Aminiya:
2025-05-01@01:05:21 GMT

Gobarar tankar mai ta yi ajalin mutum 18 a Enugu

Published: 26th, January 2025 GMT

An tabbatar da mutuwar aƙalla mutum 18 sakamakon hatsarin wata tankar mai da ta yi bindiga a Jihar Enugu.

Alƙaluman da mahukunta suka fitar ya nuna cewa hatsarin ya rutsa da mutum 31 ciki har da mutum 10 da suka samu raunuka daban-daban yayin da aka ceto wasu uku da suka tsallake rijiya da baya sai kuma mutum 18 ɗin da suka ƙone ƙurmus.

An yi taron Maulidin ƙasa duk da gargaɗin harin ’yan ta’adda a Kano An saki Falasɗinawa 200 da ke ɗaure a Isra’ila

Hakan na ƙunshe cikin sanarwa da mai magana da yawun rundunar hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa reshen Jihar Enugu, Olusegun Ogungbemide ya fitar da yammacin ranar Asabar.

Sanarwar ta bayyana cewa hatsarin wanda ya auku a sanadiyyar shanyewar birki ya shafi ababen hawa 17 da suka haɗa da tanka ɗaya, motoci 15 da kuma wani babu mai ƙafa uku.

Bayanai sun ce an shiga ruɗanin lokacin da tankar fetur ɗin ta yi bindiga, yayin da take saukowa daga wata hanya mai gangara a wani babban titi mai cunkoso a jihar ta Enugu.

TRT ta ruwaito cewa Kwamandan Hukumar Kare Haɗura ta Ƙasa a jihar, Franklin Agbakoba Onyekwere ya ce ya je wajen amma bai yi ƙarin bayani ba.

Tankar man ta kama da wuta ne ƙasa da mako guda bayan mutane fiye da 100 sun mutu yayin da wata tankar mai ta yi bindiga a Jihar Neja.

Kamfani Dillancin Labarai na Anadolu ya ba da rahoton cewa, Nijeriya ta fuskanci hatsarin tankar mai 172 inda mutane 1,896 suka mutu tun daga 2009, a yayin da matsalar ta fi muni a 2024, inda jimillar mutanen da suka mutu suka kai 266.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

An kashe mafarauta 10 a Adamawa

Aƙalla wasu mutum 10 mafarauta sun rasa rayukansu yayin aikin ceto a ƙauyen Kopire da ke Ƙaramar Hukumar Hong ta Jihar Adamawa.

Shugaban ƙungiyar mafarautan Nijeriya reshen Arewa maso Gabas, Shawulu Yohanna ne ya tabbatar wa Aminiya hakan a ranar Talata.

Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da Portugal

A cewarsa, ajali ya katse hanzarin mafarautan ne yayin wani arbatu da mayaƙan Boko Haram da suka yi musu kwanton ɓauna a jeji.

Ya bayyana cewa, mafarautan sun tunkari maharan ne bayan samun bayanan sirri da ke nuna cewa suna shirin kai hari.

“Abin takaicin shi yadda ake yi wa Gwamnan Borno ƙafar ungulu a ƙoƙarin da yake yi na ganin an kawo ƙarshen wannan hare-hare a yankin,” in ji shi.

Yohanna ya bayyana damuwa kan yadda mayaƙan Boko Haram ke ci gaba da ƙara ƙarfi a bayan nan da ke zama abin fargaba ga mazauna yankunan da abin ya shafa.

“Mun samu labarin cewa wani jirgi mai saukar ungulu ne yake jigilar mayaƙan daga sansaninsu zuwa wuraren da suke sheƙe ayarsu ba tare fuskantar wata tirjiya ba.

“Amma ina mai tabbatar da cewa muddin Gwamnatin Tarayya ta ɗauki mataki ta hanyar tanadar makamai na zamani, za a kawo ƙarshen waɗannan maƙiya cikin lokacin ƙanƙani.”

Ya roƙi Gwamnatin Tarayya da ta tanadar wa mafarauta da ’yan sa-kai manyan makamai na zamani domin kawo ƙarshen mayaƙan Boko Haram a yankin.

Wannan harin dai na zuwa ne ƙasa da sa’o’i 12 da wasu ’yan ta’adda suka kashe fiye da mutum 30 ciki har da mata da ƙananan yara a ƙananan hukumomin Kala Balge da Gambarou Ngala da ke jihar.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  • Ma’aikatar Sharia A Nan Iran Zata Bayyana Abinda ya farsu A Tashar Jiragen Ruwa Na Shahid Rajae
  • Riza’i: Babu Hannun  Waje A Cikin Hatsarin Da Ya Faru A Tashar Ruwa Ta Shahid Raja’i
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Shirya Fara Tantance ‘Yan Fansho
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • An kashe mafarauta 10 a Adamawa
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno
  • Jihar Kebbi Ta Kammala Shirye-shiryen Aikin Hajjin 2025
  • Hajjin 2025: Gwamna Namadi Ya Nada Sarkin Kazaure Amirul Hajj