Aminiya:
2025-09-17@22:12:33 GMT

’Yan bindiga sun yi hatsari bayan karbar kudin fansa

Published: 19th, August 2025 GMT

Wasu masu garkuwa da mutane sun yi hatsarin mota a hanyarsu ta zuwa rabon kudin fansar mutanen da suka sace a Jihar Nasarawa.

Jami’an tsaro sun kwato bindigogi uku da tsabar kudi Naira miliyan 6.9 daga motar ’yan bingidar bayan hatsarin motar a yankin Garaku, daura da wani shingen bincike na Jami’an Kula da Lafiyar Ababen Hawa (VIO)

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Nasarawa ta ce ta kwato makamai masu haɗari da kuɗi sama da naira miliyan shida, bayan wani haɗari da ya faru a kusa da Angwan Mayo.

’Yan sanda daga yankin Garaku sun ce da misalin ƙarfe 9:08 na safe, suka samu kiran gaggawa dangane da haɗarin motar kirar Opel Vectra wadda shaidu suka ce mutane biyu da ke cikinta  sun tsere.

Mutane 62 da aka sace sun tsere daga hannun ’yan bindiga a Katsina Albashin sanatoci 109 zai biya farfesoshi 4,709

Da isar jami’an wurin, sun tarar da taron jama’a, inda wani jami’in VIO ya mika bindigogin da kuma kudi Naira miliyan 6.9 da aka samo daga cikin motar.

Daga nan ’yan sanda da haɗin gwiwar sojoji shiga farautar waɗanda suka tsere, inda suka yi nasarar ɗaya daga cikinsu mazaunin yakin Barkin Ladi a Jihar Filato, bayan ya tsere zuwa daji.

Wanda ake zargin ya amsa cewa yana cikin wata ƙungiyar masu garkuwa da mutane guda bakwai, waɗanda suka sace wani lauya a yankin Nyanya, Abuja.

Ya bayyana cewa shi da abokinsa suna kan hanyarsu ta zuwa Jos domin rabon kuɗin fansa da suka karɓa kafin haɗarin ya faru.

An mika shi tare da abubuwan da aka kwato zuwa Sashen Binciken Laifuka na Jihar da ke Lafia, kamar yadda Kwamishinan ’Yan Sanda CP Shettima Jauro Mohammed ya umarta.

Kakakin rundunar, SP Ramhan Nansel, ya yaba da wayar da kan jama’a, tare da tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da aiki tare da sauran hukumomin tsaro domin kawar da laifuka a jihar da kewaye.

Ya kuma roƙe su da su ci gaba da ba da goyon baya ga ’yan sanda da sauran hukumomin tsaro.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Garkuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 

Yarjejeniyar, a cewar daukacin mahalarta taron, ta nuna wani gagarumin mataki na kawo karshen tashe-tashen hankula, garkuwa da mutane da satar shanu a Arewa maso Yamma, da kuma yankin Arewa.

 

Yarjejeniyar wacce Mai Maradin Katsina da Hakimin Kurfi, Alhaji Mansur Amadu Kurfi, da shugaban karamar hukumar, Babangida Abdullahi Kurfi suka shirya, ta gudana ne a dajin Wurma, inda ake fama da rashin tsaro.

 

Manyan jagororin ‘yan bindigan da suka hada da Alhaji Usman Kachalla Ruga da Sani Muhindinge da Yahaya Sani (Hayyu) da kuma Alhaji Shu’aibu duk sun yi alkawarin tsagaita wuta.

 

Daga baya suka sako mutanen da suka kama kuma suka bar manoma su koma gonakansu ba tare da wata barazana ba.

 

Sai dai kasa da wata guda da kulla yarjejeniyar, an tattaro cewa ‘yan bindigar sun sake kai hari a Zamfara inda suka yi awon gaba da masallata da dama.

 

Wata majiya ta cikin garin, ta shaida cewa, harin ya afku ne a lokacin sallar asuba da misalin karfe 5:30 na safe, inda ‘yan bindigar suka afkawa masallacin, suka kewaye shi, sannan suka tattara masallatan zuwa daji.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
  • Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff