Hatsarin kwale-kwale ya yi ajalin mutum 29 a Neja
Published: 3rd, September 2025 GMT
Aƙalla mutum 29 sun rasu a wani hatsarin kwale-kwale da ya auku a gabar kogin Malale da ke cikin Karamar Hukumar Borgu a Jihar Neja.
Aminiya ta ruwaito cewa, kwale-kwalen wanda ke ɗauke da fasinjoji 90, ya tashi ne daga Tugan Sule da ke yankin Shagunu, inda ya nufi Dugga domin zuwa wata ta’aziyya.
Dalilin da Najeriya ba ta jin tsoron matakan Trump — Tinubu Boko Haram ba kiristoci kaɗai suke kashewa a Arewa Maso Gabas ba — NdumeMajiyoyi sun bayyana cewa cikin waɗanda suka mutu har da mata da ƙananan yara, kuma zuwa yanzu an gano gawarwaki 29, yayin da aka ceto mutum 50 da ransu, sai kuma wasu mutum biyu da har yanzu ake ta ƙoƙarin lalubo su.
Daraktan Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA), Abdullahi Baba Arah, wanda Aminiya ta tuntuba ya tabbatar da aukuwar lamarin.
Haka kuma, wani babban jami’in Hukumar Kula da Hanyoyin Ruwa na Ƙasa (NIWA) a yankin, Akapo Adeboye, ya tabbatar da hakan ta wayar tarho.
A cewar Daraktan NSEMA: “Mun samu rahoton hatsarin kwale-kwale a wani gari mai suna Gausawa da ke yankin Malale a Borgu.
“Bisa bayanan da muka samu, kwale-kwalen ya tashi daga Tugan Sule da ke cikin gundumar Shagunu wanda yake ɗauke da mutum 90 ciki har da mata da yara, da nufin zuwa gaisuwar rasuwa a Dugga.
“Wannan lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11:30 na safiyar ranar Talata, 2 ga Satumba, 2025, a sanadiyar lodin fasinjoji fiye da ƙima sannan kuma kwale-kwalen ya ci karo wani da kututturen itace.”
Ya ƙara da cewa jami’ai na ci gaba da aikin ceto domin gano waɗanda suka bace.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Neja Kwale kwale kwale kwale
এছাড়াও পড়ুন:
DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu
Hukumar Tsaron Farin Kaya a Nijeriya DSS, ta gurfanar da fitaccen ɗan gwagwarmayar nan, Omoyele Sowore a kotu.
A ƙunshin ƙarar da DSS ta gabatar a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta haɗa da shafukan sada zumunta na X da kuma Facebook, inda take zarginsu da ba da ƙofar aibata Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Bida Poly ta sa sojoji kula da jarrabawar ɗalibai Kukan al’umma kan lalacewar hanyar DukkuDarekan shigar da ƙara na Ma’aikatar Shari’a ta Tarayya, M.B Abubakar da wasu lauyoyi huɗu —M.E. Ernest da U.B. Bulla da C.S. Eze da kuma E.G. Orubor, ne suka shigar da ƙarar a madadin Gwamnatin Tarayya da kuma hukumar ta DSS.
DSS wadda ta kafa hujja da sashe na 24 da ke cikin kundin dokokin yanar gizo, ta ce Sowore ya yi amfani da shafukansa na dandalan sada zumunta na X da Facebook wajen wallafa wani saƙo da ke cin mutuncin Shugaba Tinubu.
Tun dai a farkon watan nan ne DSS ta buƙaci goge wani saƙo da ɗan gwagwarmayar ya wallafa wanda ta riƙa a matsayin bayanan ƙarya, cin zarafi ta yanar gizo da kalaman haddasa ƙiyayya, waɗanda kuma ta ce na iya haddasa rikici su kuma ɓata sunan Najeriya a ƙasashen waje.
Sai dai har zuwa ranar Litinin, 15 ga watan Satumba, babu wani mataki da aka ɗauka na goge saƙon da DSS ɗin ta buƙata.