Aminiya:
2025-05-02@04:25:27 GMT

Fasinjoji 30 sun ƙone ƙurmus a hatsarin mota a Ondo

Published: 2nd, February 2025 GMT

Aƙalla fasinjoji 30 ne suka ƙone ƙurmus a wani mummunan hatsarin mota da ya auku a kan titin Ore-Lagos a Jihar Ondo, bayan da wasu motoci biyu suka yi karo da juna sannan suka kama wuta.

Ganau, sun ce motocin suna tafiya zuwa Gabashin Najeriya ne, kuma suna gudun wuce ƙima kuma ga cunkoson ababen hawa a hanyar.

Osimhen ya maka ɗan jarida a kotu Abba ya karrama fitattun Kanawa 35

Hatsarin ya haddasa tashin wuta, inda mafi yawan fasinjojin suka ƙone ƙurmus.

“Motocin biyu sun yi karo, nan take suka kama da wuta,” in ji wata ganau, Misis Precision Oluwatuyi.

“Direbobin suna tafiya da gudu a hanyar da ba ta dace ba. Na ƙirga gawarwakin mutum 28 a waje , kuma wasu mutum biyu sun mutu a hanyarsu ta zuwa asibiti.”

Shugaban Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa (FRSC), Kwamanda Samuel Ibitoye, ya tabbatar da aukuwar hatsarin.

Ya ce sakaci da gudun wuce ƙima ne ya haddasa hatsarin.

“Direbobi su tuna cewa nauyin da ke kansu shi ne su kai fasinjoji inda za su je lafiya, ba su jefa rayuwarsu cikin hatsari ba,” in ji shi.

“Fasinjoji su ma su dinga gargaɗin direbobi kan tuƙin ganganci don kaucewa irin waɗannan musifu.”

An kai gawarwakin mamatan Asibitin Ƙasa da ke Ore, yayin da sauran mutum biyu da suka jikkata ake kula da su.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hatsarin mota Ƙonewa

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda ta kaya a wasannin kusa da na ƙarshe na Gasar Zakarun Turai

A yammacin ranar Talata Arsenal ta karbi bakuncin PSG a matakin wasan kusa da na karshe na gasar cin kofin zakarun Turai na bana.

An dai barje gumi ne a filin wasa na Emirates, inda PSG ta yi wa Arsenal ci daya mai ban haushi har gida.

DAGA LARABA: Asarar Da Hausawa Ke Tafkawa Sakamakon Bacewar Tatsuniya ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno

PSG ta fara cin ƙwallo ta hannun Ousmane Dembele a minti na huɗu da take leda, haka suka je hutu har da zagaye na biyu, amma Gunners ba ta farke ba.

Wannan shi ne karo na biyu da suka fuskanci juna a Champions League a kakar nan, inda Gunners ta yi nasarar cin 2-0 a Emirates a cikin watan Oktoba.

Arsenal da Paris Saint-Germain da Inter Milan da Barcelona su ne kungiyoyin da 4 da suka kai matakin zagayen daf da karshe na gasar.

A wannan Larabar ce kuma za a yi karon batta tsakanin Inter Milan da Barcelona, bayan kimanin shekara 15 da aka yi makamancin wannan karawar daf da karshe tsakanin ƙungiyoyin biyu a Gasar Zakarun Turai.

Inter Milan ce ta kai zagayen ƙarshe a 2010, sai dai wannan karon Barcelona na fatan lashe kofin bana da zarar ta fuskanci Arsenal ko Paris St Germain a watan gobe.

Sai dai, Barca da Inter sun fuskanci juna a gasar ta zakarun Turai a 2022/23, inda ta Italiya ta yi nasara 1-0 cikin Oktoban 2022 a wasa na biyu suka tashi 3-3 a Sifaniya.

Wannan shi ne karon farko da Barcelona ke fatan kai wa karawar ƙarshe a Champions League, tun bayan da ta lashe na biyar jimilla a 2015.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun ceto fasinjoji 99 daga hatsarin kwale-kwale a Ribas
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Kamuwa Da Cutar Hawan Jini Da Hanyoyin Magance Ta
  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  • Ma’aikatar Sharia A Nan Iran Zata Bayyana Abinda ya farsu A Tashar Jiragen Ruwa Na Shahid Rajae
  • Yadda ta kaya a wasannin kusa da na ƙarshe na Gasar Zakarun Turai
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • Sojoji Sun Harbe Mutane Biyu Har Lahira Da Ake Zargi Ɓarayin Mota Ne A Filato 
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Ta yi wa saurayinta ƙaryar shekarunta 27 maimakon 47
  • Shugaban Putin Na Rasha Ya Bada Sanarwan Tsagaita Wuta Da Ukraine Na Sa’o’ii 72