‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Darakta Janar Na Hukumar NYSC
Published: 6th, February 2025 GMT
Wasu ‘yan bindiga sun kai hari kauyen Tsiga da ke karamar hukumar Bakori a jihar Katsina inda suka yi garkuwa da tsohon Darakta Janar na Hukumar Kula da Matasa masu yi wa kasa hidima NYSC, Birgediya Janar Maharazu Tsiga mai ritaya da wasu mutum takwas.
Majiya mai tushe ta bayyana hakan ga gidan rediyon Najeriya a wata hira da manema labarai, yayin da ‘yan sanda ba su tabbatar da faruwar lamarin ba.
Wani shaidan gani da ido ya bayyana yadda gungun ‘yan bindigan suka afkawa al’ummar a kan babura da misalin karfe sha biyu na dare.
“Da misalin karfe 12 na dare ne ‘yan bindigar suka shigo garin na tsiga a bisa babura, inda suka rika harbi a sararin samaniya, sannan suka nufi gidajen da suka kai hari.”
“Kimanin mutum goma daga cikin ‘yan bindigar ne suka kai farmaki gidan Birgediya Janar Maharazu Tsiga, yayin da ssauran suka bazama wasu gidajen, inda suka tasa keyar mutum takwas.” inji shi.
Wakilinmu ya ruwaito cewa ‘yan bindiga sun sha kai wa al’ummar Tsiga hari a cikin shekaru bakwai da suka wuce.
Daga Isma’il Adamu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Ƴansanda Sun Kama Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar October 31, 2025
Manyan Labarai NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa October 31, 2025 Labarai Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda October 31, 2025