Aminiya:
2025-11-03@06:25:47 GMT

An ƙone ‘ɓarawon’ babur ƙurmus a Binuwai

Published: 3rd, September 2025 GMT

Jama’ar gari sun kone wani mutum da ake zargi da satar babur da safiyar Talata a kan titin Ibrahim Kashim Road da ke Makurdi, babban birnin jihar.

Wani ganau da ya ce sunansa Andrewa Tergu, ya shaida wa wakilinmu cewa fasinjoji biyu ne suka hau kan babur din wani dan acaba da nufin ya kai su unguwar Railway Quarters a garin na Makurdi.

’Yan daba sun tarwatsa taron neman zaman lafiya na dattawan Katsina Gwamnatin Tarayya ta ayyana Juma’a a matsayin ranar hutun Mauludi

Sai dai dan acabar bai sani ba, ashe akwai wani mutum daya da yake tsaye a daidai inda zai sauke fasinjojin, inda yake tsaye yana jiran su isa.

Da isar su, sai ya sa hannun a aljihu kamar zai ciro kudi ya sallami dan acabar, amma sai ya zaro almakashi ya caccaka masa a wurare daban-daban.

Andrew ya ce dan acabar ya fado daga kan babur din nasa inda ya rika ihun neman taimakon mutanen gari.

“A kokarin barayin na guduwa ne daya daga cikinsu ya fado daga kan babur din da suka sata, inda mutane suka far masa da duka, suka jawo shi kan titi sannan suka banka masa wuta,” in ji Andrew.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoton dai, lokacin da wakilinmu ya ziyarci inda wurin ya faru, ya iske jami’an Hukumar Tsaftace Muhalli ta Jihar suna kokarin share wurin da aka kone wanda ake zargi da satar babur din.

Da muka tuntubi kakakin rundunar ’yan sandan jihar, DSP Udeme Edet, ta tabbatar da faruwar lamarin sannan ta yi alkawarin ba wakilinmu cikakken bayani daga bisani.

Sai dai har zuwa lokacin hada wannan rahoton ba ta kai ga yin hakan ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Barayin babur Binuwai

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

A jawabinsa yayin taron, Gwamna Sani ya gabatar da kasida mai taken: “Gina Haɗin Gwiwa Domin Ci Gaban Kowa”, inda ya bayyana yadda Jihar Kaduna ke ci gaba da samun nasara a fannoni da dama kamar gyaran birane, bunƙasa noma, da tsarin tallafiwa jama’a.

 

Gwamnan Ya ce tsarin ci gaban jihar yana dogara ne kan faɗaɗa damar tattalin arziki da kare marasa ƙarfi, da ƙarfafa jama’a su samu nasara a rayuwarsu.

 

Gwamna Uba Sani, ya kuma halarci shirin baje koli na birnin Dubai mai taken : “Sauya Arewa a Nijeriya: Jagoranci, Ƙirƙira, da Tasirin Zamantakewa”, inda nan ma ya jaddada cewa jagoranci mai nagarta da amfani da fasaha a mulki suna da matuƙar muhimmanci wajen buɗe damarmaki ga mutane da birane.

 

A yayin taron, Gwamnan ya gudanar da wata ganawa ta musamman da Marwan Bin Galita, Darakta Janar na birnin Dubai inda suka tattauna batutuwan haɗin gwiwa a fannin kirkirar makamashin sharar gida da kula da sharar gida ta zamani, da kuma tsare-tsaren gine-ginen birane na zamani.

 

A ganawar, duk Bangarorin biyu sun amince da zurfafa haɗin kai a fannin fasaha da musayar ƙwarewa domin tallafawa sauyin jihar Kaduna zuwa tattalin arzikin mai ɗorewa.

 

Gwamna Sani ya bayyana cewa halartar Jihar Kaduna a taron (APCS 2025) na nuna shirin jihar na shiga sahun ƙasashen duniya wajen yin haɗin kai, ƙirƙira, da zama abin koyi a fannin ci gaba mai ɗorewa da ci gaban kowa da kowa a fadin Nijeriya da ma duniya baki ɗaya

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi October 31, 2025 Labarai Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede October 31, 2025 Labarai Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa
  • Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA
  • Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP