Aminiya:
2025-11-03@07:52:10 GMT

’Yan bindiga sun yi hatsari bayan karbar kudin fansa

Published: 19th, August 2025 GMT

Wasu masu garkuwa da mutane sun yi hatsarin mota a hanyarsu ta zuwa rabon kudin fansar mutanen da suka sace a Jihar Nasarawa.

Jami’an tsaro sun kwato bindigogi uku da tsabar kudi Naira miliyan 6.9 daga motar ’yan bingidar bayan hatsarin motar a yankin Garaku, daura da wani shingen bincike na Jami’an Kula da Lafiyar Ababen Hawa (VIO)

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Nasarawa ta ce ta kwato makamai masu haɗari da kuɗi sama da naira miliyan shida, bayan wani haɗari da ya faru a kusa da Angwan Mayo.

’Yan sanda daga yankin Garaku sun ce da misalin ƙarfe 9:08 na safe, suka samu kiran gaggawa dangane da haɗarin motar kirar Opel Vectra wadda shaidu suka ce mutane biyu da ke cikinta  sun tsere.

Mutane 62 da aka sace sun tsere daga hannun ’yan bindiga a Katsina Albashin sanatoci 109 zai biya farfesoshi 4,709

Da isar jami’an wurin, sun tarar da taron jama’a, inda wani jami’in VIO ya mika bindigogin da kuma kudi Naira miliyan 6.9 da aka samo daga cikin motar.

Daga nan ’yan sanda da haɗin gwiwar sojoji shiga farautar waɗanda suka tsere, inda suka yi nasarar ɗaya daga cikinsu mazaunin yakin Barkin Ladi a Jihar Filato, bayan ya tsere zuwa daji.

Wanda ake zargin ya amsa cewa yana cikin wata ƙungiyar masu garkuwa da mutane guda bakwai, waɗanda suka sace wani lauya a yankin Nyanya, Abuja.

Ya bayyana cewa shi da abokinsa suna kan hanyarsu ta zuwa Jos domin rabon kuɗin fansa da suka karɓa kafin haɗarin ya faru.

An mika shi tare da abubuwan da aka kwato zuwa Sashen Binciken Laifuka na Jihar da ke Lafia, kamar yadda Kwamishinan ’Yan Sanda CP Shettima Jauro Mohammed ya umarta.

Kakakin rundunar, SP Ramhan Nansel, ya yaba da wayar da kan jama’a, tare da tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da aiki tare da sauran hukumomin tsaro domin kawar da laifuka a jihar da kewaye.

Ya kuma roƙe su da su ci gaba da ba da goyon baya ga ’yan sanda da sauran hukumomin tsaro.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Garkuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

“Amurka ba za ta tsaya kawai tana kallo ba yayin da irin waɗannan ta’addancin ke faruwa a Nijeriya da sauran ƙasashe.

“Mun shirya, muna da ƙarfi da niyyar kare Kiristoci a faɗin duniya,” in ji Trump.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano October 31, 2025 Manyan Labarai Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi October 31, 2025 Manyan Labarai Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fursunan da aka yanke wa hukuncin kisa ya tsere daga gidan yari a Yobe
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare