Aminiya:
2025-05-01@02:21:58 GMT

’Yan sanda sun ceto mutum 23 da aka sace a Kaduna

Published: 3rd, February 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, tare da Sojoji sun samu nasarar ceto mutum 23 da ’yan bindiga suka sace a wani artabu da aka yi a ƙauyen Doka, da ke Ƙaramar Hukumar Kajuru.

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, DSP Mansur Hassan, ya fitar, ya bayyana cewa babban jami’in ’Yan Sandan yankin Kajuru ne ya jagoranci samamen.

Arsenal ta yi sukuwar salla a kan Man City da ci 5 Osimhen ya maka ɗan jarida a kotu

Ya ce bayan samun bayanan sirri game da maharan, jami’an tsaro sun kai farmaki inda suka ceto dukkanin mutanen 23, waɗanda mazauna Kauru ne.

A yayin artabun, wasu daga cikin maharan sun mutu, yayin da wasu suka tsere cikin daji da raunukan harbin bindiga.

A cewar sanarwar, an sake haɗa mutanen da iyalansu a Ƙaramar Hukumar Kauru.

An luma ƙara tsaurara matakan tsaro a yankin domin tabbatar da cewa babu wata fargaba.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Kaduna, Rabiu Muhammad, ya bayyana gamsuwarsa da wannan gagarumar nasarar.

Ya ce za su ci gaba da yaƙi da ta’addanci a Jihar Kaduna bisa jagorancin Gwamnan Jihar, Uba Sani.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Artabu

এছাড়াও পড়ুন:

Hajjin 2025: Gwamna Namadi Ya Nada Sarkin Kazaure Amirul Hajj

 

Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Umar Namadi, ya amince da nadin Mai Martaba Sarkin Kazaure, Alhaji Dr Najib Hussaini Adamu, a matsayin Amirul Hajj na Jihar Jigawa, kuma shugaban tawagar Gwamnatin jihar domin gudanar da aikin Hajjin 2025.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Sakataren Gwamnatin Jihar Jigawa, Malam Bala Ibrahim, ya sanya wa hannu kuma aka raba wa manema labarai.

Gwamnan ya kuma amince da nadin mambobin tawagar Amirul Hajjin.

Malam Bala Ibrahim ya bayyana cewa, mambobin sun hada da Dr. Yusuf Abdurrahman, Babban Limamin Masarautar Hadejia da Alhaji Lawan Ya’u Roni, Talban Kazaure.

Sauran su ne Dr. Mahmoud Yunusa, Sa’in Dutse da kuma Alhaji Adamu Dauda Zakar, Durbin Hadejia.

Sanarwar ta bayyana cewa an yi wadannan nade-nade ne bisa la’akari da irin kwazon da suka nuna a ayyukansu, sadaukarwa, kishin kasa, amana da kuma tsoron Allah.

A cikin sakon taya murna ga wadanda aka nada, Sakataren Gwamnati ya bukace su da su ci gaba da nuna wadannan dabi’u yayin da za su gudanar da wannan muhimmin aiki da aka dora musu, don kara tabbatar da amanar da gwamnatin da al’ummar Jihar Jigawa suka dora a kansu.

Sanarwar ta kara da cewa, ana sa ran tawagar Amirul Hajjin za ta yi aiki kafada da kafada da Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa da kuma sauran hukumomin da suka dace a matakin Jiha, Tarayya da na kasa da kasa domin tabbatar da gudanar da aikin Hajji cikin nasara da inganci.

Sanarwar ta bayyana cewa nade-naden sun fara aiki nan take.

 

Usman Muhammad Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Sokoto Ya Amince Da Sauya Wa Manyan Sakatarori 25 Ma’aikatu A Jihar 
  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  • Hajj 2025: Kaduna Ta Gaddamar Da Ayarin Likitoci Da Za Su Kula Da Alhazan Jihar
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Sojoji Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace, Sun Ƙwato Shanu 32 A Katsina
  • Jihar Kebbi Ta Kammala Shirye-shiryen Aikin Hajjin 2025
  • Hajjin 2025: Gwamna Namadi Ya Nada Sarkin Kazaure Amirul Hajj
  • Tawagar Jami’ai Da ‘Yan Kasuwar Ta Tunusiya Ta Gana Da Mataimakin Shugaban kasar Iran