Ƙungiyar masu kafafen yada labarai na Arewa za ta daukaka kara kan hukuncin kotu a kan tashar Arewa24
Published: 3rd, September 2025 GMT
Ƙungiyar masu kafafen yaɗa labarai ta Arewacin Najeriya (NBMOA) ta yi watsi da hukuncin da Babbar Kotun Tarayya ta yanke na yin watsi da ƙarar da ta shigar a kan tashar Arewa24, inda ta ce za ta ɗaukaka ƙara.
Idan za a iya tunawa, Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, a watan Agusta, ta yi watsi da karar da kungiyar NBMOA ta shigar a kan Arewa24, saboda “rashin hukunci da rashin cancanta”, kamar yadda aka gani a cikin kwafin takardar hukuncin kotun (CTC).
Kotun, a cikin wata sanarwa da ta fitar, ta tabbatar da cewa AREWA24 tana gudanar da harkokinta ne bisa ƙa’ida, kuma ba ta da hurumin samun ƙarin lasisin gudanar da ayyukanta, ba tare da karya wata doka ba.
Sai dai, Shugaban NBMOA, Alhaji Ahmed Tijjani Ramalan, a cikin wata sanarwar da ya raba wa manema labarai a ranar Talata, ya bayyana hukuncin da alƙalin kotun, Mai Shari’a Omotosho ya yanke da cewa ya zama tamkar “halatta tashoshin ƙasashen waje marasa lasisi”, wanda ya yi musu laƙabi da matsayin ‘kaska’, a masana’antar yaɗa labarai ta Najeriya”.
Ƙungiyar ta dage cewa, Arewa24 tashar talabijin mallakar Amurka, wacce ke da ofisoshi a Kano da Legas, na watsawa da yaɗa shirye-shiryenta da wasannin kwaikwayo na Hausa, wanda ake yi wa laƙabi da shirye-shiryen duniya, ana shigo da su zuwa gidajen talabijn na Najeriya ta DStv, GOtv da StarTimes.
A cewar ƙungiyar, duk shirye -shiryen da tashar take watsawa ba ta da lasisi da Hukumar Kula da Kafafen Watsa Labarai ta Ƙasa (NBC).
Kungiyar ta kuma ce tashar tana cajin kuɗin tallace-tallace ba bisa ƙa’ida ba, baya ga farashin da suke caza da ya zarce tunani, kuma ya keta wajibcin da aka sanya wa masu watsa shirye-shiryen gida.
NBMOA ta kuma zargi AREWA24 da watsa shirye-shirye da basu dace ba, tana mai gargaɗin cewa hukuncin da kotun ta yanke zai bai wa tashar damar ci gaba da aiwatar da shirye-shiryen da suke lalata tsarin Gwamnatin Tarayya, tare da yin barazana ga tashoshin cikin-gida, wanda ke fama da ƙasa mai tsanani.
Ta ƙara da cewa ana tilasta wa masu watsa shirye-shirye na asali, waɗanda ke bin doka, barin kasuwanci.
Ƙungiyar tace wannan hukuncin ya halatta kafafen yaɗa labarai na ƙasashen waje da basu da lasisi su riƙa yaɗa shirye-shiryen da suka ci karo da al’adunmu, da ɗabi’un al’umman ƴan Arewa.
“Ba za mu tsaya haka kawai ba yayin da tashohin ƙasashen waje ke yin katsalandan a harkar yaɗa labarai, da kuma lalata masana’antarmu,” in ji Ramalan.
Tuni dai Ƙungiyar NBMOA ta shigar da ƙara a Kotun Ɗaukaka ƙara da ke Abuja, inda ta buƙaci da a yi mata adalci, inda kuma ta nemi da a soke hukuncin da waccan kotu ta zartar don tabbatar da adalci.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Arewa 24 shirye shiryen yaɗa labarai shirye shirye
এছাড়াও পড়ুন:
An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
Rundunar Sojin Kasa ta Najeriya ta sanar da samun nasarar cafke Ifeanyi Eze Okorienta, wanda aka fi sani da “Gentle de Yahoo”, ɗaya daga cikin manyan kwamandojin ƙungiyar IPOB, a wani samame da ta kai a yankin kudu maso gabashin ƙasar.
Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya NAN ya ruwaito wata majiya daga hedikwatar rundunar sojin tana cewa an cafke Gentle de Yahoo ne yayin farmakin da sojojin suka kai a ranar Lahadi kan sansanonin ’yan ƙungiyar a cikin wani dajin da ke ƙaramar hukumar Okigwe a Jihar Imo.
An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a RibasMajiyar ta ce a yayin cafke jagoran na IPOB, an kuma ƙwato makamai da dama daga hannunsa, ciki har da bindigogi kirar Turai, harsasai, kakin sojoji da na ’yan sanda.
“Cafke wannan kwamanda babban ci gaba ne wajen murƙushe ayyukan ta’addanci da ƙungiyar IPOB ke aikatawa, musamman a yankunan da suke hana zaman lafiya,” in ji majiyar.
Kungiyar IPOB, wacce ke fafutukar ballewa daga Najeriya don kafa ƙasar Biyafara, ta kasance a gaba-gaba wajen aikata hare-hare da ta da tarzoma a jihohin kudu maso gabas, musamman ta hannun sashen rundunar da suka kafa da kansu mai suna Eastern Security Network (ESN).
Ana dai zargin cewa Eze yana ɗaya daga cikin jagororin da ke tsara harin kwantan bauna, da hana zirga-zirga a wasu sassan yankin, wanda hakan ya jefa al’umma cikin fargaba da zaman ɗar-ɗar.
Wannan nasara na zuwa ne bayan makonni kaɗan da wata kotu a ƙasar Finland ta yanke wa Simon Ekpa, wani babban jigo a ƙungiyar IPOB, hukuncin ɗaurin shekaru shida a gidan yari kan laifukan da suka shafi ta’addanci da tayar da zaune tsaye.
Masu sharhi na ganin cewa cafke Gentle de Yahoo wata alama ce da ke nuna cewa ana shirin ragargaza ƙungiyar IPOB gaba ɗaya, duk da cewar har yanzu akwai sauran rina a kaba, musamman ganin cewa wasu sassan yankin na ci gaba da fuskantar matsalolin tsaro.