Aminiya:
2025-06-15@13:41:08 GMT

An yi taron Maulidin ƙasa duk da gargaɗin harin ’yan ta’adda a Kano

Published: 26th, January 2025 GMT

An gudanar da taron Maulidin ƙasa duk da gargaɗin da ’yan sanda suka yi kan barazanar harin ’yan ta’adda a Jihar Kano.

Aminiya ta ruwaito cewa, ’yan ɗariƙar Tijjaniyya daga sassan Nijeriya daban-daban sun halarci taron Maulidin na Shehu Ibrahim Inyas na shekara-shekara da aka gudanar a Filin Wasa na Sani Abacha da ke ƙwaryar Birnin Dabo.

An saki Falasɗinawa 200 da ke ɗaure a Isra’ila Tinubu zai tafi taron makamashi a Tanzania

Sai dai tun a jiya Juma’a ce mai magana da yawun ’yan sandan Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar da sanarwa mai ɗauke da gargaɗin cewa ’yan ta’adda na shirin kai hari a jihar saboda haka jama’a su ƙauracewa duk wani taro da shiga cunkoso.

Daga bisani Kwamishinan Labarai na Jihar Kano, Abdullahi Waiya, ya fitar da sanarwar cewa babu makawa sai taron ya gudana.

Ya ƙara da cewa gwamnatin jihar ba ta da labarin wata barazanar tsaro, don haka babu dalilin dakatar da taron ko tunanin mugun abu zai faru a wurin taron wanda aka shafe shekaru 39 ana gudanarwa duk shekara da mahalarta daga duk faɗin Nijeriya kuma an cika ka’idoji wajen shirya shi bana.

Bayan wannan martani da Kwamishinan ya yi ne rundunar ’yan sandan ta lashe amanta da cewa za ta bayar da cikakken tsaro a wurin taron.

Taron Maulidin karo na 39 ya samu halarcin Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima wanda ya jinjina wa ’yan ɗariƙar Tijjaniyya da suka kasance jakadun haɗin kai a tsakanin al’ummar Musulmi.

Shettima wanda ya kasance babban baƙo a yayin taron, ya bayyana ɗarikar Tijjaniyya a matsayin wadda ta yi tsayin-daka wajen koyar da addinin Islama a bisa tafarki madaidaici tsawon shekaru da dama.

Shettima wanda Babagana Fannami ya wakilta, ya jaddada irin jajircewar da ɗariƙar Tijjaniyya ta yi wajen koyar da kyawawan ɗabi’u na fiyayyen halitta Annabi Muhammad (SAW).

A nasa ɓangaren, Gwamna Abba Kabir Yusuf wanda ya kasance mai masaukin baƙi a yayin taron, ya yaba wa ɗariƙar Tijjaniyya musamman dangane da tabbatar da haɗin kai tsakanin sauran ɗariƙu a ƙasar.

Sarki Muhammadu Sanusi II wanda kuma shi ne shugaban ɗariƙar Tijjaniyya a Nijeriya, ya yi addu’ar haɗin kan musulmi a duniya tare da sauran mabiya addinai da aƙidu daban-daban.

Mataimakin Gwamnan Kwamared Gwarzo da Sarki Sanusi II da Gwamna Abba Kabir a wurin taron Maulidin

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Harin Isra’ila a kan Iran ya jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin zama dar-dar

An shiga yanayin zaman dar-dar a yankin Gabas ta Tsakiya bayan wasu munana hare-hare da Isra’ila ta kaddamar a kan tashoshin Nukiliya da manyan sojojin Iran a ranar Alhamis.

Hukumomin Isra’ila dai sun tabbatar da kai harin inda suka ce ya kunshi daruruwan jirage kan abin da suka kira da kololuwar wurin hada makaman Nukiliya na Iran da kuma manyan sojojinta.

NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna

Daga cikin manyan mutanen da ake zargin harin ya hallaka har da Manjo-Janar Hossein Salami, Shugaban Rundunar IRGC ta Iran da wasu manyan kwamandoji da manyan masana a tashar Nukiliyar.

Rundunar Tsaron Isra’ila (IDF) ta sanar da cewa jiragen yaki sama da 200 ne suka yi aikin kai hare-haren kuma sun kai su ne a muhimman wurare sama da 100 a Iran.

Sai dai jim kadan bayan labarin kai harin, Iran ta mayar da martani.

Kafofin yada labaran gwamnatin kasar sun rawaito cewa Iran ta harba jirage marasa matuka sama da 100 da suke hakon wurare daban-daban a cikin Isra’ila.

Kazalika, Shugaban addini na kasar, Ayatollah Ali Khomenei ya sha alwashin sai Isra’ila ta dandana kudarta.

Tuni rahotanni daga Isra’ila suka nuna yadda mutane suka shiga sayayya a kasuwanni ba ji ba gani suna adanawa saboda gudun abin da zai faru na martani.

Wasu hotuna da kamfanin dillancin labaran Faransa (AFP) ya wallafa sun nuna tituna a biranen Tel Aviv da Kudus sun dade.

Lamarin dai ya sa an soke tashi da saukar jirage zuwa kasashe da dama na yankin na Gabas ta Tsakiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
  • DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
  • Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
  • Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Harin Isra’ila a kan Iran ya jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin zama dar-dar
  • Mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu — Tinubu