HausaTv:
2025-11-03@09:54:17 GMT

Kissoshin Rayuwa Sirar Imam Hassan (a) 12

Published: 5th, February 2025 GMT

12-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa Shirin wanda yake kawo maku kissoshi wadanda suka zo cikin alkur’ani mai girma ko cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin Dastane rastan na shahid Aya. Murtadha muttahhari, ko cikin littafin Mathnawi na maulana jalaluddeen ,Rumi, ko kuma cikin wasu littafan.

Da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu.

///… Madalla, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, mun ci gaba da kawo maku sirar Imam Alhassan (s) Jikan manzon All..(s) sannan limami na 2 daga cikin limamai masu tsarki daga iyalan gidan manzon All..(s) kuma da na farko ga  Fitima(s) diyar manzon All..(s).

Kuma a cikin shirimmu da ya gabata mun yi maganar yadda manzon All..(s), bayan kwanaki kadan da komawarsa Madina daga aikin Hajji, sai All..ya umurce shi ya je makabartar Bakiyya, ya kuma nemam masu gafara, don haka a cikin dare ya kira, daya daga cikin yentattun bayinsa wanda ake kira Abu Maubihah inda ya fada masa cewa, an umurce ni in nemawwa mutanen makabartan bakiyya gafara daga All ..T kuma ina son ka rakani.

A lokacinda suka isa makabartar sai ya fadawa Abu Maubihah, kan cewa an bani zabi na mubudan taskokin duniya har abada, sannan aljanna, da kuma haduwa da All..,na a yanzu,  amma na zabi haduwa da Ubangiji na All…

Sai kuma bayan kwanaki kadan, manzon All..(s) sai fara rashin lafiyarsa ta karshe, Sannan ya fara tunanin yadda iko zai koma ga Aliyu dan Abitalib (a) a bayansa ba tare da wata matsala ba. Ya so ya dauki wadannan matakan ne, saboda ya fahinci cewa akwai wasu manya-manyan sahabban manzon All..(s) wadanda suke kodayin shugabaci a bayansa.

Don haka ne ya tada rundunar Usama dan Zaidu, dan shekara 17 a duniya, sannan tattara dukkan wadannan manya-manyan sahabbansa, daga cikin muhajirun da ansar, tare da Umurnin su tafi yaki zuwa kasar Ruma ta gabas don yaki da su. Don haka, kafin su dawo yayi wafati, sannan Aliyu dan Abitalib ya karbi shugabanci ba tare da wata matsala ba. Kuma ko sun dawo ba zasu iya yi masa tawaye ba.

Manzon All..ya nunawa Usama dukkan dabarbarun yakin da yaki bukata. Sannan ya bashi tutar, ya ce masa ya kama hanya. Sai Usama ya  je wani wuri a bayan madina wanda ake kira Jurf ya kafa sansanin sojojinsa yana jiransu  su fita.

Usama yayi ta jiransu, amma suka ki fitowa, wasu ma suka fara sukar shugabancin Usama dan Zaidu, a wannan yakin. A lokacinda labari ya zo masa, cewa wasu sunki fita, sannan sun fara sukansa kan shugabantar da Usama, a nan ma sai ya sake fitowa, ya yi masu Magana inda ya sake jaddada masu cewa, Usman ya canacanci shugabanci, haka ma babansa kafin shi. Duk da cewa a lokacimma sun ki amincewa da jagorancin bababansa.

Mun kama fara kawo maku darussan da za mu iya dauka, a cikin wannan hadisin, na cewa dabarar da manzon All..(s) ya yi na nisantar da masu kodayin mulki a bayansa ya kasa samun nasara. Amma kuma ya zama hujja a kansu har duniya ta nade.

sannan su ma sun fahinci haka, shi ya sa suka sabawa manzon All..(s). Bayan haka

mun ji cewa a cikin manya-manyan sahabban da ya Sanya a cikin rundunar Usama akwai, Abubakar, da Umar da Abu ubaida dan Jarrah da Usman da sauransu.

Sanna ya ki sanya su kan rundunar ne, don kada wani daga cikinsu ya yi amfani da matsayin don su maida shi damar biyar bukatunsu na kaiwa da shugabanci a bayansa.

Don haka ya tushe masu hanya, sannan ya la’anci duk wanda ya ki tafiya da rundunar Usama.

Banda haka wa ta dubarar da manzon All..(s) ya yi, na shugabantar da Usama dan Zaidu kan wadannan manya-manyan sahabban, shi ne ya nuna masu cewa, shugabanci cancanta ce, ba yawan shekaru ba.

Kuma All..ya na bawa shugabanci ne, ga wadanda ya ga dama, kuma zai bashi ilmi da kuma karfin da yake bukata don cancantar shugabancin.

Don haka manzon All..(s) ya bar wannan duniyar, manya-manyan sahabban manzon All..(s) suna, karkashin shugabancin Usama dan Zaidu wanda bai fi shekaru 17 a diniya ba.

A wani hadisi manzon All..(s) ya na cewa: wanda ya gabatar da kansa a cikin musulmi al-hali ya san cewa akwai wanda ya fi cancanta da aikin to hakika ya kha’inci All..da manzonsa da kuma muminai (s).

A wani hadisin, ya na cewa: All..ya na kudaitarwa, sosai kan, wajen zaben mafi korewar mutane,  wanda ya kasance mafi cancanta ga wani matsayi. Lalle, su sanya maslahar al-umma ne abin lura a wajen su, a lokacin zaben. Su kasance amintattu a cikin abinda suke karba daga hannun mutane.

Sannan su zamanto amintattu a kashe kudaden kan abubuwan jin dadin rayuwar mutane. Sannan su tafiyar da al-amuran mutanen a cikin adalci kadai.   

Wannan ka da ya kasance, da yawan shekaru ne ake zabe ba, sai dai ya kasance tare da kwarewa da kuma sanin makamar aiki, da sanin abubuwan da mutane suke bukata.

Don haka manzon All..(s) a cikin shugabantar da Usama Dan Zaidu ya kakkabo wasu daga cikin wadanda suke takara da Amirulmuminina (a) kan shugabancin al-ummar musulmi a bayansa.

Ya karya zukatansu, daga neman wannan mukamin, ya kuma kashe guiwarsu da yunkurinsu na neman wannan matsayin. Ya nisantar da su nesa ba kusa ba daga wannan burin nasu.

Sannan su ma sun fahinci hakan, daga wajen manzon All…(s).  Baku ga cewa, Umar ya na cewa: Ya kai Usaman! Manzon All.. zai yi wafati kana shugabana?

 Basu gushe ba suna jan kafa, sun ci ga ba da sabawa umurnin manzon All..(s) har sai da ya yi wafata. (s).

Wannan kadan Kenan na abinda za’a iya fahinta, na shugabatar da Usama dan shekara kimani 17 kan shaihunan kurasihawa, da kuma wasu shuwagabannin ansar wadanda suka kodayin shugabancin al-ummar musulmi bayan wafatin manzon All.. (s).

Har’ila yau wannan ya tabbatar mana akwai makirci babba da aka kulla don hana Imam Ali (s) za ma a kan kujerar da shi kadai ya dace da ita bayan manzon All..(s).

Daga nan sai zazzabi ta yi tsanani wa manzon All..(s), a lokacin, matansa suna kusa da shi, a duk lokacinda suka sa hannunsu a kansa suna jin yadda yake zafi.

Sukan sanya ruyuwan sanyi kusa da shi, a duk sanna ya sa hannunsa cikinsa sai ya shafa fuskansa da sanyin hannunsa..

Sai mutane su na ta kai kawo suna bankwana da shi, sai da suka taru a gidansa,  sai ya fada masu:

Yace: Ya ku mutane, an kusa a dauki raina, daukewa mai sauki, sannan a tafi da ni. Hakikin na gabatar da maganganu, don sauke uzuri da ke kaina a kanku. Sai dai lalle ni ina barin Littafin All..mai girma da daukaka da kuma zurriya ta  Ahlubaiti na.  Sai ya kama hannun Aliyu(a) ya daga ta, ya ce: Ga Aliyu nan tare da Alkur’ani , kuma kur’ani ya na tare da Ali ba za su rabu ba, har sai sun riskeni a tabki.

Abinda yakamata al-umma ta yi shi ne ta bi umurnin manzon All..ta bi abinda ya fada mata ta bi Amirulmuminina (s), ta mika masa shugabanci, don shi ne kawai zai tafiyar da al-amarinsu kan koyarwar Alkur’ani mai girma. Da kuma hukunci da hukuncin All..T

Ta yin haka ne kawai za ta tsira daga dukkan tawaya, kuma fitinu ba za su same ta ba, haka ma dukkan hatsurra ba za su sameta ba.

Daa kuwa musulunci, zai dau matasyinsa kai tsaye, a duniya, ya kuma sami iko da da ita gaba daya. Ya cika shi da adalci.

Har’ila yau kafin rasuwarsa manzon All..(s) ya daura rawaninsa, sai ya je masallaci ya hau mimbarinsa, sai ya ce masu, Lalle Ubangijina ya hukunta, ya kuma rantse kan cewa ba zai yafe zuluncin azzalumi ba, don haka ina hadaku da All…duk wani mutum wanda yake da wani abu da na yi masa sai ya tashi ya fada don yayi kisasi, saboda kisasi a gidan duniya yafi mani da kisasa a Lahira. Inda za’a yi hakan a gaban mala’iku da annabawa…}.

Manzon All..(s) ya na nuna masu kan cewa zalunci ko wace irice, mutum ya warware shi a lduniya ya fi masa a yi masa adalci a lahira.

An dade ba wanda yayi Magana sai wani mutum daga karshen masallacin, mai suna Sawadat dan Qais, sai ya ce: ee ya manzon All..(s) ka taba doka na a wani lokaci a ciki na. don haka ina son kisassi.

Sai manzon All..(s) yace masa ya zo . sannan ya aiki Bilal ya kawo bulala daga gidansa, da ya kawo sai mutane suna gani me mutumin nan za iyi yi wa manzon All..(s) a cikin wannan halin da yake na rashin rafiya.

Sai Sawada ya zo kusa yana karkarwa., saboda haibar manzon All.. sai ya ce: Ya manzon All..ka kwaye mani cikinka, sai ya ce ya manzon All..(s) kayi mani izini in Sanya bakina a kan cikinka?, sai yace masa ee. Sai ya Sanya bakinsa a kan cikin manzon  All… idanunsa ya na zubar da hawaye.

Sai ya na cewa  ina neman tsari daga wuta albarkan wurin kisasi da ga manzon All..(s), a ranar lahira.

Sai manzon All..(s) ya ce masa, za ka yi kissasi ne ko kai yi afwa?, sai yace,  sai yace Afwa ya manzon All..(s). 

Sai manzon All..(s) ya daga hannayensa ma su albarka ya na uddu’a yana cewa: Ya Ubangiji! ka gafartawa Sawadah, saboda afwar da ya yi wa annabinka Muhammadu. (s).

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: manya manyan sahabban ya manzon All Ya manzon All

এছাড়াও পড়ুন:

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

An ture Mataimakin Gwamna Gefe, Tsarin karba-karba Na Goyon Bayan Kwara ta Arewa.

Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazak, zai kammala wa’adinsa na biyu a shekarar 2027, amma babu wata alamar cewa mataimakinsa, Mista Kayode Alabi, zai gaje shi.

Yanayin siyasa a jihar na nuna cewa yankin Sanatocin Kwara Arewa ne ake sa ran zai samar da gwamna na gaba; Alabi yana daga Kwara Kudu.

Kwara ta Arewa ba ta samar da gwamna da tun daga 1999, yayin da Kwara Kudu ta rike kujerar siyasa ta farko a jihar na tsawon shekaru takwas, kuma zuwa 2027 Kwara Tsakiya za ta kasance ta rike kujerar na shekaru 20.

Masu nazarin siyasa guda biyu, Comrade Abdul-Rahoof Bello-Labelabe da Comrade AbdulLateef Ishowo, sun bayar da dalilan da suka sa mataimaka ke samun wahalar gadon shugabanninsu.

Kwamared Abdul-Rahoof Bello-Labelabe ya ce, “Mataimakan gwamnoni ana kallonsu ne a matsayin wasu mutane da ke shiga zabe a kan tikitin jam’iyya daya tare da gwamnonin da suke aiki tare.

Amma a mafi yawan lokuta, ba su ne zabin gwamnonin ba, sai jam’iyya ta tilasta wa gwamnonin domin cika sharudan zabe.”

“Tun da kundin tsarin mulki bai bai wa mataimaka wasu ayyuka na musamman ba, galibi gwamnonin suna kallon su a matsayin safaya taya kawai.

“Wannan rashin aikin hukuma ko warewa da ake yi wa mataimaka na haifar da rashin jin dadi, hassada da rashin amana, sannan kuma yana haifar da fushi da dangantaka mara kyau da shugabansu.

“Saboda haka, gwamnonin na tafiyar da mulkinsu ne, suna barin mataimakansu a duhu. Don haka, a karshen wa’adin gwamnonin, tsoron ramuwar gayya ko adalci mai daukar fansa zai fara yawo a zukatansu, kuma za su nemi wani mutum mafi aminci domin ya gaje su, domin samun kwanciyar hankali da zaman lafiya bayan sauka daga mulki.”

A nasa bangaren, Kwamared AbdulLateef Ishowo ya ce, “Abin ya danganta da irin rawar da ake takawa. Yayin da wasu mataimaka ke da matsananciyar halayya kuma suna da buri fiye da kima, wasu shugabanni kuma suna da mulkin kai ba tare da bukata ba.

“Dauki tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar da tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo, misali; yayin da na karshe ya bar fagen siyasa ga na farko cikin kyautatawa, Atiku ya yi amfani da damar wajen kokarin kwace matsayi daga shugabansa. Wannan dai yanayi ne na musayar bangarori biyu.”

 

BORNO: Karfin Iko Ya Hana Kadafur Cimma Burinsa

Kididdigar siyasa da ta kasance al’ada a siyasar Jihar Borno tun fara dimokuradiyya a 1999 za ta zama babban cikas ga mataimakin gwamna na yanzu, Alhaji Usman Kadafur, wajen gaje Gwamna Babagana Umara Zulum a karshen wa’adinsa a zaben shekara mai zuwa.

Yayin da yake magana da wakilinmu a Maiduguri, wani masani kan siyasa kuma dan asalin Kudu Borno, Adamu Ali, ya ce abu ne mai wuya Kadafur ya gaji Zulum, inda ya lura cewa a farko, Kadafur ba shi ne mafi karbuwa ba ko ma a Karamar Hukumarsa ta Biu a Kudu Borno.

Ali, wanda ya bayyana cewa Kadafur bai yi tasiri ga mutanen yankinsa ba, ya kara da cewa babu wata yarjejeniya ta hukuma da ke nuna cewa iko ya kamata a mika wa Borno ta Kudu, yankin da mataimakin gwamnan ya fito.

Ya ce, a gaskiya, lokaci guda tilo da aka sami dan fatan mika iko zuwa Borno ta Kudu shi ne a lokacin mulkin tsohon Gwamna Ali Modu Sheriff. A yankin Uba na Borno Kudu, Sheriff ya yi wata sanarwa cewa, bayan shi, iko ya kamata ya koma Borno ta Kudu saboda abokinsa, marigayi Zubairu Maina. Sai dai, da zarar Zubairu Maina ya rasu, duk wannan tsari ya tsaya cak.

Masanin siyasar ya ce, “Idan ka duba tsarin, kafin wani ya fito a matsayin gwamna, akwai wani tsari, kuma wannan tsari yawanci yana tafiya ne ta hanyar zaben farko. Ana gudanar da zaben farko ne ta hannun wakilai, kuma mafi yawan wakilan sun fito ne daga kabilar Kanuri wadda ke sarrafa Arewa da Borno ta Tsakiya.”

“Yankin Borno ta Kudu na da kananan hukumomi tara kawai, kuma duk da irin kokarin da suka yi, ko da dukkan kananan hukumomin sun hadu, za su samar ne da kashi daya cikin uku na wakilai ne kawai. Saboda haka, saboda wannan dalili, zai yi wuya ga mataimakin gwamna na yanzu, Kadafur, ya gaji ubangidansa, Gwamna Zulum, balle a ce iko ya koma Borno ta Kudu sai dai idan wani abu mai ban mamaki ya faru.”

LEADERSHIP Weekend ta ruwaito cewa tun fara dimokuradiyya, kabilar Kanuri a Arewa da Borno ta Tsakiya ce ke samar da gwamna, yayin da mukamin mataimakin gwamna ake bai wa mutanen Borno ta Kudu.

Bisa dalilin da ya sa mataimakan gwamna ba sa yawan gaje gwamnoninsu, wani babban dan siyasa a Borno, Alhaji Ahmed Ashemi, ya ce gwamnonin ba sa son mutanen da suka yi aiki tare da su su hau mukamin gwamna su kuma zama masu karfi kamar yadda suka kasance lokacin da suka zama gwamna.

Ashemi ya ce, “Bayan shekaru takwas ko hudu, gwamnonin ba sa son mataimakansu su zama gwamnonin kuma su zama masu mulki a birnin.”

“Ta yaya wanda nake ba wa umarni kuma yake bin bayana zai zama gwamna kwatsam? Daga baya kuma na koma gefe na zama dan kallo.”

“A wasu wurare, saboda wata kabila ce ke rike da kujerar gwamna tsawon lokaci, masu rike da iko ba za su so a mika kujerar zuwa wata karamar kabila ta hannun mataimakin gwamna ba — sai dai idan wani lamari kamar mutuwa ya sauya tsarin.”

 

GOMBE: Siyasar Addini Ta Hana Mataimaki Cimma Burinsa

Yayin da Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya na Jihar Gombe ke shirin fita daga ofis a 2027, yanayin siyasar jihar ya fara dumi. Tambayar da ke mamaye al’amuran siyasa ita ce: “Wa zai fito a matsayin gwamna na gaba?”

Mataimakin Gwamna, Dr Manassah Daniel Jatau, dan kirista daga Kudu na Karamar Hukumar Balanga, zai iya kasancewa cikin wannan tattaunawa da damar gaje shugabansa, amma tun dawowar dimokuradiyya a 1999, siyasar Gombe tana bin wani tsarin da ake iya hasashe wanda aka tsara ne bisa la’akari da yankuna da addini.

Dukkan gwamnonin da aka zaba tun daga Abubakar Habu Hashidu zuwa Danjuma Goje, Ibrahim Hassan Dankwambo, har zuwa Inuwa Yahaya na yanzu duk sun fito ne daga arewacin jihar da Musulmi suka fi rinjaye, yayin da mataimakansu suke fitowa daga kudu inda Kiristoci suka fi yawa.

Ga masana kamar Dr Musa Tukur, malamin kimiyyar siyasa a Jami’ar Gombe, wannan tsarin hada yankuna biyu ya taimaka wajen inganta hadin kai, amma kuma ya haifar da katangar gado. Babu wani mataimakin gwamna a tarihin dimokuradiyyar Gombe da ya taba gadon shugabansa.

Wannan yana nuna cewa yawancin masu zabe a yankunan da Musulmi suka fi rinjaye suna yawan zabar ‘yan takarar Musulmi, yayin da yankunan Kiristoci ke fifita Kiristoci. Wannan ne dalilin da ya sa tun daga 1999, kujerar gwamna ta kasance a hannun bangaren arewa mai rinjayen Musulmi.

Saboda haka, masu lura da al’amura na ganin cewa takarar shekara ta 2027 ba za ta karya wannan tsari ba, wanda hakan ke nuna cewa hanyar Jatau zuwa mulki za ta kasance mai wahala. A cewar mai sharhi kan harkokin siyasa, Ibrahim Alkali, “Gombe ba ta kai matsayin da za ta ba da dama ga dan kudu Kirista ya zama gwamna ba, musamman duba da yanayin cikin gida na jam’iyyar APC.”

Yayin da wasu maganganu a kafafen sada zumunta ke nuna cewa ana hasashen wanda Gwamna Yahaya zai fi so ya gaje shi, da sunaye kamar Injiniya Aliyu Muhammad Kombat da Arc. Yakubu Yunusa na kamfanin Lubell Nig Ltd., mai sharhi Abdulrahman Musa ya bayyana cewa salon Yahaya ya yi kama da na shugabannin da ke kallon batun gadon mulki a matsayin hanyar kare gadonsu, ba wai neman zama uba a siyasa ba.

Duk da cewa Jatau mataimaki ne mai biyayya kuma gogaggen ma’aikaci a fanninsa, wasu daga cikinsu na ganin ba ya cikin manyan ‘yan takarar da ake tattaunawa a kansu don su gaji kujerar mulki. Sai dai wasu na ganin cewa tsayawar Jatau takara na iya zama gwaji ga matakin wayewar siyasar jihar.

 

Jihar Imo: Mataimakin Gwamana Bai Da Kahon Karon Yin Takara

Yanayin siyasa a Jihar Imo bai nuna cewa mataimakiyar gwamna, Hajiya Chinyere Ekomaru, za a ba ta dama ta gaji gwamnatin Gwamna Hope Uzodimma ba.

Dalilin hakan ba ya da nisa, domin mataimakiyar gwamnan tana kama da sabuwa a harkar siyasa, tana da karancin kwarewa, tsarin siyasa da kwarewar da ake bukata don tafiyar da jihar mai rikitarwa kamar Imo.

Wannan kuma yana da alaka da asalin aikinta, kasancewarta ma’aikaciyar gwamnati mafi yawan lokacinta, ba tare da samun gogewar siyasa sosai ba.

Idan aka kalli halayyarta da kyau, ana iya fahimtar cewa watakila kawai an jawo ta cikin siyasa ne don cike gurbi, ba tare da niyyar ta gaji shugabanta ba.

Wani mai sharhi kan siyasa, Dr Harold Onumo, ya shaida wa LEADERSHIP Weekend cewa yawancin gwamnonin ba sa son barin mataimakansu su gaje su saboda son kai, tsoron abin da ba a sani ba, da kuma karancin kwarin gwiwa.

Ya bayyana cewa wasu gwamnonin na jin tsoron cewa idan suka ba da dama irin wannan, mataimakansu za su iya zama masu kudi da tasiri fiye da su.

A cewarsa, gwamnonin yawanci suna son su ci gaba da zama masu sarrafa al’amura, kuma su kasance ana kallonsu a matsayin “uba” a siyasa.

“Suna son su ci gaba da zama shugabanni kuma su rike tsarin siyasa gaba daya. Sun fi son yanayi inda su kadai suke da iko a fagen siyasa,” in ji shi.

Ga Dr Chinyere Ekomaru, mataimakiyar gwamnan Jihar Imo ta yanzu, batun gadon mulki na iya zama babban kalubale, musamman ganin yadda manyan ‘yan siyasa ke kara neman kujerar Douglas House.

Tun bayan dawowar dimokuradiyya a 1999, babu wani gwamna a Jihar Imo da ya taba nasarar saka mataimakinsa ya gaje shi a kujerar mulki.

Yayin da Cif Achike Udenwa ya fi son Cif Iyke Ibeh, manyan ‘yan siyasa sun hadu ne suna goyon bayan Dr Ikedi Ohakim.

Lokacin da Ohakim ya nemi wa’adi na biyu, tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan ya ba da goyon baya ga Owelle Rochas Okorocha maimakon sa.

A lokacin da Okorocha ya yi kokarin saka wanda yake so surukinsa, Cif Uche Nwosu manyan kungiyoyin siyasa suka ki, lamarin da ya haifar da fitowar Emeka Ihedioha, wanda daga baya aka maye gurbinsa da Uzodimma.

A halin yanzu, rikici na tasowa tsakanin yankin majalisar dattawan Owerri da Okigwe kan wanda ya kamata ya gaji Uzodimma.

Yankin Owerri na jaddada cewa tun daga 1999 sun rike kujerar gwamna na kusan watanni takwas ne kawai a karkashin Cif Emeka Ihedioha.

A gefe guda kuma, yankin Okigwe na cewa dole ne a kammala wa’adinsu da aka katse lokacin mulkin Dr Ikedi Ohakim kafin yankin Owerri ya sake samun damar rike kujerar.

Masana harkokin siyasa na jaddada cewa Dr Chinyere Ekomaru, a matsayinta na mace, ba ta da karfin siyasa ko tasiri da zai ba ta damar ta gaji Uzodimma, domin har yanzu ba ta taka muhimmiyar rawa a kowace babbar matsalar siyasa a cikin jihar ba.

Sir Sunny Ndukwu, wani jigo a jam’iyyar PDP daga Ngor Okpala, ya ce babu wata dama da Ekomaru za ta samu.

A cewarsa, burin yankin Owerri a yanzu shi ne kujerar gwamna gaba daya, ba na mataimaki ba kamar a da.

Ya bayyana cewa, da marigayi Cif Emmanuel Iwuanyanwu, tsohon Shugaban Ohanaeze Ndigbo na Duniya, yana raye, da Ekomaru na iya samun dama. Amma da rasuwarsa, damar siyasarta ta ragu kwarai.

“A da, tsawon shekaru fiye da ashirin, ana tattauna makomar siyasar yankin Owerri a fadar marigayi Cif Emmanuel Iwuanyanwu. Mataimakiyar gwamnan Jihar Imo a yanzu, samfur ce daga gidan siyasar Iwuanyanwu.

“Zan iya fada maka, da yana raye, da Ekomaru tana cikin manyan ‘yan takarar kujerar gwamna. Amma yanzu Iwuanyanwu ya rasu, kuma wannan damar siyasa da take da ita a baya ta shude, sai dai in da gaske tana da niyyar tsayawa takarar 2027.”

Ya kara da cewa: “Magana ta gaskiya, bana tunanin Gwamna Uzodimma zai zabi Ekomaru a matsayin wacce zai goyi baya don ta gaje shi. Zaben gwamnan Imo zai kasance mai zafi sosai, kuma ba na tunanin gwamnan zai zabi wanda ba shi da ingantaccen tsari na siyasa a ko’ina cikin jihar.

“Kodayake Uzodimma gwamna ne mai ci, duk wanda zai zaba a matsayin magajinsa dole ne ya kasance mutum mai karfi a siyasa, domin sakamakon zaben gwamna na 2023 na iya bambanta kwarai da abin da za mu gani a 2027,” in ji Ndukwu.

Ko da yake Uzodimma bai bayyana wanda yake so ya gaje shi ba tukuna, masu lura da harkokin siyasa na ganin cewa hakan zai kasance aiki mai wahala, amma zai iya yiwuwa idan aka yi la’akari da dangantakarsa mai karfi a jam’iyyar APC.

 

Bauchi: Ministoci da Magoya baya na Neman Gaje Bala Mohammed

Takarar neman zama gwamnan Bauchi a shekarar 2027 ta fara a hankali tun kafin fitowar tallace-tallace da gangamin siyasa. A bayan fage, ana kafa kungiyoyi, ana gudanar da tarurruka a Abuja da Bauchi, kuma ana tsaurara niyyar takara.

Gwamna Bala Mohammed na jam’iyyar PDP yana wa’adinsa na karshe, kuma fafutukar neman wanda zai gaje shi tana jan hankalin fitattun manyan ’yan siyasa a tarihin jihar.

Abin da ya bambanta wannan takara shi ne irin mutanen da ke son tsayawa: ministocin tarayya, sanata, kwamishinoni, kwararru, da manyan masu tsara dabarun siyasa duk suna hangen zama gwamna.

Wannan ba zabe kadai ba ne, har ma rikici ne na tasiri, gadon mulki, da kuma tasirin kungiyoyin siyasa na yankuna daban-daban.

Ko da yake jam’iyyar ADC karamar jam’iyya ce, tana da fitattun ‘yan takara biyu: tsohon Shugaban Hafsan Sojojin Sama kuma dan takarar APC a zaben 2023, Ambasada Sadikue Abubakar, wanda ya dawo takara da kwarewar soja, gogewar diflomasiyya, da kuma gagarumin goyon baya.

Baya ga shi, akwai Sanata Halliru Dauda Jika, dan siyasa mai karfi a kasa wanda ke da zurfin tasiri a siyasar Bauchi. Sai dai kalubalen su shi ne yadda za su iya farfado da karfin jam’iyyarsu wacce ba ta da tsari mai karfi kamar manyan jam’iyyu.

Jam’iyyar All Progressibes Congress (APC) ita ce ake ganin tana da jerin fitattun ‘yan takara mafi karfi.

Sanata Shehu Buba Umar na zuwa da kwarewar majalisa, goyon bayan talakawa, da kuma tsari mai karfi.

Bala Wunti kuwa, shahararre ne a fannin man fetur da iskar gas. Ko da yake wannan shi ne karo na farko da zai shiga siyasa kai tsaye, Wunti yana samun karbuwa sosai a Bauchi.

Ministoci biyu da ke kan mulki sun kara zafafa takarar sosai: Ministan Lafiya da Walwalar Jama’a, Farfesa Muhammad Ali Pate, kwararren masani ne da duniya ke girmamawa, yayin da takwaransa na Harkokin Waje, Jakada Yusuf Tuggar, ke da karfafan dangantaka a duniya.

 

A bangaren APC, tambayar ba wai wanene yake son tikitin takara ba bace, har ma wa jam’iyyar za ta iya haduwa a bayansa.?

Jam’iyya mai mulki, PDP, kuwa tana fuskantar rikicin tsarin wanda zai gaje ta.

Dr Yakubu Adamu, Kwamishinan Kudi kuma daya daga cikin amintattun abokan Gwamna, sabon shigowa ne daga fannin banki amma baya da zurfin tushe a siyasa.

Farouk Mustapha, Kwamishinan Harkokin Musamman da Cigaban Karkara, yana zuwa da kuzarin talakawa da karbuwa daga bangarori daban-daban na siyasa.

Ya taba yin takarar gwamna a karkashin jam’iyyar APC kafin ya koma PDP a gabanin zaben 2023, kuma ya kasance Darakta Janar na yakin neman zaben Gwamna Bala Mohammed.

 

Usman Adamu Shi Ma Dan Takara Ne Mai Biyayya Ga Gwamnati

Duk da haka, yiwuwar shigar Sanata Abdul Ningi, babban dan siyasa mai karfin tasiri a fadin jihar na iya canza daidaiton siyasa da kuma kalubalantar ikon gwamna.

Tare da ministoci, kwamishinoni, kwararru, gogaggun ‘yan siyasa da kuma rikicin biyayya ga jam’iyya da burin kashin kai, zaben 2027 na neman zama mafi rikitarwa a tarihin siyasar Bauchi cikin shekaru da dama.

Lissafin ya riga ya fara a hankali, cikin dabara, kuma cikin tsanani.

 

Nasarawa: Gwamna na juyawa, mataimakin gwamna na neman kujerar majalisar dattawa

A Jihar Nasarawa, mataimakin gwamna mai ci, Dakta Emmanuel Akabe, an ruwaito cewa yana neman kujerar majalisar dattawa ta yankin kudu, alamar cewa tsarin juyawar mulki da ake bi a jihar bai dace da yankinsa ba.

Wakilinmu ya ruwaito cewa tsarin da aka kafa tun daga 1999 yana bai wa yankuna damar karbar mulki ta juyawa bayan kammala wa’adin shekaru biyu daga wani yanki.

Ana sa ran cewa a 2027, mulki zai koma Nasarawa ta Yamma (yankin Keffi).

An riga an fara ganin manyan tallolin siyasa (billboards) da ke dauke da sakonnin burin Dakta Akabe na neman kujerar majalisar dattawa a Lafia, babban birnin jihar, da sauran sassan yankin mazabar Nasarawa ta Kudu.

Wanda ke rike da kujerar a halin yanzu, Sanata Mohammed Onawo, ana hasashen yana da wasu manyan burin siyasa.

Mataimakin Gwamna Akabe, kamar yadda LEADERSHIP Weekend ta gano, yana da kyakkyawar alaka da babban ubangidansa, Gwamna Abdullahi Sule, kuma har yanzu an ba shi cikakken ‘yanci wajen gudanar da aikinsa.

Oyo: Mataimakin gwamnan ya kame bakinsa a yayin da tsarin rabon mulki ke haifar da matsin lamba daga waje

A Jihar Oyo, mataimakin gwamna, Barista Bayo Lawal, bai nuna wata sha’awa ta tsayawa takarar gwamna a 2027 ba.

Haka kuma babu wata matsala da aka sani tsakaninsa da gwamnan jihar, Seyi Makinde.

Ko da yake akwai kiraye-kirayen da ke neman a bai wa yankin Oke-Ogun inda mataimakin gwamna ya fito damar zama gwamna na gaba, Lawal bai bayyana wani niyyar tsayawa takara ba a fili.

Sai dai wasu ‘yan takara daga jam’iyyun siyasa daban-daban sun fara nuna sha’awar shiga gasar zaben gwamna.

 

Legas: Masu Tasiri A Siyasa Na Hangen Wasu Ba Mataimakin Gwamna Ba

A Jihar Legas, ana ganin cewa Gwamna Babajide Sanwo-Olu ba shi da karfi sosai wajen yin tasiri a zaben wanda zai gaje shi.

Mataimakinsa, Dr Obafemi Hamzat, a cewar rahotanni, ba ya cikin jerin mutanen da ake kallon su a matsayin masu yuwuwar zama magadansa a shekarar 2027, lokacin da su biyun za su kammala wa’adin su na biyu tare.

A baya, Hamzat ya taba zama Kwamishinan Kimiyya da Fasaha a lokacin da Shugaba Bola Tinubu yake gwamna na Jihar Legas. Ya ci gaba da rike wannan mukamin a karkashin Gwamna Babatunde Fashola da ya hau karagar mulki a shekarar 2007.

Majiyoyi daga cikin manyan masu tasiri a siyasar Legas sun nuna cewa zai yi wuya a ba Hamzat mulki saboda gogewarsa da ‘yancin kansa. Wata daga cikin majiyoyin ta ce, “Zai yi wahala a sarrafa mutum mai irin wannan kwarewa da gogewa.”

Tun bayan saukarsa daga mulki a shekarar 2007, Shugaba Tinubu ne ya kasance ginshikin da ke yanke shawara kan wanda zai zama gwamna a Legas.

Ogun: Mataimakin Gwamna Ba Ya Cikin ‘Yan Takara, Manayn ‘Yan Siyasa Sun Fara Gangami

Haka nan a Jihar Ogun, Gwamna Dapo Abiodun na iya kin amincewa da fitowar mataimakiyarsa, Noimot Salako-Oyedele, a matsayin wacce za ta gaje shi.

Ana samun rahotannin cewa Sanata Solomon Adeola, shugaban kwamitin Majalisar Dattawa kan Kasafin Kudi, da tsohon Jakadan Nijeriya a Birtaniya, sun fara nuna sha’awar takarar kujerar gwamna domin gadar Abiodun.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya November 2, 2025 Manyan Labarai Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka November 2, 2025 Manyan Labarai An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano November 2, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • ‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
  • Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya
  • Zaɓen Tanzania: Shugaba Samia Suluhu Hassan ta yi tazarce
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai