen samun nasara idan kun yi amfani da fasahar sadarwa ta zamani wajen kawo korafe-korafe cikin sauki,” inji shi.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa korafe korafen jama a korafe korafe jihar Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Ministar Jin Dadin Jama’a ta Sudan: Mayakan RSF Sun Kashe Mata 300 Da Yi Wa 25 Fyade A El Fasher

Ministar Jin Dadin Jama’a ta Sudan, Salma Ishaq, ta bayyana cewa Mayakan (RSF) sun kashe mata kusan 300 tare da yi wa 25 fyade a El Fasher, babban birnin Jihar Darfur ta Arewa a yammacin Sudan, a matsayin wani bangare na ayyukan kisan kiyashin da suke aikatawa a yankin.

A ranar 26 ga Oktoba, dakarun RSF sun kwace iko da El Fasher kuma sun yi kisan gilla ga fararen hula, a cewar kungiyoyin cikin gida da na kasa da kasa.

A cikin sanarwar da ta fitar Salma Ishaq, Ishaq ta ce abin da ya faru a El Fasher “ya yi kama da abin da ya faru a El Jeneina a shekarar 2023, amma ba a bankado da kuma yada laifukan da suka faru a El Geneina kamar yadda aka yi a El Fasher ba.” Ta kara da cewa dakarun (RSF) sun aikata fyade sau 25, ciki har da cin zarafin yara a gaban iyayensu mata, kafin daga baya a kashe su.

Ta kara da cewa “mutane kadan ne suka tsira a kan da ke tsakanin El Fasher da Tawila, kafin kashe su an azabtar da su, cin zarafinsu, da kuma fyaɗe.” Ta yi gargaɗin cewa ci gaba da kasancewar RSF a El Fasher “zai haifar da kawar da mutanen Darfur,” tana mai bayyana abin da ke faruwa a matsayin kisa ne na kabilanci da nuna wariya, inda ta zargi wasu kasashe da hannu a cikin lamarin.

Ministar ta kammala da cewa, batun mayakan RSF ba batu ne da za a iya magance shi ta hanyar kira ko hanyoyin diflomasiyya da tattaunawa ba, domin kuwa ba su fahimtar hakan, sai dai hanya ta amfani da karfi kawai, in ji ta.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Pezeshkian: Bunkasa Masana’antar Makamashin Nukiliyar Iran Don Inganta Rayuwar Al’ummar Iran Ne November 2, 2025 Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran November 2, 2025 Larijani: Iran Ba Ta Tsoron Gudanar Da Tattaunawa, Amma Ta Zama Mai Amfani November 2, 2025 Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza November 2, 2025 Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher November 2, 2025 IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya November 2, 2025 Amurka : zamu dauki matakin soja idan Najeriya ta gaza kawo karshen kashe Kiristoci November 2, 2025 Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza November 2, 2025 Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran November 2, 2025 Sojojin Amurka Na Kara Fuskantar Venezuwela Adaidai Lokacin da Trump Ke Musanta Batun Kai Hari November 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministar Jin Dadin Jama’a ta Sudan: Mayakan RSF Sun Kashe Mata 300 Da Yi Wa 25 Fyade A El Fasher
  • Majalisar Karamar Hukumar Bubura Ta Kai Tallafin Kayayyakin Abinci Cibiyar Gyaran Hali
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa