HausaTv:
2025-06-22@18:11:55 GMT

Saudiya Ta Yi Amfani Da Fasahar AI Don Sauwaka Ayukan Hajjin Shekara ta 2025

Published: 6th, June 2025 GMT

Gwamnatin kasar Saudiya ta yi amfani da fasahar kirkirarren tunani ko (AI) don sauwakawa kanta da kuma mahajjata a hajjin wannan shekara ta 2025, kama daga kula da cinkoson mutane, kiyaye lafiyar mahajjata da haka kuma ta kyautata ayyukan mahajjata a cikin nutsuwa da rashin damuwa.

Jaridar ArabNews ta kasar Saudiya ta bayyana cewa tare da wannan fasahar ta kula da zafin dukkan wuraren da mahajjata zuwa zuwa da kuma hana cinkoson mutane a kewayen Kaaba da sauran wurare.

.

Jami’I mai kula da bangaren kirkirerren fasaha wato AI na aikin Ajjin bana ya shaidawa Jaridar ArabNews kan cewa sun kirkiro abubuwa da dama don sawwaka aikin hajji ga mahajjata da kuma khidimomin da kasar saudiyya take yiwa mahajjata, Ya ce an yi amfani da wannan fasahar a masallacin Madina da kuma na dakin nKaaba.

Ya ce jami’an shige da fice na kasar Saudiya suna amfani da kayakin aiki na zama a ayyukansu . sannan suna aikin bincike da kansu a tashoshin jiragen sa 11 a kasashen 7 a duniya, inda suke tabbatar da cewa mahajjaci ya cancanci ya je aikin hajji tun daga kasarsu kafin ya shiga jirgi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

Gonar ta ‘AA Dibine Agro’, ta kasance a yankin Pasali Karshi da ke cikin karamar Hukumar Karu a Jihar Nasarawa.

Kazalika, kudirin shi ne; nomawa da kuma samar da isasshen Filanten din da za a rika kai wa har zuwa babban birnin tarayya  Abuja, domin sayar da shi.

A cewar tasa, abin da gonar ke son cimma shi ne, taimaka wa fannin aikin noma na tarayyar kasar nan, wanda hakan zai kuma kara tallafawa wajen kara samar da ayyukan yi ga ‘yan kasa tare da samar da wadataccen abinci.

Sai dai, ya bayyana cewa; rashin kudaden da za a yi amfani da su wajen cimma wannan manufa, su ne babban cikas.

Gonar, wadda aka samar da ita a zagayen Katangu, domin kiwon dabbobi, na matukar fama da karancin ruwa da ya yi sanadiyyar dakatar da gudanar da dukkanin wasu ayyuka da ake yi a cikinta.

Bugu da kari, rashin samar da hanya; wadda za a rika amfani da ita wajen safarar amfanin gonar da aka girbe, na daya daga cikin kalubalen da gonar ke fuskanta.

Amma duk da irin wadannan matsaloli da gonar ta ‘AA Dibine’ ke fuskanta, ta tanadi wasu muhimman manya-manyan shirye-shiye.

Daga cikin shirye-shiyen sun hada da; burin samar da wuraren kiwon dabbobi da kiwon Kajin gidan gona da wuraren kiwon Kifi da kuma sarrafa abincin dabbobi, wanda hakan zai taimaka wajen habaka tattalin arzikin yankin tare da samar da ayyukan yi da kuma kara bunkasa noma.

kungiyar ta COMAFAS, ta fi mayar da hankali ne wajen tallafa wa manoma da kuma kara habaka fannin aikin noma.

A cewar Dakta Maduka, kungiyar ta amince da yarjejeniyar ce, duba da cewa; ta lura da manufar da gonar ta ‘AA Dibine Farm Limited’, ta sanya a gaba, musamman domin tsamo gonar daga cikin babban kalubalen da take fuskanta tare kuma da samun damar cimma burin da ta sanya a gaba.

Ya kara da cewa, hadakar za kuma ta taimaka wajen samar da ilimi da masu zuba hannun jari da kuma samun tallafin kudi ga gonar. Haka zalika, kudin zai taimaka, wajen sama wa gonar kayan aikin da take bukata da kuma samar da hanyar yin jigilar amfanin gonar da aka shuka.

Sauran daukin da hadakar za ta samar, sun hada da horo da kuma tabbatar da shugabanci nagari da sauran makamantansu.

Dakta Maduka, ya kuma bayar ta tabbacin cewa; ta hanyar jawo sauran abokan hadaka cikin wannan aiki, za a iya noman wannan Filanten mai matukar tarin yawa a gonar, duba da cewa; yankin na da yanayi mai kyau na yin noma da ake bukata, inda kuma hakan zai kara taimakawa wajen samar da ayyukan yi.

Kazalika, ya bayyana cewa; hadakar za kuma ta kara taimakawa wajen kara habaka tattalin arzikin yankin tare da samar da wadataccen abinci yadda ya kamata. 

A cewar tasa, gonar ta ‘AA Dibine Farm Limited’, za ta kasance mai aiki da kayan noma na zamani a tsakanin sauran gonakin da ke fadin kasar nan, ta hanyar taimakon kungiyar ta COMAFAS.

Har ila yau, daukacin masu kulla wannan yarjejeniya, sun amince da kara habaka wannan bangare na noma a dukkanin fadin Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)
  • Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa
  • Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?
  • Babban Al’amari Ne A Samu Ƴar Shekara 6 Ta Haddace Qur’ani A Makarantar Raudatul Jannah – Mai Sikeli
  • Hajjin Bana: Jihohi 11 Sun Kashe Naira Biliyan 6.2 Kan Mahajjata
  • Wani ya kashe mahaifiyarsa mai shekara 71 a Akwa Ibom
  • Zamfara Ta Zama Jiha Ta Farko Da Ta Ƙaddamar da Tsarin Ilimin Fasahar Zamani
  • An Kafa Fiye Da Kamfanonin Waje 24,000 A Sin Cikin Watanni 5 Na Farkon Bana
  • Yin sulhu da ’yan bindiga dabara ce ba gazawa ba — Gwamnatin Sakkwato
  • Yunkurin Tauye Ci Gaban Fasahar Kera “Chips” Ta Sin Ba Zai Haifar Da Da Mai Ido Ba