Saudiya Ta Yi Amfani Da Fasahar AI Don Sauwaka Ayukan Hajjin Shekara ta 2025
Published: 6th, June 2025 GMT
Gwamnatin kasar Saudiya ta yi amfani da fasahar kirkirarren tunani ko (AI) don sauwakawa kanta da kuma mahajjata a hajjin wannan shekara ta 2025, kama daga kula da cinkoson mutane, kiyaye lafiyar mahajjata da haka kuma ta kyautata ayyukan mahajjata a cikin nutsuwa da rashin damuwa.
Jaridar ArabNews ta kasar Saudiya ta bayyana cewa tare da wannan fasahar ta kula da zafin dukkan wuraren da mahajjata zuwa zuwa da kuma hana cinkoson mutane a kewayen Kaaba da sauran wurare.
Jami’I mai kula da bangaren kirkirerren fasaha wato AI na aikin Ajjin bana ya shaidawa Jaridar ArabNews kan cewa sun kirkiro abubuwa da dama don sawwaka aikin hajji ga mahajjata da kuma khidimomin da kasar saudiyya take yiwa mahajjata, Ya ce an yi amfani da wannan fasahar a masallacin Madina da kuma na dakin nKaaba.
Ya ce jami’an shige da fice na kasar Saudiya suna amfani da kayakin aiki na zama a ayyukansu . sannan suna aikin bincike da kansu a tashoshin jiragen sa 11 a kasashen 7 a duniya, inda suke tabbatar da cewa mahajjaci ya cancanci ya je aikin hajji tun daga kasarsu kafin ya shiga jirgi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Mahajjata kusan miliyan biyu na hawan Arfa a Saudiyya
Miliyoyin alhazai ciki har da ’yan Najeriya ne suka taru a Dutsen Arfa domin tsayuwa a yayin Aikin Hajjin bana duk da tsananin zafin ranar da ake fama da shi a kasar Saudiyya.
Ministan Aikin Hajji na kasar dai ya shawarci mahajjatan da su kasance a cikin tantinansu tun daga tsakain karfe 10 na safe zuwa karfe 4:00 na yamma, saboda tsananin zafin rana.
Ko a ranar Lahadi sai da Hukumar Hasashen Yanayi ta Kasar (NCM) ta yi gargadin cewa zafin zai iya kai wa ma’auni 47, inda ta shawarce su da su dauki matakan kariya.
Musulman Kudancin Kaduna sun yi taron addu’ar zaman lafiya Kotu ta aike da ɗan Tiktok gidan yari kan yin shigar mata a KanoTo sai dai duk da haka, mahajjata maza da mata sun rika yin tattaki daga wurare masu nisa domin taruwa a dutsen domin yin addu’a.
Da yake zantawa da wakilinmu, daya daga cikin mahajjatan Najeriya, Yusuf Hassan, cewa yana sane da shawarar da aka bayar, amma duk da haka zuciyarsa ba za ta iya natsuwa ba sai yah au dutsen na rahama.
“Na yi wa kaina alkawarin cewa sai nah au Dutse Arafat na yi addu’a a duk lokacin da Allah y aba ni dama. Saboda haka ni burina ya cika,” in ji shi.
Sai dai wakilin namu ya shaida cewa akasarin mahajjatan sun yi amfani da shawarar, inda suka tsaya a cikin tantinan nasu suna karatun alkur’ani da salloli da addu’o’i.
Kazalika, wakilin namu ya ce ya hangi jirage masu saukar angulu na shawagi a sararin samaniya, yayin da ’yan sanda da sauran jami’an tsaro ke ci gaba da sintiri suna yi wa mahajjatan jagora.
Dutse Arafat dai na da tarihi sosai a Musulunci saboda a nan ne tarihi ya nuna Annabi Muhammad (S.A.W) ya gudanar da hudubarsa ta bankwana.
Daga dutsen ne kuma za su koma Muzdalifa da yamma, su kwana a can, kashegari da safe kuma su fara jifan Shedan.