Aminiya:
2025-11-02@18:37:34 GMT

’Yan daba sun tarwatsa taron neman zaman lafiya na dattawan Katsina

Published: 3rd, September 2025 GMT

Wasu matasa da ake zargin ’yan daba ne sun tarwatsa wani taro da dattawan Katsina suka shirya a kan zaman lafiya a jihar jim kadan da fara shi ranar Talata.

Hakan na zuwa ne ’yan kwanaki kadan bayan an kai irin makamantan irin wadannan hare-haren a kan tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa’i da tsohon Ministan Shari’a, Abubakar Malami.

Wata kungiya mai rajin tabbatar da zaman lafiya a jihar mai suna Katsina Security Community Initiative ce ta shirya taron na ranar Talata da nufin lalubo bakin zaren kan matsalar tsaron da ta addabi jihar.

Gwamnatin Tarayya ta ayyana Juma’a a matsayin ranar hutun Mauludi Tinubu ya dawo da shugaban NTA da ya sauke

Katsina dai ta shafe tsawon shekaru tana fama da matsalolin tsaro na ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane don neman kudin fansa, lamarin da ya yi sanadin kisan mutane da dama tare da rasa dukiyoyi na miliyoyin Naira.

Sai dai an kai harin ne a daidai lokacin da Gwamnan jihar, Dikko Umar Radda ya jagoranci tawagar dattawan jihar zuwa Fadar Shugaban Kasa Bola Tinubu, inda suka sa labule kan matsalar tsaron jihar.

Shi dai taron na Katsina ya tattara kwararru da dama, cikinsu har da tsofaffin sojoji da ’yan sanda da malamai da kuma sauran shugabannin al’umma.

To sai dai an fara samun matsala a taron ne lokacin da wanda ya shirya shi, Dr Bashir Kurfi, ya fara jawabi a kan matsalar tsaron jihar.

A cikin jawabin nasa dai, ya yi zargin cewa kananan hukumomin jihar da dama yanzu sun kusa zama kufai, yayin da harkokin tattalin arziki da noma da kiwo da ma harkokin karatu suka durkushe saboda hare-haren ’yan bindigar.

Amma yana cikin jawabi ne sai wani ya tashi ya katse shi, inda ya ce gwamnatin jihar na niya bakinta wajen magance matsalar, amma su ba sag ani, don haka ba za su bar shi ya ci gaba da magana ba.

Sun kuma zargi Dr Kurfi da cewa dan adawa ne saboda a zamanin gwamnatin da ta gabata bai yi irin wadannan maganganun ba, inda suka kira shi da makiyin gwamnati mai ci.

Da aka bukaci mai maganar da ya jira lokacin yin tsokaci kafin ya yi bayani, sai wasu takwarorinsa ma suka mike, nan take wajen kuma ya yamutse.

A nan ne suka fara jifa da kujeru har suna kai wa wasu daga cikin ’yan jaridar da ke daukar rahoto a wajen hari.

Bayanai sun nuna an girke ’yan dabar a ciki da wajen wurin tarom, yayin da wasu daga cikinsu suka rika nuna wukake suna barazanar caka wa duk wanda suke gani a matsayin makiyin gwamnatin jihar.

Sai dai duk da harin da ya tarwatsa taron, wanda ya shirya shi ya ce ba za su saduda ba.

Ya kuma zargi gwamnatin jihar da daukar nauyin ’yan dabar, inda ya ce dukkansu suna da alaka da gwamnatin, domin da bakinsu ma sun fadi hakan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan daba Taron zaman lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare

A ranar 30 ga wata ne shugabannin kasashen Sin da Amurka suka gana da juna a birnin Busan na kasar Koriya ta Kudu, lamarin da ya jawo hankulan kasa da kasa, inda shugabannin 2 suka yi musayar ra’ayoyi dangane da huldar da ke tsakanin kasashen 2 da al’amuran da suka jawo hankulansu. Sun amince da inganta hadin gwiwar kasashen 2 a fannonin tattalin arziki da cinikayya da makamashi da kyautata mu’amalar al’adu.

A yayin ganawar, shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya jaddada cewa, yana son hada kai da shugaba Donald Trump na Amurka wajen aza harsashi mai kyau na raya huldar da ke tsakanin kasashen 2, tare da samar wa juna kyakkyawan yanayin samun ci gaba. A nasa bangaren, shugaba Trump ya ce, kasar Sin, abokiyar Amurka ce mafi girma. Kasashen 2 za su hada kansu wajen samun nasarar gudanar da manyan ayyuka da dama a duniya. Nan gaba Amurka da Sin za su kara samun nasara a hadin gwiwarsu. Shugabannin 2 sun amince su rika yin mu’amala da juna. Shugaba Trump yana sa ran kai ziyara a kasar Sin a farkon shekara mai zuwa, ya kuma gayyaci shugaba Xi ya ziyarci Amurka.

Masharhanta sun yi nuni da cewa, ganawar shugabannin 2 ta sanya tagomashi kan kyautatuwar huldar da ke tsakanin Sin da Amurka, ta kuma tsara manufar raya huldar kasashen 2 a nan gaba, tare da kwantar da hankulan kasashen duniya.

Abubuwan tarihi da kuma hakikanin abubuwa sun nuna cewa, wajibi ne Sin da Amurka su zama abokan juna. A wannan muhimmin lokaci, ganawar da shugabannin kasashen 2 suka yi ta sake tsara manufar kyautata da raya huldar da ke tsakanin kasashen 2. Muddin kasashen 2 suka aiwatar da muhimman daidaito da shugabannin 2 suka cimma, da mutunta ruhin adalci, tare da martaba juna da samun moriyar juna, to, za a raya huldar da ke tsakanin kasashen 2 ba tare da wata matsala ba, da kuma kara samar da kwanciyar hankali da tabbaci a duniya. (Tasallah Yuan)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi October 31, 2025 Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo October 30, 2025 Daga Birnin Sin Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma  October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
  • Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari