Qasem : Dole Ne Lebanon Ta Tabbatar Da Cewa Isra’ila Ta Aiwatar Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta
Published: 2nd, February 2025 GMT
Sakatare Janar na kungiyar Hizbullah ta Lebanon Sheikh Naim Qasem ya ce gwamnatin Lebanon ce ke da alhakin tabbatar da cewa Isra’ila ta mutunta yarjejeniyar tsagaita bude wuta a kasar ta Lebanon.
“Gwamnatin Lebanon, bayan tsawaita yarjejeniyar tsagaita bude wuta, ita ce ke da alhakin bibiyar lamarin da kuma matsa lamba kan kasashe masu sa ido da masu shiga tsakani don dakatar da hare-haren da Isra’ila ke kaiwa da keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta,” in ji shi a wani jawabi da ya yi ta gidan talabijin dazu.
Sheik Qasem ya ce kungiyar Hizbullah na taka-tsan-tsan don bai wa gwamnatin Lebanon damar sauke nauyin da ya rataya a wuyanta karkashin yarjejeniyar tsagaita bude wuta da Faransa da Amurka suka shiga tsakani a ranar 27 ga watan Nuwamba.
Ya yi gargadin cewa Isra’ila na ci gaba da karya yarjejeniyar tsagaita bude wuta.
Ya kamata Isra’ila ta janye dukkan sojojinta daga Lebanon a ranar 26 ga watan Janairu a karkashin yarjejeniyar tsagaita bude wuta da ta rattabawa hannu da kungiyar Hizbullah a watan Nuwamba.
Sai dai kuma ta ki yin hakan, inda aka tsawaita wa’adin zuwa ranar 18 ga watan Fabrairu.
Sama da ‘yan kasar Lebanon 80 ne kuma aka kashe a hare-haren da Isra’ila ke kaiwa kasar tun bayan da yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta fara aiki.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: yarjejeniyar tsagaita bude wuta
এছাড়াও পড়ুন:
Kasar Slovenia Da Haramta Tura Makamai Zuwa Haramtacciyar Kasar Isra’ila
Slovenia ta kasance Ƙasar Turai ta farko da ta ba da sanarwar hana tura makamai zuwa haramtacciyar kasar Isra’ila
Kasar Slovenia ta sanar da haramta musayar zirga-zirgan kayayyakin kasuwanci tsakaninta da haramtacciyar kasar Isra’ila musamman safarar makamai da kayan aikin soji zuwa Isra’ila, inda ta zama kasa ta farko ta Turai da ta dauki wannan matakin. Fira Minista Robert Gollub ne ya kaddamar da wannan matakin domin nuna adawa da mummunan bala’in jin kai a Gaza.
Wata sanarwa da ofishin fira ministan ya fitar ta tabbatar da hakan yayin wani taron majalisar ministocin da aka gudanar a farkon alhamis.
A karkashin sabon kuduri, duk makamai da kayan aikin soja an hana aikewa da su daga Slovenia zuwa haramtacciyar kasar Isra’ila, ko shigo da su daga haramtacciyar kasar Isra’ila, ko kuma jigilar su ta yankin Slovenia.
Wannan matakin dai ya zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da sukar matsalar jin kai a Gaza da kuma gazawar Tarayyar Turai wajen daukar kwararan matakai dangane da gwamnatin yahudawan sahayoniyya.
Sanarwar ta kara da cewa: Sakamakon rashin jituwar cikin gida da kuma rarrabuwar kawuna, a halin yanzu kungiyar Tarayyar Turai ba ta iya gudanar da wannan aiki na ladabtar da Isra’ila.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasar Spain Ta Bayyana Abin Da Ke Faruwa A Gaza A Matsayin Abin Kunya Ga Bil’Adama August 1, 2025 Iran ta yi watsi da zargin gwamnatocin turai na yunkurin kashe wasu mutane a kasashensu August 1, 2025 Mali da Rasha sun tattauna kan hadin gwiwar makamashi August 1, 2025 Afirka ta Kudu na shirin daukar matakan kauce wa tasirin harajin Amurka August 1, 2025 Haaretz: Sojojin Isra’ila 7 ne suka kashe kansu a watan Yuli August 1, 2025 Gaza: Mutane Da Dama Sun Yi Shahada A Yau Wasu Kuma Sun Jikkata August 1, 2025 Kungiyar AU Ta Yi Watsi Da Kafa Gwamnatin Adawa Da Kungiyar RSF Ta Yi A Sudan August 1, 2025 Shugaban Kasar Iran Zai Ziyarci Pakistan A Gobe Asabar August 1, 2025 Habasha Ta Kaddamar Da Shirin Shuka Bishiyoyi Miliyan 700 A Rana Daya August 1, 2025 Sayyid Abdulmalik Husi: Taimakon Da Ake Jefawa Gaza Ta Sama Yaudara Ce August 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci