Aminiya:
2025-09-18@00:57:02 GMT

Gobarar tankar mai ta yi ajalin mutum 18 a Enugu

Published: 26th, January 2025 GMT

An tabbatar da mutuwar aƙalla mutum 18 sakamakon hatsarin wata tankar mai da ta yi bindiga a Jihar Enugu.

Alƙaluman da mahukunta suka fitar ya nuna cewa hatsarin ya rutsa da mutum 31 ciki har da mutum 10 da suka samu raunuka daban-daban yayin da aka ceto wasu uku da suka tsallake rijiya da baya sai kuma mutum 18 ɗin da suka ƙone ƙurmus.

An yi taron Maulidin ƙasa duk da gargaɗin harin ’yan ta’adda a Kano An saki Falasɗinawa 200 da ke ɗaure a Isra’ila

Hakan na ƙunshe cikin sanarwa da mai magana da yawun rundunar hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa reshen Jihar Enugu, Olusegun Ogungbemide ya fitar da yammacin ranar Asabar.

Sanarwar ta bayyana cewa hatsarin wanda ya auku a sanadiyyar shanyewar birki ya shafi ababen hawa 17 da suka haɗa da tanka ɗaya, motoci 15 da kuma wani babu mai ƙafa uku.

Bayanai sun ce an shiga ruɗanin lokacin da tankar fetur ɗin ta yi bindiga, yayin da take saukowa daga wata hanya mai gangara a wani babban titi mai cunkoso a jihar ta Enugu.

TRT ta ruwaito cewa Kwamandan Hukumar Kare Haɗura ta Ƙasa a jihar, Franklin Agbakoba Onyekwere ya ce ya je wajen amma bai yi ƙarin bayani ba.

Tankar man ta kama da wuta ne ƙasa da mako guda bayan mutane fiye da 100 sun mutu yayin da wata tankar mai ta yi bindiga a Jihar Neja.

Kamfani Dillancin Labarai na Anadolu ya ba da rahoton cewa, Nijeriya ta fuskanci hatsarin tankar mai 172 inda mutane 1,896 suka mutu tun daga 2009, a yayin da matsalar ta fi muni a 2024, inda jimillar mutanen da suka mutu suka kai 266.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

 

A yayin samamen, kakakin ‘yansandan Neja ya ce an kama mutane shida a wurin da ake hakar ma’adinan yayin da wasu kuma suka tsere.

 

Abiodun ya bayyana sunayen wadanda ake cafken da Aliyu Rabiu, Samaila Ibrahim, Sadiku Auwal, Ibrahim Babangida, Musa Adamu da Sani Hassan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara